الجمعة، 31 يوليو 2020

FALALAN GOMAN FARKO NA ZULHAJJI 2

 

اسم المترجم : أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاريخ : 3-12-1441هـ

Hudubar Juma'a a masallacin Annabi na Shaikh Abdul Muhsin  Al kasim 3-12-1441AH / 24-7-2020AD

 

Hudubar farko:

  Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin sarki  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa , muna neman gafarar sa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma babu mai shiryar da shi, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya, kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa  da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.

 

Bayan haka: ku ji tsoron Allah-

Ya ku bayin Allah,- cancancin tsoronSa, ku yi murakabarSa a boye da bayyane.

Ya ku musulmi!

Allah na zaba a cikin halittun shi wanda ya so  kuma ( Ubangijinka na halittan abin da ya so kuma ya zaba) sai ya zabi manzanni  daga cikin mala'iku, da mutane, ya zabi ambatonSa daga cikin magana, kuma ya zabi dakunanSa daga doron kasa. Ya zabi ramadana da watanni masu alfarma daga cikin watanni, Jahiliyya sun kasance suna kari a kwanaki ta jinkirta don bin son rai, azuminsu bai zama a lokacinsa ba, hajjinsu kuma ba a kan lokacinsa ba, kuma Allah ya yi mana falala da turo Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma ga zamani ya zagayo kamar yadda ya ke, hajjinsa ya kasance a zulhajji, ya fada a cikin hudubarsa : Lalle zamani ya kewayo kamar yadda ya saba a sifarsa tun randa Allah ya halicci sammai da kasa)Buhari da Muslim.

         Sai adadi ya cika kidaya ya inganta al'amari ya koma bisa yadda ya gabata a littafin Allah a farko.

Fifiko tsakanin dararraki da ranaku na kira ne zuwa ga ribatan alherin da ke cikinsu, kuma Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kwadaitar bisa ribatar ni'imomi da za su gushe ba makawa, sai ya ce : (Ka Ribaci Abubuwa Biyar Kafin Zuwan Biyar : Ka Ribaci Ƙuruciyarka Kafin Tsufanka, Ka Ribaci Lafiyarka Kafin Rashin Lafiyarka,Ka Ribaci Wadatarka Kafin Talaucinka, "Ka Ribaci Lokacinka Kafin Zuwan Shagula, Ka Ribaci Rayuwarka Kafin Mutuwarka) Nasa'i ne ya rawaito.  

Ga goman zulhijja ya shigo mana Allah ya yi rantsuwa da dararrakin su sai ya ce (ina rantsuwa da Alfajir)(da dararraki goma) , su ne ranakun Allah masu alhuruma , kuma cikamakin watanni sanannu wanda Allah ya ce game da su, (Hajji watanni ne sanannu).

Wuninsu ya fi daraja akan wunin goman karshe na Ramadan , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (mafificin ranakun duniya su ne ranaku goma) Ibnu Hibban ya rawaito,

falalan goman Zulhijja ya samu ne sakamakon tattaruwan manya manyan ibadoji a cikinta na daga salla – da azumi – da sadaka – da hajji – wanda hakan baya samuwa a waninta.

kuma dukkan ayyuka na kwarai a cikinta ya fi soyuwa zuwa ga Allah na daga irin wannan aikin idan ya faru a waninta.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ba wasu ranaku wanda ayyukan alheri a cikin su ya fi soyuwa ga Allah irin wadannan ranaku)  wato yana nufin ranaku goma, sai suka ce ya Manzon Allah ko da jihadi a tafarkin Allah?  Sai ya ce: (ko da jihadi a tafarkin Allah sai dai mutumin da ya fita da rayinsa da dukiyarsa bai dawo ba da wani abu na daga wannan) Abu Dawuda ne ya rawaito asalinsa na Bukari.

Ibnu Rajab Allah ya kara yarda a gare shi ya ce '' kuma wannan hadisi yana nuni da cewa aiki na kwarai a wannan kwanaki goma ya fi soyuwa  ga Allah akan aiki a sauran kwanakin duniyaba tare da toge wani abu ba daga cikin su ''

Magabata Allah ya musu rahama sun kasance suna kokarin ayyuka na kwarai a cikin su '' Sa'id binu jubair Allah ya mishi rahama ya kasance idan goman farko na Zulhijja ya shigoya ya kan yi kokarin da ba za a'a iya ba ''

Na daga cikin falalan Allah da karamcin Sa Ya sanya  nau'uka na da'a daban daban a ciki na daga cikin abin da aka shar'anta akwai yawaita ambaton Allah , Allah subhanahu wa Ta'ala ya ke ce:(kuma su ambaci sunan Allah a ranaku sanannu) Ibnu Abbas Allah ya kara yarda a gare shi, shi da mahaifin shi ya ce:<< wadan nan kwanaki goman>> ambaton shi Allah Subhanahu wa Ta'ala a ciki na daga cikin ibadodi na kusanci Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce; (Ba wata rana da tafi girma da soyuwa wurin Allah aiki a cikin su a wurin Allah irin ranaku goma to ku yawaita a cikin su halala da kabarori Da kuma godiya wa Allah) Ahmad ne ya rawaito,

 Imam Annawawi Allah ya mishi rahama ya ce:<< mustahabbi ne yawaita  zikiri a wadannan goma kari akan su, mustahabbi ne na daga haka a ranar arfa fiye da sauran kwanaki goman, mafificin zikiri karatun littafin Allah shi ne shiriya kuma da haske bayyananne >>

Kabbarori wanda suke na saki wzaiwai ba kaidi a dukkan lokaci yana cikin manyan alamomi a watan zulhijja Ibnu Umar da Abu huraira Allah ya kara yarda a gare su sun kasance suna fita kasuwa a cikin ranakun nan guda goma suna kabarbari mutane suna kabbara da kabarbarin su , an shar'anta yin kabbara mai kaidi karshen salloli tun daga asuban ranar arfa ga alhazai da wasun su shehul islam Allah ya mishi rahama ya ce mafi ingancin zantuka a cikin kabarbari wanda jamhurin magabata suka yi da fukaha'u da sahabbai da limamai shi ne ayi kabbaran tun daga asuban asuban arfa har zuwa karshen ranakun attashrik karshen ko wani sallah.

Na daga cikin abin da ya ke mustahabbi a ranaku goma azumtan su, rana na tara shi ya fi dacewa a cikinta , Imam Annawawi- Allah ya mishi rahama- ya ce '' lallai mustahabbi ne mustahabbanci mai karfi '' .

Yin sadaka aiki ne na kwarai wanda ya ke yaye bakinciki ya ke tafiyar da bacin rai , mafi alheri  ta kasance a lokacin bukata da kuma lokaci mafi daukaka na zamani.

Tuba matsayinta a addini na da girma da daukaka domin ita ce sababi na samun rabauta da kuma samun sa'ada, Allah ya wajabta ta ga dukkan al'umma daga dukkan zunubbai. , sai ya ke ce ga wanda ya yi da'awan mata da da ga Allah (ase ba za su tuba zuwa ga Allah ba su nemi gafaran Shi ?) kuma ya ce ga muminai (ku tuba zuwa ga Allah gaba daya ya ku muminai ko za ku samu rabauta) , Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana rokon Allah a wuni so dari , kuma ya tuba zuwa gare Shi , Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa: (ya ku mutane ku tuba zuwa ga Allah domin ni ina tuba zuwa ga Allah sau dari a wuni) Bukari da muslim suka rawaito , mu muka fi dacewa da bukatuwa zuwa ga tuba , mafi alherin ranaku ga bawa shi ne ranan da ya tuba , Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da Ka'ab binu Malik Allah ya kara yarda a gare shi (Albishirinka da mafi alherin rana albishirinka da mafi alherin ranan da ya zo a gareka tunda mahaifiyarka ta haife ka) Bukari da Muslim ne suka rawaito .

Abin mamaki da kyan tuba mutun zai tuba a mafi kyan ranaku zuwa ga Allah duk wanda ya yi gaskiya a tuban sa to darajarsa zata daukaka Allah zai canja mishi munanan shi ya maida su kyawawa .

A cikin ranaku goma na Zulhijja ana nufan dakin Allah da aikin haji daya daga cikin rukunnan musulunci kuma ginshikan shi masu girma Allah Subhanahu wa ta'ala ya ke cewa (Allah ya wajabta fiskantan daki  ga mutane duk wanda ya samu iko na zuwa) , wanda ya gaza yin hajji saboda wani uzuri to shima yana  tarayya da alhazai a cikin lada idan ya gaskata niya, ta iya yuyuwa ma mutumin da ya tafi da zuciyarsa sai ya riga wanda ya tafi da jikinsa .

A goman farko na Zulhijja akwai ranar arfa azumtansa yana kankare zunuban shekara guda da kuma shekara mai zuwa (Ba wata rana da Allah ya fi yawaita 'yanta bayi daga wuta kamar ranan arfa) Muslim ne ya rawaito.

A ciki ne akwai ranan suka mafi alherin ranaku na yanka kuma shi ne mafi bayyana kuma shi ne mafi yawan tara jama'a shi ne ake cewa yaumulhajjil akbar (ranan hajji mai girma) Allah Madaukakin Sarki ya ce: ( shelantawa daga Allah da ManzonSa zuwa ga mutane ranan hajji mafi girma) .

Shi ne mafi girman ranaku a wurin Allah Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(lallai mafi girman ranaku a wurin Allah shi ne ranan suka sa'an nan kuma sai ranan sha daya) Abu dauda ne ya rawaito.

Kuma daya daga cikin I'idi ne na musulmai , rana ne na farin ciki da annashawa ta hanyan sauke wani rukuni daga cikin rukunnan musulunci, wasu mutane suna gafala tare da farin ciki daga ambaton Allah to ya kasance ambato a wannan ranaku yana da daraja , Allah subhanahu wa Ta'ala ya ce:(ku ambaci Allah a cikin ranaku kididdigaggu) – wato sune ranakun nan na Tashrik - , Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Ranakun Tashrik ranaku ne na ci da sha da ambaton Allah) Muslim ne ya rawaito.

Ibnu Hajir Allah ya mishi rahama ya ce: '' Ya tabbata falalan wadan nan ranaku goma , saboda haka wadan nan ranaku na ayyamuttashrik falalan su ya tabbata ''

A cikin ranakun suka akwai ibada ta dukiya da kudi kuma ita ce mafi soyuwar ayyuka zuwa ga Allah, Allah ya hada su da sallah sai ya ce:(ka yi salla ga Ubangijinka kuma ka yi suka) , Allah ya kwadaitar bisa ga ikhlasi a wurin suka, kuma ya kasance Allah aka nufa a ciki Shi kadai ba alfahari ko riya ko kuma neman a ji ko kuma ya zama kwai tsurar al'ada ce, Allah subhanahu wa Ta'ala ya ce :(naman shi baya riskan Allah ko jinin su saide tsoron Allah ne ya ke riskan Shi) kuma << Annabi ya yi laiha da raguna biyu masu fari da baaki a kahgon su ya yanka su da hanun shi >> Bukari da Muslim ne suka rawaito. ''al'amlah '' (shi ne baki wanda saman shi akwai fari) "al'akran"( kuma shi ne mai kaho) , babu laifi mutun ya yi bashi don ya yi laiha kuma ya nemi mayuwa a wurin Allah kada ya rika zambo sakamakon tsadanta , domin ladan ta wurin Allah yana da girma duk wanda ya nufi ya yi laiha to ya haramta a gare shi a cikin ranaku goman nan da ya dauke wani abu na daga gashin shi ko farcen shi , Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa (Duk wanda ya kasance yanada abun yanka zai yanka to idan jinjirin watan zulhijjah ya kama to kada ya dauki wani abu na daga gashin shi ko kkuma kumban shi har sai ya yi laiha) Muslim ne ya rawaito.

Bayan haka ya ku musulmai:

Wanda ya samu sa'ida shi ne wanda ya ribaci lokutan nan na watannin nan da ranakun nan da sa'o'in nan ya kusanci Allah Majibincin shi da abin da ya ke na ayyukan da'a , ya wuci wani abu ya riske shi na wannan alheru ya samu sa'ada wanda zai aminta da su bayan haka daga wuta da abin da ke ciki na daga alheru kuma ya rabauta da aljanna wanda fadinta ya kai sammai da kasa .

Ina meman tsarin Allah daga shaidan abin jifa

(Ku yi gaggawa zuwa ga Uban gijin ku da aljannah wanda fadinta ya kai sama da kasa an tanadeta ga wanda suka yi imani da Allah da ManzanninSa wannan falala ne na Allah ya kan bada shi ga wanda ya so Allah Ma'aboci falala ne Mai girma).

Allah Ya sa mini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma. 

 

Huduba ta biyu :

   

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawanSa dodiya a gare Shi bisa datarwan shi da baiwan Sa na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kadai Ya ke ba Shi da abokin tarayya ina mai girmama Sha'aninSa , na shaida Annabin mu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da sahabbansa da aminci tabbatacce mai kari.

Ya ku musulmai:

Addinin musulunci addini ne mai girma da an gina shi akan janyo maslahohi da kuma tunkude barna saboda wata hikima da Allah ya ke nufi da ita, ya shafawa mutane a doron kasa gabacin kasa da yammacinta da wata annoba wanda ba a taba irinta ba a tarihin doron kasa ko da sau daya kuma da boyuwarta da yaduwarta da gazawan samo maganinta wanda yana kama wanda ya kiyaye daga gareta a wani lokaci kuma ya kuskure da umarnin Allah wanda ake zaton zai kamu da ita.

 Hakika Allah ya kebance wannan gari (Alharamain Ashsharifain) da wasu darajoji kuma ya daukaka darajan jagororinta ta hanyan hidima da kuma kaunan su ga musulmai a dukkan doron kasa da kuma tsorace musu  abin da zai faru gare su na daga cutuwa, saboda haka ne jagororinta suka dauki matakai na hana yaduwar wannan cuta na annoba domin fatan gushewarta ba tare da an samu cakudayyan mutane ba sashin su ga sashi musamman a hajji tunda ana tafiya ne zuwa gare shi kuma ana zuwa a dawo yana karuwa a garuruwa, sai suka maida karin alhazai zuwa ga shekara mai fiskantowa domin fatan alheri da neman yayewan Allah da rahamarSa, Allah ya saka musu da alheri bisa ga musulunci da musumai.

Allah Subhanahu wa Ta'ala Ya siffantu da falala da karamci da rahama na daga wanda ya nufi hajji ya gazara yi to za a rubuta mishi ladan shi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (lallai a cikin Madina akwai wasu mutane da baza ku yi wasu tafiya ba ko ku yanka wani kwari ba face sun kasance tare da ku) sai suka ce ya Manzon Allah : alhali suna Madina sai ya ce:(iye, uzuri ne ya tsare su) Bukari ne ya rawaito .

Sannan ku sani Allah Ya umarce ku da salati da  aminci ga AnnabinSa.

 


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق