الثلاثاء، 14 يوليو 2020

GODIYA BISA NI'IMOMI

اسم المترجم : أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاريخ : 12-11-1441هـ

Hudubar Juma'a a masallacin Annabi na Shaikh Aliyu Bin Abdurrahman Al-Huzaifi 12-11-1441AH / 2-7-2020AD

 

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Majibinci abin godiya, Ma'aboci al'arshi mai girma, wanda ake fata don yaye dukkan bakinciki mai tsanani, ina kyautata yabo ga Ubangiji kuma ina gode masa bisa ni'imominSa ba mai iyakance su face shi cikin wadanda  muka sani da wadanda ba mu sani ba, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, Mai aikata abin da ya so, na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne. abin koyi a dukkan al'amura na shiriya, Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga bawanka Muhammad da iyalansa da sahabbansa wadanda suka taimaki musulunci da aiki da shi da kuma kira zuwa gare shi da jahadi don daukaka kalmarSa har zuwa lokacin da tauhidi ya wargaza duhun shirka,

Bayan haka ku ji tsoron Allah Ubangijinku, ta hanyar tashi da wajibabbu, da kauracewa muharramai za ku rabauta da daddadar  rayuwa da kyakkyawan karshe. Allah Madaukakin Sarki yace : (wancan gida na lahira muna sanya ta ne ga wadanda ba su son dagun kai a doron kasa ko barna, akiba na ga masu takawa).

Ya ku musulmai!

Hakika Allah ya halicci wannan duniya ne don ya cika al'amarinSa a ciki kuma  mashiarSa ta zartu a cikinsu ya yi  hukunci a cikin Su da hukuncinSa da ba mai bin sawu, kuma ya gudanar da su da gudanarwarSa wanda ke cike da hikima da iliminSa da hikimarSa, da rahamarSa da kudurarSa, halittu na sanjawa ne daga wani yanayi zuwa wani yanayi ne tsakanin falalarSa da rahamarSa da adalcinSa da hikimarSa.

Duk abin da ya samu halitta na yalwa da alheri to fa tsaban falalarSa ne da rahamarSa, Allah Madaukakin sarki ya ce :   (Duk abin da ya same ka na kyakkyawa to daga Allah ne) kuma Mai tsarki yace : (Duk abin da Allah zai budewa mutane na rahama to ba mai rike ta kuma abin da ya rike to ba mai turowa  bayanSa kuma shi Mabuwayi ne Mai hikima) Allah Madaukakin sarki ya ce :   (Ashe baku gani cewa Allah ya hore muku abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin kasa kuma ya yalwata muku ni'imominSa bayyanannu da na boyayyu).  Allah Madaukakin sarki ya ce :   (kuma duk abin da ke gare ku na ni'ima to daga Allah ne). kuma Allah Mai tsarki ya ce :  (kuma idan kun kidaya ni'imar Allah ba ku iya lissafa ta, lalle ne Allah Mai yawan gafara ne Mai jinkai).

To ni'imomi mafarinsu daga Ubangiji ne,Mabuwayi da daukaka kuma karshen su ma daga gare Shi ne ba wani da ya cancanci ni'ima daga gare Shi , na daga cikin rahaman Allah ga bayin Shi da ya umarci bayi da su yi godiya bisa ni'imomi domin su wanzu su karu, ya gargadi daga rashin godiya game da su domin kada su gushe ko su kauce, sai Allah Mabuwayi ya ce (ka ambata yayin da Ubangijinku ya ce muddin ku ka gode to lallai zan kara muku idan kuma ku ka butulce , to lallai azabaTa na da tsanani)

Godiya wa ni'imomi ana yi ne ta hanyan tashi da farillu da kuma rashin aikata alfahasha da munkarai , ya kuma tafiyar da ni'imomi cikin abin da zai yardar da Allah Madaukaki da kuma girmama Mai ni'ima Mabuwayi da daukaka , Allah Mai tsarki ya ce :(ku godewa ni'imar Allah in kun kasance Shi kadai ku ke bautawa) kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :(ku yi aikin godiya ya iyalan Dauda , kuma kadan ne daga cikin bayi Na masu godiya) wasu ma'abota ilimi suka ce ''Ba wani lokaci da zai zo a dare ko wuni face a iyalan Dauda akwai mai ruku'i  ko sujada ko kuma wani mai aikin da'a"

 To ka tuna ya kai musulmi ni'imomin Allah a gareka ka yi tunani yanda Ubangijinka ya fari wadannan ni'imomi a gareka alhali kai kuma ba ka cancance su ba a gare Shi , ka yi godiya game da su ga Ubangiji Mai tsarki , kamar yanda Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi godiya ga Ubangijin Shi  da su a fadinsa (Ya Mai yalwan gafara : ya Mai shimfida hannaye biyu da rahama , Ya Ma'aboci dukkan ganawa ya Makura na dukkan kokawa ya mai karamcin rangwame ya Mai girman kyauta ya Mai fara ni'imomi tun kafin cancancanta ya Ubangijin mu ya Shugabanmu Majibincinmu ya makuran bukatanmu ina rokon Ka ya Allah kar ka soya halitta ta da wuta) Hakim ne ya rawaito a cikin Al- mustadrak daga hadisin Amru dan shu'aibu daga babansa daga kakansa kuma ya ce hadisi ne ingantacce .

Tuna ni'imomi da girmama su yana haifar da kaunar Allah da jin kunyarSa,  ta yaya zai kasance daga mai hankali ya fiskanci Mai kyautatawa da muzgunawa, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (ku kaunaci Allah saboda kalace da ya ke baku, na daga ni'imarSa , kuma ku kaunace ni saboda kaunan Allah, ku so iyalan gidana saboda kaunata) Tirmizi ne ya rawaito kuma ya inganta shi da Hakim kuma ya ce sahihi ne daga hadisin Ibnu Abbas  Allah ya kara yarda a gare su , wannan na daga cikin gudanarwan Allah da kyautanSa da alherori da albarkatu da kyawawa ga bayi ba wani da ya isa ya cika ni'imomin Allah da da'a domin falala dukkan shi na Allah ne  Madaukaki sai dai Allah yana yafiya kuma yana rahama yana bada falala kuma yana yarda da kadan na daga ayyuka na kwarai da iklasi da kuma bin sunnah annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (aikin dayanku ba zai shigar da shi aljanna ba sai aka ce : ko kai ma ya Manzon Allah ? sai ya ce ko nima sai dai Allah ya lullubeni da rahamarSa) Ahmad ne ya rawaito daga hadisin Abu Huraira Allah kara yarda a gare su , Ibnu Rajab Allah ya mishi rahama ya ce game da bayi na kwarai : sun kasance suna tuhuman ayyukansu da kula da ayyukansu da tuban su kuma suna tsoron kada a ki karba musu sai hakan ya kasance yana sanya musu tsananin tsoro , da yawan kokari cikin ayyuka na kwarai , Hasan dan basari Allah ya mishi rahama ya ce '' na riski wasu mutane da dayansu ya ciyar da abin da ya kai cikin doron kasa to da bai amunta ba saboda girman zunubi a cikin zuciyansa''  ta tike.

Kamar yanda alheri da ni'imomi da yalwa da hukuncin Allah ne da kaddararSa da falalanSa da rahamarSa haka nan musibu da sharrori  da ukubobi  duka da hukuncin  Allah ne da kaddararSa da a'adalcinSa da hikimarSa , Allah Madaukakin sarki ya ce :(Allah ne Mahaliccin dukkan komai kuma Shi wakili ne ga dukkan komai) An karbo daga Abdullahi dan Amr Allah ya kara yarda a gare shi shi da mahaifin shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (lallai Allah ya rubuta kaddarori na halittu kafin ma ya halicci sammmai da kasa da shekara dubu hamsin , al'arshinSa kuma yana kan ruwa) Muslim ne ya rawaito da Tirmizi .

Allah Mabuwayi da daukaka ya halicci sabuba kuma ya halicci abin da ya ke bayan sabuba , Ubangiji yana halitta da sababi kuma yana halitta ba tare da sababi ba , abin da ya so shi ke kasancewa , abin da bai so ba baya kasancewa , yana yin jarabawa da alheri kuma yana yin jarabawa da sharri , Allah Madaukakin sarki ya ce:(Hakika muna jarabtan ku da sharri kuma da alkairi a matsayin fitina kuma gare mu ne za ku koma) , sai ya bada lada ga masu yin da'a masu godiya kuma ya yi ukuba ga masu sabo masu juhudi (musanta ni'ima) dukkan duniya na gudana ne bisa sunnar Allah yanda Allah ya so kuma ya bayyana a cikin littafinSa to Allah mai girma Mai iko Mai tausayi Mabuwayi ,Mai hikima Shi ne wanda ya kyautata duniya kuma ya ke tunkude shi Allah Madaukakin sarki ya ce :(Yana gudanar da al'amari kuma yana saukar da ayoyi daki daki ko za ku samu sakankancewa game da haduwa da Ubangijinku) AllahMai tsarki ya ce :(Yana gudanar da al'amura ba wani mai ceto face bayan izininSa , wancannin ku Shi ne Ubangijinku ku bauta miShi shin ba za ku yi tunani ba?) Allah Mabuwayi ya ce:(Wanda ke cikin sammai da kasa suna tambayan Shi a ko wani rana kuma yana cikin sha'ani)

An karbo daga Abu Darda'i Allah ya kara yarda a gare Shi ya ce : Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Dukkan ko wani rana yana cikin sha'ani na daga cikin sha'anoniSa ya gafarta zunubai ya yaye bakin ciki ya amsa mai roko , ya dauke wa wasu mutane kuma ya sanyawa wasu mutane) Bazzar ne ya rawaito .

  Da duniya na tafiya ne a cikin zamaninta kaman yanda mutane suke so da jarabawa bai faru ga Annabawa ba amincin Allah su tabbata a gare su da kuma bai kasance suna da kyakkyawan akiba ba su da mabiyansu da kuma wanda suka saba musu ba su kasance suna da nau'o'i  na ukubobi ba sai dai hukunci na Allah ne Shi kadan Shi , Allah Madaukakin sarki ya ce :(ka ce lallai al'amari duka naShi ne) Allah Madaukakin sarki ya ce: (wadanda suke bautawa wani koma bayan Allah ba wani abin da suka mallaka ko da tantanin kwallon dibino ba).

Musibu na kankare laifuka ga musulmi kuma suna daga darajojin shi,

An karbo daga Abu Huraira daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Bala'i ba zai gushe ba ga mumini da mumina a cikin rayinsa da dansa kuma a dukiyarsa har ya hadu da Allah bayi da wani kuskure) Tirmizi ne ya rawaito kuma ya ce hadisi ne hasanun sahihun da Hakim kuma suka inganta shi.

An karbo daga Muhammad dan Kalid Assulami daga babansa daga kakansa ya ce: na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa : (lallai bawa idan wani matsayi ya tsere a gare shi daga Allah to bai riske ta ba da aikin shi sai Allah ya jarrabe shi a jikinshi ko kuma a dukiyansa ko kuma a dansa sannan Allah ya hakurtar da shi a kan haka har ya riski wannan matsayi din da ya tsere mishi daga Allah Madaukaki) Abu dauda ne ya rawaito shi da Ahmad da Abu ya'ala.

Bala'i na zuwa ne gwargwadon karfin addinin mutun da kuma raunin shi, An karbo daga Mus'ab dan sa'ad daga babansa ya ce : na ce : ya Manzon Allah : a cikin mutane wanene ya fi bala'i sai ya ce: (Annabawa sannan sai wadanda suka fi riko sai wadanda suka fi riko, ana jarabtan mutun ne gwargwadon addininsa idan har ya kasance addininsa nada karfi to sai bala'insa ya yi karfi idan ya kasance a cikin addininsa yana da rauni sai Allah ya jarrabe shi gwargwadon addininsa bawa ba zai gushe ba yana haduwa da bala'ai har ya bar shi yana tafiya a doron kasa bai da wani laifi tare da shi) Tirmizi ne ya rawaito kuma ya ce hadisi ne hasan sahihi kuma Ibnu Maja ma ya rawaito shi.

 Musibu kuma da bala'o'i da annobobi suna sauka ne gamagari ; domin a bada lada ga al'umar musulmi saboda hakurin da suka yi da neman lada a wurin Allah kuma abin lura ne ga mutane don su yi tunani cikin kofofi na zunubai da suka aikata domin kada su maimaita irin zunuban saboda su aikata abin da ya fi girma kuma saboda kada a yi musu ukuba da abin da ya fi girma domin su wa'azantu da abin da suka kasance a ciki na daga ni'imomi kafin saukar bala'i domin waraka ko lafiya ta tabbata a cikinsu da aminci da yalwa ta hanyar da'a, Allah Madaukakin sarki ya ce: a cikin sunnoninSa (ya wuci Ubangijinku ya muku rahama idan kun koma kuma muma mu koma)

Allah Mabuwayi da daukaka ba ya dawwamar da annoba sai dai yana dauke ta idan ya so, ku jira yayewa daga Allah , ku fiskanci bala'i da addu'a da kuma komawa zuwa ga Allah domin lallai Ubangiji tsarki ya tabbata a gare Shi Mawadaci ne daga azabtar da mutane sai dai Shi Allah Madaukaki yana so musu ne don su yi aiki na kwarai kuma su kauracewa munanan laifuka, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Idan bayiNa suka tambaye ka game da Ni ka ce: lallai Ni iNa kusa kuma Ina amsa kiran mai kira idan ya kiraye Ni , to su amsa kira Na kuma su yi imani da Ni ko za su samu shiriya) Allah Madaukakin sarki ya ce: ( lallai rahamar Allah kusa ta ke ga masu kyautata wa).

Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma .

 

Huduba ta biyu :

 

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai na shaida ba abin bautawa  da gaskiya sai Allah Shi kadai ya ke ba Shi da abokin tarayya Mai karfi kuma AlMatinu na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne amintacce , Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanKa  da kuma ManzonKa Muhammad da iyalanSa da sahabbanSa baki daya.

Bayan haka : ku ji tsoron Allah cancancin takawa ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci, ya ku bayin Allah ku sani lallai wadatuwan  bawa  da kuma sa'adarsa yana cikin bukatuwansa  zuwa ga Ubangijinsa ne da yakininsa da hakan , Allah Madaukakin sarki ya ce: (Ya ku mutane ku talakawa ne zuwa ga Allah kuma lallai Allah kuma Shi Mawadaci ne abin godiya).

Lallai dukkan tabewa ga bawa da hasararsa da halakarsa gurin zatonsa cewa ya wadatu daga Ubangijinsa kuma ya rudu da kansa da abin da Allah ya bashi Allah Mai tsarki da daukaka ya ce: (lallai wanda ya yi rowa kuma ya wadatu ya karyata kyakkyawa da sannu za mu kama shi da tsanani ba zai amfane shi ba dukiyansa idan ya halaka) , an karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su shi da mahaifinshi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Ni'imomi guda biyu mutane da yawa suna hasara a cikinsu : lafiya da kuma zama haka) Bukari ne ya rawaito .

Ya ku bayin Allah lallai Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce mai yawa .

     

      

 

 


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق