اسم
المترجم : أمين سعد عبد الله
اللغة
: الهوسا
التاريخ
: 19-11-1441هـ
Hudubar Juma'a a
masallacin Annabi na Shaikh Abdulbari dan Awad Assubaiti 19-11-1441AH / 9-7-2020AD
Hudubar farko
Dukkan yabo da
godiya sun tabbata ga Allah. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah,
bayan haka.
Tarihin Annabi
kan haskaka mana hanyar tafiya a rayuwa. Na daga cikin shafuka na sira masu
kamshi akwai tarihin sulhun Hudaibiyya da darusansa da mawakif na sa da abin da ya faru a ciki Allah
ya ambace shi da budi Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Lalle Mu Mun yi ma budi wanda yake budi bayyananne).
Sahabbai sunyi
bushara da mafarkin da Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya gani cewa za su shiga Makka kuma su yi
dawafi a dakin Allah Madaukakin sarki ya
ce :- (Lalle ne Hakika Allah ya gaskata wa ManzonSa
mafarkinsa da gaskiya: Lalle za ku shiga
masallacin Harami in Allah ya so,
kuna amintattu kuna masu aske
kawukan ku da masu saisaye , ba ku jin
tsoro).
Mutum dubu da dari hudu daga cikin masu umra suka tafi tare da Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi suna da kuzari
game da abin da suke ji na karfin guiwa, zukatan su na cike da shu'uri
suna masu nufan dakin kaba bayan
yankewan shekaru da wannan wurin din mai
albarka wanda zukata ke karkata zuwa
gare ta wanda ta kasance kuma bata gushe
ba kuma baza ta gushe ba wato shudewan zamani da kuma lokaci , alkibla
ne da zukata kuma wurin karkata ne da
zuciya rayuka kan samu natsuwa a
farfajiyan ta kuma ta dauki ibra a kasanta kuma ta zubar da hawaye Ibrahima alaihissalam ya mata adu'a (Allah
Ubangiji lallai na zaunar daga cikin
zuri'a ta a kwari wanda ba yi da shuki a wurin dakin ka mai alfarma , Ya Ubangijin
mu domin su tsaida sallah ka sanya
zukata na mutane na karkata zuwa gare su )
Shauki zuwa ga
masallaci mai alfarma da kwadayin wurare
na alheri da ibada dalili ne na rayuwan
zukata kuma dalili ne na hasken zuciya
da kuma lafiyan ta Allah Madaukakin
sarki ya ke cewa (Lallai kawai masu raya
masallatan Allah su ne wadan da suka yi imani da Allah da ranar lahira kuma suka tsaida salla suka bada zakksa ba su ji tsoron kowa ba sai Allah
to, ya wuci wadannan su kasance cikin shiryayyu) Annabi tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi harama daga zulhulaifa ya fara talbiya asaniyya
kusa daga makka asaniyya kusa da
makka taguwar sa ta durkusa wato alkasuwa wato ta kwanta taki ta tafi daga wurinta sai
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Ba kin tafiya ta yi ba
kuma wannan ba dabi'arta ba ne sai dai akwai abin da ya rike ta ne
wanda ya rike giwa ,)Buhari ne ya rawaito
Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya tunkude daga taguwarsa alkasuwa yayin da aka tsarge ta ta yi tirjiya da fadin sa cewa a'a wannan ba dabi'ar ta ba
ne wannan baya cikin halinta domin ya bada hanzari ga dabba wanda yake ba
magana take yi ba sabo da sanin halin ta
na asali da kuma wato siranta mai
kyau domin ya koyar da al'umar sa darasi
wurin mu'amala da hukunci mai kyau bisa
ga maukifi da aka samu akai da kuma cikin dauke
laifi da samar da uzuri da mutumin da yake da wasu abubuwa da suke abun shaida na
alheri da falala a baya Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya tura Usman Allah ya yarda da shi da sako na musulunci wato ita ce zaman lafiya ba kiyayya ba ya basu labari cewa mu ba mu zo don yakan
wani ba Usmanu sai ya zo garin makka ya
gayawa Kuraishawa game da sakon Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi cewa sun zo ne suna masu ziyaran dakin kaba suna masu girmamawa da alfarmarsa da kuma
dawafi da shi sai suka ki , aka samu kai
komo tsakanin Manzon Allah da kuraishawa
Annabi ya yi amfani da tausayawa
a cikin al'amura da kuma dauke
kai cikin abin da ba zai cutar da addini ba
wanda kuma ba zai bata sha'ani na
hakkin Allah ba Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa (Na
rantse da wanda raina yake hanun sa ba
za su tambaye ni wata khudda ba wanda suke girmamata na alhurmomin Allah face na basu ita) Buhari
ne ya rawaito .
Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya rinjayar da bangare na
maslahan kare jinayen musulmai da
kuma kubutar rayuka kuma yayi dubi zuwa
ga karshen al'amari a assasawa al'uma
fikhu na manufa da kuma gaya ya kasance a makka a hudaibiyya mutane dayawa daga cikin muminai da kuma masu rauni daga maza da mata da 'yan yara , da'ace sahabbai sun shiga makka aka samu yaki a
tsakani da ba wanda zai aminta da ya
kubuta daga a taba shi kamar yanda Allah mai tsarki da daukaka yake
cewa :-(Kuma ba domin wadan su maza muminai da wadan su mata muminai ba ba ku sansu ba, ku taka su
har wani aibi ya same ku daga gare su ba
ba da sani ba (da Allah ya yi
muku izinin yaki )
Amfanin sulhun
ya bayyana karara da kuma fa'idoji na zahiri wanda ya kasance karshen shi bude garin makka da kuma musuluntar mutanenta da shigan mutane addinin Allah
tawaga-tawaga.
Na daga cikin dubi zuwa ga makoma na al'amura
kasancewan haji a wannan shekara wani
nau'i ne daban, an kebe shi da wani adadi iyakantacce da wasu ka'idoji da aka shar'anta a karkashin wannan yanayi na korona , da cutarwanta ya game komai annobanta ya taba ko wani abu , wannan matakin mai hikima wanda jagorori suka dauka na mamlakar arabiyya saudiyya ita ta dace wato tana cikin abubuwa da suke
mafi muhimmanci yana tafiya tare da
manufofi na shari'a kuma yana fadawa ne
akan maslahan musulmai wurin kiyaye
rayuka da kuma tunkude duk wani abu da
zai ka ga hadari wanda yake
tabbatacce , ko kuma wanda aka fi
rinjayin zato akan shi da kuma
yin taka tsantsan wurin yaduwar wannan
annoba din da kuma cututtuka masu yaduwa.
Tattaunawa da aka yi ya haifar da
ittifaki da tarihi ya ambace shi
da sulhun hudaibiya wanda
sahabbai suka koma zuwa garin madina ba
tare da sun yi dawafi a dakin ka'aba ba
sai dai Allah ya girmama su ya
yalwata musu lada ta inda ya
yarda da su sai yake cewa hakika Allah ya yarda da muminai ya yin da suke mubaya'a a gare ka
karkashin bishiya shi ya san abin da ke cikin zukatan su sannan ya saukar da natsuwa a gare su
kuma ya basu ladan budi a kusa, da wannan ne zai bayyana wa musulmi cewa idan yayi iya kokarin shi ya yi iya abin da zai iya wani abu ya yi shamaki tsakanin shi da ibada don sauke wannan ibadan to kada ya yi fushi kuma kada ya yi bakin
ciki domin za a maida mishi abin da ya rasa
ladan shi kuma yana rubuce falalan Allah kuma yana da yalwa an karbo daga Abdullahi Dan Abbas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :-
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:-(Cikin abin da ya ke rawaitowa daga Ubangijin shi mai tsarki da daukaka lallai Allah ya rubuta kyawawa da munana sannan ya bayyana haka duk wanda ya nufi aikata kyakkyawa bai aikata
ba to za a rubuta mishi ladan shi cikakke idan
kuma ya nufi aikatawa sai ya aikata to
za a rubuta mi shi ladan shi guda goma
har zuwa dari bakwai zuwa ga ribi mai yawa idan kuma ya himmatu da mummuna bai aikata ba
to Allah zai rubuta mishi kyakkyawa guda cikakke, I dan kuma ya himmatu da ita sannan ya aikata
ta to za a rubuta mi shi mummuna guda daya) Buhari ne ya rawaito da
muslim.
Madalla da irin
wannan falala mai girma wanda mai jinkai
mai rahama ya ke kwaranyo da shi zuwa ga
bayin shi muminai yayin da aka gama sulhu
tsakanin Manzon Allah da kuraishawa Manzon Allah ya tashi sai ya ke cewa ku tashi ku soke abin yankan ku kuma ku aske kawunan ku , ya fadi haka har sau uku ba daya daga cikin su da ya tashi
sai wani alamomi na bakin ciki ya
bayyana a gare shi a zaton wasu daga
cikin su wannan sulhun ci baya ne sai
ummu salma ta yi nuni zuwa ga Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi tace ya Annabin Allah kana so a yi
hakan? To ka fita kada ka ka fadi ko kalma ga daya daga cikinsu, har sai ka
soke rakuminka, ka kira mai askinka ya maka aski, sai ya fita bai yi wa kowa
magana ba daga cikinsu ya aikata haka ya soke dabbarSa kuma ya kira mai askinSa ya masa aski yayinda suka
ga haka kowa sai ya tashi ya soke dabbarsa sai wannan yayiwa wannan aski wannan
ma ya yiwa wannan aski har sashinsu ya kusa ya ti fada da sashi saboda bakinciki
) Bukari ne ya rawaito
Shawara mai
zurfi daga ummu salama Allah ya kara yarda a gareta ga Annabi manzo wanda ya
canga akwalar abinda ya faru na waki'I a wannan mawuyacin yanayi wannan maukifi
da waninsa da yawa yana tabbatar da matsayi da daukaka irin na mace a musulunci
da karrama musulunci gareta da kuma karfafanta ga sakon musuluncin lallai mace
mai hankali mai tunani mai ra'ayi da ayyukanta na da dauri wurin sana'anta wato
rayuuwa da gina shi da kuma habaka shi .
Ummu salama Allah ya kara yarda a gareta ta raya da
shawaranta daya daga cikin mafi rukunnai na tarbiyya abun koyi a aikace wanda
ita ce mafi yawan amfani a dasa ginshiki kuma dabi'u da kuma gyara halaye .
Yana bayyana a
sulhul hudaibiya kaunar sahabbai ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi wanda ba a kwatanta shi da kuma daukaka wanda ba irinsa , abin da ke
nuni ga haka Urwa daya daga cikin jakadun kuraishawa zuwa ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
fadinsa ga mutanensa kaman yanda ya zo a cikin Buhari sai Urwa ya koma ga
mutanensa sai ya ce ya mutane na: '' wallahi ; hakika naje wurin sarakuna naje
ga kaisar da kisra da Najashi wallahi ni ban taba ganin wani sarki ba ko da su
daya wanda mutanensa ke girmama shi kamar yanda mutanen Muhammadu da sahabban
Muhammadu suke girmama shi ba wallahi in da zai fitar da majina to face sai ta
fadi a tafin hanun daya daga cikinsu ya shafe a fiskansa da kuma fatansa , idan
ya umarce su gaggawa suke yi don su aikata umarninsa idan ya yi alola suna dab
da su yi fada da juna wurin ruwan alolansa, idan ya yi magana sai su sassauta
muryansu gaba gare Shi ba sa iya daga ido su yi dubi zuwa gare shi saboda
girmama shi lallai shi yabijiro muku da wata hanya ta shiriya to ku karbeta''.
Huduba
ta biyu :
Yayinda Suhailu dan amru ya zo don tattaunawa da Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ga jakadan kuraishawa manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai ya ke
cewa: (hakika
al'amarinku ya saukaka) Bukari ne ya
rawaito ,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya yi tafa'a'ul wannan abin nanatawan
musulmi a cikin al'amura masu jujjuyawa zai yi fatan alheri kuma ya
kyautata zato ga Ubangijinsa a irin wannan yanayi na annoba muna kyautata zato
ga ubangijinmu muna sakankancewa cewa lallai
yaye bakin ciki na tahowa bala'i kuma na gushewa kuma komi zai koma
daidai iska a bigire mai tsarki ya kwanta ya tsarkaka ya yi dadi zukata su je
su yi dawafi da jikunkuna a ka'aba sannan kafafuwa su taka su yi sa'ayi tsakanin
safa da marwa ba da jimawa ba mu'munai za su yi farin ciki Allah Madaukakin
sarki ya ce : (Hakika Allah ya gasgata ManzonSa da mafarki da suka yi
na gaskiya cewa za ku shiga masallacin alharam in Allah ya so kuna cikin amunci
kuma kuna masu aske kawunan ku kuna masu gajarta gashinku ba kwa tsoro).
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق