اسم المترجم : أمين سعد عبد الله
اللغة : الهوسا
التاريخ : 10-12-1441هـ
Hudubar Juma'a a
masallacin Annabi na Shaikh Abdulbari dan Awad Assubaiti 10-12-1441AH /31-7-2020AD
Yalwar afuwar
Allah
Hudubar farko
Dukkan yabo da
godiya sun tabbata ga Allah wadda ya sanya aljanna sakayyar hajji mabruri, ina
kyautata yabo gare shi, tsarki ya tabbata a gare shi kuma ina gode mishi bisa dukkan falala da alheri da ya saukake na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya
shi ne Mai yafiya kuma Mai gafara,
shi ne Mai yawan yafiya kuma Mai gafara
kuma na shaida shugaban mu kuma Annabinmu Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne ya bautawa UbangijinSa da yakini zuciyarsa sai ta zama tana farin ciki da
kaunarsa tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi, duk wanda ya kaunace su shine abin taimakawa kuma mai samun lada.
Bayan haka;
Ina muku wasiya da ni kaina da tsoron Allah, Allah Madaukakin
sarki ya ce :- (Ya ku wadan da suka yi imani ku
ji tsoron Allah cancancin tsoron shi
kada ku mutu face kuna musulmai ).
Yafiyan Allah kalma ce da take jefa natsuwa a cikin
zuciya da kwanciyan hankali a cikin
zuciya da kuma sika cikin abin da yake wurin Allah.
(Hakika
Allah ya kasance Mai yafiya ne kuma Mai yawan gafara yana yafewa wanda yayi zunubi kuma ya gafartawa wanda ya yi laifi kuma yana
rangwantawa wanda yayi kuskure) ( shi ne wanda ya ke karban tuba daga bayinSa
kuma yake yafewa daga kusakurai kuma ya
san abin da kuke aikatawa ).
Na daga cikin
kyawun afuwar Allah yana son masu
tuba kuma yana farin ciki da komawa zuwa
gare shi
Na daga cikin
yalwan afuwar Allah da ribanya kyawawa da yake yi da kuma bada lada bisa ga
nufan yin abu ba tare da munana ba.
Na daga
cikin kyakkyawan afuwan Allah shi ne yakan canza munanan ayyuka ya maida su kyawawa
bayan tuba na gaskiya, idan bawa
ya daina aikata aikin haramun ya
fiskanci sabuba na tuba da da'a ya kara imani tare da imaninsa sai ya karfafi dalilai na imani a cikin zuciyarsa, sai Allah ya karrama
shi da
kyakkyawan yafiyarSa.
Abin mamaki da
yalwa da kuma kawa irin na afuwar Allah Mai
tsarki da Daukaka,
Allah ya ce :- (sai
wanda ya tuba ya yi imani kuma ya yi aiki , aiki na kwarai to wadannan Allah zai canza musu laifukan
su kyawawa, Allah ya kasance Mai gafara ne Mai jin kai) .
Na daga cikin
yalwan afuwar Allah cewa rahamarSa tana
rigayar fushinSa yafiyarSa kuma tana
riga ukubarSa, Buhari ya rawaito shi daga
Hadisin Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- Na ji Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa :- (Lallai Allah
yayin da ya yi halittan halitu ya rubuta
a wurin shi a saman al'arshin shi, lallai
rahama ta ta rigayi fushi na ).
Na daga cikin yalwar afuwar Allah shi ne jinkirtawa bayinSa da yake yi kafin ya kama su domin Allah Mai tsarki da daukaka shi yana fiskantar jahilcin bayi da hakuri sa'annan kuma zunubinsu yana fiskantar sa da
gafara, sannan bayyana sabo kuma yana
fiskantar shi da suturtawa, kafurcewa ni'ima kuma Allah yana fiskantar ta da ni'imtarwa.
Na daga cikin yalwar afuwar Allah da
ya sanya masu kankare zunubai nau'uka daban –daban, na daga cikin masu kankare
zunubai akwai yalwata alwala, da ambaton Allah karshen farillu, da yawan taku
zuwa masallatayya, da azumin ramadana da azumin ranar Arafa da azumin ranar
Ashura., da adu'ar kaffatul majlis da umara da Hajji da sauke sallolin
farilla. Da sadaka da hakuri da halartan majlisai na zikiri, da salati ga
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Na daga cikin koyarwar Annabi kwadayin neman afuwa da
yafiya yana rokon Allah a lokacin da ya wayi gari da lokacin yammaci (Ya
Allah ina rokonka afuwa da waraka a addini na da duniya ta da iyalai na da
dukiya ta).
Allah ka sa min albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai
girma.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga wanda da ni'imarSa ce kyawawa ke cika ina kyautata yabo a gare shi kuma ina gode mishi
bisa kyautarSa masu yawa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai
Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya
Abin bautar halittu na shaida shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma Manzon sa
ne , shi ne abin koyin mu a duk wani yanayi da aka shiga na tsanani tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi da sahabbansa ma'abota falala abin
girmamawa.
Bayan haka, ina muku wasiyya da kaina da tsoron
Allah duk wanda ya dimanci da'a ga Allah to zai rabauta da afuwar Allah.
Tare da wannan
falala mai girma da kuma yafiya mai yawa,
mutum zai kiyaye daga ruduwa da afuwar Allah da girman karamcinSa Allah Madaukakin sarki ya ce :-(Ya kai
mutum mai ya ruda ka
game da Ubangijin ka Mai karamci ).
Ya dace a
wadannan kwanaki a bayyana manyan alamomi na musulunci na daga ciki akwai kabbarori wanda suke masu kaidi karshen salloli na farilla, wanda ke farawa tun daga safiyan ranar
arfa har zuwa faduwan ranar karshe na
ayyamut tashrik .
Allah Mai girma
ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
kuma Allah Mai girma ba bu abin
bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai
girma dukkan yabo da godiya na shi ne.
ku saurara
kuma ku yi salati ya ku bayin Allah bisa
ga Manzon nan na shiriya hakika Allah ya
karrama ku a littafinSa.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق