الجمعة، 31 يوليو 2020

HUDUBAR BABBAR SALLAH

خطبة عيد الأضحى لفضيلة الشيخ أحمد طالب

اسم المترجم : أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاريخ : 10-12-1441هـ

Hudubar babbar sallah na masallacin Annabi tare da Shaikh Ahmad bin Hamid   Al dalib 10-12-1441AH / 31-7-2020AD

 

Hudubar farko:

Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu Akbar

 

Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu Akbar

 

Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu Akbar

 

Allahu Akbar kabiran  , walhamdu lillahi kasiran , wa subhanallahi bukratan wa asila.

Allah Mai girma Abin girmamawa.

 Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Abin daukakawa  kuma tsarki ya tabbata ga Allah abin tsarkakewa  kuma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Abin kadaitawa  babu dabara ko karfi sai ga Allah Abin dogaro, abin fauwalawa na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya  muna masu  tabbatarwa da kuma kadaitawa, na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da aminci mai kari.

Tsarki ya tabbata ga Allah  kuma godiya ta tabbata ga Allah   ba abin bautawa da gaskiya sai Allah , kuma  Allah mai girma  ba  dabara  ko karfi sai ga Allah Madaukaki kasaitacce .

Mafi soyuwan magana zuwa ga Allah  kuma mafi soyuwan magana zuwa ga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  bisa duk abin da rana ta fito a kan shi wanda take mafi daukaka wanda aka 'yanta kuma mafi kyau akan dawakai masu linzami da sirdi  da kuma mafi tsadar raguna da aka sa musu alama na hadaya  karbabbiya

Allah Mai girma wanda  zai cika tsakanin sama da kasa ya kankare zunubai ko da ya kai tarukucen kumfan kogi ne  da fadowansu zuwa kasa kamar yanda 'ya'yan itace ke zuba .

Allah mai girma ……su ne dashen aljanna kuma masu tseratarwa  kuma garkuwa kuma Albakiyatussalihatu wanda ladan su ke wanzuwa sakayyan su ke dauwama .

Allah mai girma… suna shawagi a  kewayen al'arshi mai rahama suna da sauti kaman sautin kudan zuma   suna tunatarwa game da sahibinsu  ba zai gushe ba yana da abin da ake ambatonsa da shi gaba ga UbangijinSa, kuma Ubangijin ka bai kasance mai mantuwa ba.

Kuma ba wani mutum da ya fi daraja a wurin Allah akan mumini wanda  ya yi tsawon kwana a musulunci  yana yawaita ambaton Allah .

Allah mai girma…..

Sune sadaka na gangan jiki  kuma masu nauyaya mizani  kuma masoya zuwa ga Mai rahama kuma da su ne ake nade sunayen Allah kyawawa da siffofin shi Madaukaka  su ne masu tattaro abin da suka tarwatse  kuma su ne matattara na yin da'a.

Allah Mai girma….

(Ya ku wadanda suka bada gaskiya  ku ji tsoron Allah  ku fadi magana da take  dai-dai, zai gyara muku ayukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yiwa Allah biyayya da ManzonSa to hakika ya rabauta, rabauta mai girma ) Ahzab 71

(Ya ku wadanda suka yi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa, ku yi masa tasbihi safiya da maraice , shi ne wanda ya ke salati a gare ku da mala'ikun sa domin ya fitar da ku  daga duhu zuwa haske  kuma ya kasance mai rahama  ne ga muminai, gaisuwan su ranar haduwan su da shi shi ne aminci , kuma ya tanada musu lada mai girma ) Ahzab 44.

Da shaidawa da salla da azumi da zakka da jahadi da  hajjin dakin Allah  ba wani abu ba ne sai wasu sifofi ne na girmama Allah  da kuma wasu dalilai ne na ambaton Allah ba wanda zai samu daukaka  da talbiya  ko ya koshi da  tarwiya  ko ya yi arfa da taskiya, ko ya tsaya wurin girmamawa  ko kuma ya kusanto da mika wuya  ko ya yi jifa da walaha ko ya yi dawafi da hantsi, ko ya yi suka da kabbara  ko ya yi jifa da garji, face wanda harshen sa ya kasance danye  ne daga amabaton Allah.

Allah mai girma.

 

 

HUDUBA TA BIYU

 

Allah Mai girma Allah Mai girma Allah Mai girma Allah Mai girma Allah Mai girma Allah Mai girma Allah Mai girma

(Ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijinku lallai girgizan kasa wani abu ne mai girma,  ranar da za ku ganta duk wata mai shayarwa takans ingije abin da ta ke shayarwa, duk ma'abociya ciki zata sauke cikinta za ka ga mutane cikin maye alhali ba maye ba ne suke ba face azabar Allah ce mai tsanani). Haj 1-2.

 

  Allahu akbar kabiran, walhamdulillahi kasiran, wa subhanallahi bukratan wa asila,

Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi.

Ku yi laiha ya ku bayin Allah –Allah ya karba muku laihanku ba wani abin da mai bauta zai kusanci Allah da shi a ranar laiha da ya kai zubar da jinin dabbobin gida ga Allah Ubangijin talikai  ya ci ya yi kyauta  ya yi sadaka ya bayyana manyan alamomin addinin Allah  sunnan baban ku Ibrahim  amincin Allah ya tabbata a gare shi da Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi .

Ku sani cewa baya inganta a laiha a yi da  mara lafiya wacce rashin lafiyanta  ya bayyana ko makauniyar dabba wacce makantanta ya bayyana  ko gurguwan dabba  wacce bata iya tafiya tare da masu lafiya,  ko kuma mai gutsurarriyar kunne  wanda sama da rabin kunnen ta ya gutsure  ko kahonta , haka nan banda ramemmiya wanda babu bargo a kashin ta , haka nan kuma ba a so a yi da mara hakori  wanda hakwaranta na gaba suka cire daga asalin su   ko kuma wacce nonon ta ke motse kuma ya bushe tare da girma  haka nan kuma ba a so a yi da wacce ta kamu da cuta, cuta mai raba.

Ba ayi da rakumi  kasa da shekaru biyar , ko saniya sai  wacce ta kai shekaru biyu   ba ayi da akuya  sai wacce ta cika shekara ko rago sai wanda ya cika wata shida  rakumi na iya isarwa  mutane bakwai  saniya ma na isarwa mutum bakwai  abin da yake sunna shi ne a soke rakumi a tsaye an daure hanun shi na hagu , a yanka saniya kuma da dabbobi a baryan su na haku suna fiskantar alkibla  kuma za a ce ya yin  yanka ''Bismillahi'' , bisa wajabcin ''wallahu akbar'' bisa mustahabbanci .

Abinda yake sunna shi ne ya ci sulusi daga namanta ,  ya yi sadaka da sulusi yayi kyauta da sulusi.

 Kada ya saida fatan ta   ko wani abu na daga gare ta  kada kuma ya bawa mahauci ladansa daga cikinta  .

An sanya lokacin yanka tun daga kare sallan idi har zuwa karshen kwanaki biyu bayan sa .

Allah mai girma Allah mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah  kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya na Allah ne.

 (Kuma rakuman,  mun sanya su a gare ku,  a ibadojin Allah kuna da wani alheri babba a cikin su . Sai ku ambaci sunan Allah a kansu suna tsaye akan kafafu uku  sa'annan idan  sasanninsu  suka fadi , to,  ku ci daga gare su , kuma ku ciyar da mai wadar zuci  da mai bara . kamar haka muka hore muku su,  tsammaninku, kuna godewa .

Namomin su ba za su sami Allah ba, haka jinainansu, amma takawa daga gare ku tana samun Sa. Kamar haka ya hore su  sabo da ku,  domin ku girmama Allah  sabo da shiriyar  da  ya yi mu ku . Kuma ka yi  bushara  ga masu kyautata yi.)

 

Ya ku bayin Allah ku riki mai daga adua mai bude kofofin sama …salati da aminci ga limamin Annabawa kuma shugaban masu takawa.

Adu'a.  

 

 

 

 

 


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق