الأربعاء، 1 يوليو 2020

NI'IMA TA LAFIYA

اسم المترجم : أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاؤيخ : 5-11-1441هـ

Hudubar Juma'a a masallacin Annabi na Shaikh Husaini Al-Assheikh

Mafi girman ni'imomin duniya ita ce ni'imar lafiyan jiki, ba wata  ni'mar da ta ke daidai da ita na daga cikin ni'imomin duniya  duk yanda ta yi dadi , Allah ya azurta mu gaba daya da lafiya da waraka saboda haka ne ba wanda ya san dadin lafiya sai wanda ya dandani dacin cututtuka da rashin lafiya Allah ya kare mu da ni da ku daga su Manzon Alla tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ni'imomi guda biyu mutane na hasara a cikinsu, shi ne lafiya da kuma zaman banza)Buhari ne ya rawaito

'yan uwa a musulunci :

Mai samun farin ciki, wanda aka datar da shi , shi ne wanda ya san ni'ma yayin samuwanta ya kuma tashi da hakkin ta , ya kuma ji kimanta a jikin shi , mafi wajabcin godiya ga ni'ma na lafiya shi ne ka hakabata ya kai musulmi wurin da'a ga Allah na sauke wajibabbu da kiyayewa bisa ga umarce umarce, da yin nesa daga bakaken abubuwa da mununan laifuka , da gaggautawa zuwa ga ayyukan nafilfilu da kuma ayyuka na kwarai Allah Madaukakin sarki ya ce:(ku yi gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijinku da aljanna wanda fadinta ya kai sammai da kasa an tattaleta ga masu tsoron Allah),

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa (ku gaggauta da ayyuka kafin abu guda bakwai, shin akwai abin da ku ke jira ne face talauci abin mantawa? Ko wadata abin da ke sa dagawa?, ko kuma rashin lafiya da ke yin barna?, ko tsufa da ke kararwa? ko kuma mamaci abun shiryawa?,ko kuma dajjal? to sharrin abin da ya ke boye da ake jira ko kuma tashin alkiyama? kuma tashn alkiyama shi ya fi tsanani shi ya fi daci)Tirmizi ne ya rawaito kuma ya ce hadisi ne hasan .

'yan uwa na musulunci :

Musulmi a  ko wani halin da ya ke ciki yana cikin alheri ne mai girma da lada mai yawa a duk lokacin da ya yi ikilasin niyarsa ga Allah ya yi gaskiya a wurin biyayyan sa , duk wanda aka jarabce shi da rashin lafiya ya yi hakuri ya nemi lada to hakan zai zamo mishi daukaka ne a darajojin shi kuma da kankara ne ga laifukan shi , Allah Madaukakin sarki ya ce : (hakika za mu jarabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da tawaya na daga dukiya da rayuka da 'yayan itace ka yi albishir ga masu hakuri) (wadanda idan musiba ta same su sai su ce lallai daga Allah mu ke kuma gare Shi za mu koma) (wadannan suna da kyakkyawan ambato daga wurin ubangijin su kuma da rahama kuma wadannan su ne shiryayyu) , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(ba wata musiba da zata samu musulmi na rashin lafiya ne ko wani abu koma bayan haka face Allah ya kankare mishi laifukan shi kamar yanda ganyen itace ta ke karkadewa diga itaciya) Muslim ne ya rawaito.

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya shiga wa Ummussa'ibsa ya  ce :(mai ke gare ki ne ya ummussa'ib kina karkarwa ? sai ta ke cewa zazzabi ne , kar Allah ya mata albarka sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : kar ki zagi zazzabi domin tana tafiyar da kusakuran bani a'adama kamar yanda zugazugi ke tafiyar da kazantan karfe) Muslim ne ya rawaito.

Na daga cikin mafi girman ni'imar Allah cewa Allah yana gudanar da lada ga bawa mai  rashin lafiya irin ladan aikin da yake yi a halin yana mai lafiya, kamar yadda ya zo a sahihul Buhari Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shiya ce :     (Idan bawa ya yi rashin lafiya ko tafiya to Allah Madaukaki zai  ci gaba da rubuta masa ladan aikin da ya saba yi a halin yana da lafiya mazaunin gida).

                                                                                                                          Ka sani ya kai wanda a ka jarabta da rashin lafiya  Allah na kusa da bawanSa to ka nemi mafaka a gare shi, ka roke shi waraka da lafiya kana tsayuwa a kan sabuba na jinya wadanda su kansu suna cikin hakikanin  dogaro ga Allah Mabuwayi da daukaka, da Allah ne kadai bakin cikinka ke yayewa kuma cutarka ta tafi ( kuma idan na yi rashin lafiya to shi ke warkar da ni).      

Ka kasance bisa yakinin rahamar Allah da falalarSa, kuma shi ne Mai warkarwa kuma Isasshe,  ( kuma lalle tare da tsanani akwai sauki. To kuma lalle tare da tsanani akwai sauki)


 

Huduba ta biyu

Duk yadda dan adam ya kai da karfi da bunkasa da tunbatsa a fagen ilimi to fa sifa ta rauni na damfare da shi, Allah Madaukakin Sarki ya ce ( kuma ba a baku wani abu na ilimi ba face kadan). Kuma Mai tsarki yace : (Kuma an halicci mutum da rauni).

To cikakken  Karfi na hakika sifa ne ga Allah  Alkawiyyu Al Matin Mamallakin dukkan komai bisa hakika, Mai gudanar da al'amura kuma Mai tunkude su, kowani abu na faruwa ne da hukuncinSa da kaddararSa. Kuma karkashin gudanarwarSa da ganin damarSa (Mashi'arSa)  ( Ya ku mutane ku talakawa ne zuwa ga Allah, kuma Allah shi Mawadaci ne Abin godiya).  

To mu yi kokari wurin bauta masa, mu kafu wurin masa biyayya kuma mu kankan da kai a gare shi mu nemi mafaka daga bangarenSa. Allah Madaukakin Sarki yace :( ku tuba zuwa ga Allah Ya ku wadanda suka yi imani ko zaku rabauta) 


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق