اسم
المترجم : أمين سعد عبد الله
اللغة :
الهوسا
التاؤيخ :
26-10-1441هـ
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga
wanda ya cike manzancin sama da shari'armu,ya sanya Annabinmu ya zama cikamakin
Annabawa da Manzanni ya sanya al'umarmu ta zama tsaka – tsakiya kuma mafi
alherin al'uma da a ka fitarwa mutane, Na
shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin
tarayya, yana halittan abin da ya so ya kuma
zaba, na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne Al Musdafa Zababbe, daga cikin zababbun
zababbu .
Ya shugabanci halittu ba ja , to shi ne bayyananne halittu na baya.
Annabin gaskiya wanda ya zo da
gaskiya mafificin halittu kuma mafi kyaun su a dabi'u da halitta , kuma
mafi fasahan su a wurin furuci.
Hakika ya isar da sako ya sauke
nauyin amana kuma ya yi nasiha wa al'uma
ya yi jahada a tafarkin Allah cancancin jahadi har mutuwa ta zo
mishi tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi da iyalan shoi da sahabban
shi da wanda suka bisu da kyautatawa har
zuwa ranar sakayya .
Bayan haka.
Bayan haka, lalle mafi alherin zance
shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabinmu
Muhammad, kuma sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan bidi'a bata ce,
kuma dukkan bata na wuta.
(Ya ku wadanda suka bada
gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face kuna musulmai)
Ya jama'ar musulmi!
Allah ya kan zabi Manzanni a cikin mala'iku da mutane, hakika ya zabi Muhammad tsira da amincin Alla
su tabbata a gare shi, daga mafi tsada
da kima na ma'adanai kuma ya girmama shi ya fifita shi akan sauran mutane
ya sanya shiryarwar sa shi ne ma'auni na
fifiko kuma da kiyasi bai bata ba , kuma
bai ketare haddi ba , kuma baya yin magana daga son zuciyar sa ,
(maganarsa) bata zamo ba , face wahayi
ne da ake aikowa, (mala'ika) mai tsananin karfi
ya sanar da shi , Ma'abucin karfi
da kwarji sa'annan ya daidaita .
Allah ya tsiratar da
dan -adam ta dalilinsa daga duhun
shirka, da kudurkumin jahilci da zurfin
duhu, daga kuma tabarbarewan halaye da
dabi'u , da juyawar fidira da
kekkecewa da radadi da zunubai da
karkasuwa , sai ya kasance mai kwadayin shiryar da mu da tseratar da mu da kuma samun walwalar mu Allah Madaukakin
sarki ya ce :- (Lalle ne hakika Manzo daga cikin
ku ya je muku . abin da kuka wahala da
shi mai nauyi ne a kansa. Mai kwadayi ne sabo da ku. Ga muminai mai tausayi
ne, mai jin kai .)
An karbo daga Abdullahi dan Amr dan As Allah ya
kara yarda a gare shi cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya karanta fadin Allah a cikin
sha'anin Ibrahim (Ya Ubangiji lalle su
dinnaan sun batar da dewa daga cikin mutane
duk wanda ya bi ni to lallai shi, yana tare da ni )
Isa alaihissalam ya ce
:- (In za ka azabtar da su to bayin ka ne in
kuma za ka gafarta musu to kai mabuwayi ne mai hikima ) sai Manzon
Allah ya daga hannayen sa sai ya ce:- (Ya Allah
al'uma ta al'umata) sai ya yi kuka
sai Allah mabuwayi da daukaka ya ce ya Jibrilu tafi zuwa ga Muhammad ka
ce lallai mu za mu yardar da kai game da
sha'anin al'umar ka ba za mu
musguna maka ba)
An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare su, Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-(Misali na da misalin ku
kamar misalin mutum ne ya kunna
wuta sai
kwari da fari suka rinka kokarin fadawa a cikin ta , shi kuma ya na
kokarin tare su daga gare ta to ni ina
kokarin katange ku ne daga wuta alhali
ku kuma kuna kokarin ficewa daga hanuna ) Muslim ne ya rawaito
Na daga cikin bada kulawarsa ga al'umarsa akwai adana musu
adu'arsa da yayi a ranar da mutum zai gujewa dan'uwansa da mahaifiyarsa
da mahaifinsa, da matarsa da yaransa, kowane mutum a wannan rana da shanin da
ya ishe shi. An karbo daga
Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi cewa Annabi tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi yace : ( ko wani
Annabi na da adu'a karbabbiya, to ni na adana nawa don nemawa Al'umata ceto ,
za a bada ta in sha Allahu ga duk wanda ya mutu cikin al'uma ta bai hada Allah
da wani). Tirmizi ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah!
Hakika Allah ya umarce mu da mu sakawa duk mutumin da ya
kyautata mana, sai yace : (shin akwai wani abu ga
sakayyar kyautatawa face kyautatawa).
(To duk wanda ya yi muku wani alheri to ku
kyautata masa).
Ku saurara! lalle na daga cikin hakkin Annabinmu Muhammad
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da ya ke kan mu shine mu saka
masa bisa kyautatawarsa gare mu, da falalarsa da ke kan mu tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi, to yin salati a gare shi na daga cikin mafi girman
hanyar tsira. Da kuma sadarwa mafi kima, da kusanci mafi girma da da'a mafi
tsarkaka. Kuma yana cikin mafi girman abin da mutum zai raya lokuta da shi. A
ribanya kyawawa da shi, a daga darajoji da shi, a kankare laifuka da shi, a
yaye bakinciki da bacin rai da damuwa, tare da ribin gomomin salati daga Allah.
AlHaitami yace hadisi ne mai daraja ta biyu wanda Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :
( Ba wani bawa da zai tuna ni sai ya min salati face Allah ya rubuta masa kyawawa goma ya kankare
masa laifuka goma, ya kuma daga daraojinsa guda goma.
An karbo daga Ubayyu dan ka'ab Allah ya kara
yarda a gare shi ya ce: na ce ya Manzon Allah
ni ina yawaita salati a gare ka kamar nawa ne zan sanya na daga salati
na ? sai ya ce:- '' iya abinda ka so'' sa ya ce: '' kamar rubu'i daya bisa hudu
yayin da ka so idan ka kara akan haka
to, ya fi alheri a gare ka , sai na ce
kamar rabi fa sai ya ce : '' iya yanda
ka so idan ka kara akan haka ma
ya fi alheri a gare ka sai na ce
to zan yi biyu bisa uku sai ya ce ka yi
iya yanda ka so idan ma ka kara akan
hakan alheri ne a gare ka sai naq ce
to,zan sanya salati na gaba daya a gare ka ,
sai ya ce : - '' to in dai haka
ne za a dauke damuwan ka a yafe ma
zunuban ka Tirmizi ne ya rawaito kuma ya
ce hadisi ne mai daraja na biyu).
Ya ku jamaa'ar musulmi:
Lallai Muhammadu tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi shi ne mafi karamcin mutane , Allah ya hada imani da shi da imani
da kansa da biyayya gare shi da kuma
biyayya ga kansa da kaunar sa da kaunar
Allah da ambaton Allah da ambaton sa , shaidawa na
tauhidi shi ne daya daga cikin alamomi masu girma na
musulunci , adireshin imani
kuma shi ne ramzin zaman lafi kuma jumla na kiran salla ana maimaita
shi a wurin kiran salla a ko wani rana
bisa kunnuwa na shaida ba abin bautawa
da gaskiya sai Allah na shaida Annabi Muhammad Manzon sa ne imani ba ya kulluwa da daya daga cikin shahada guda biyu sai an hada ta da daya
sabo da haka ya wajaba a gare mu da shari'a na Allah da kuma hakkin sa da ke kan mu
da kwadayin sa bisa siran mu da mu cika zukatan mu da kaunar sa
da kimanta shi da girmama shi da
bin sunnar sa da tafarkin sa .
Ku saurara lallai ne yana daga cikin babbar alama ta kaunarsa da kuma wajibi na hakkinsa da sunnarsa da
yake mafi karfi da da'a ga
Ubangijinsa yawaita salati a gare shi (lallai Allah da mala'iku suna salati ga Annabi, Ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a
gare shi da aminci tabbatacce )
.
To ya bayin Allah : Ku yawaita salati ga Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ku motsa harsunan ku da
shi ku danyaya labban ku da shi .
Ya bayin Allah: lallai Allah
hakika ya ribanya ladan salati ga
Annabi ya girmama ma'abotansa da masu
yin sa. An karbo daga Abu Dalha
Al-ansari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ( Manzon Allah ya wayi gari wata rana zuciyan sa tsarkake cikin dadin rai ana gani
a fiskan sa da walwala sai suka ce ya manzon Allah yau ka wayi gari cikin
annashawa a cikin dadin rai ana ganin
haka a fiskarka sai ya ce :- haka ne
wani mai zuwa ya zo min daga wurin Ubangiji na mabuwayi da daukaka sai
ya ce duk wanda ya ma salati guda a cikin al'umarka , to Allah
zai rubuta mishi kyawa guda goma da ita kuma zai goge mishi guda goma na laifuka da ita zai daga darajojin shi guda goma kwatankwacin
su.)
An
karbo daga Abu Huraira Allah ya kara mishi yarda ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a garew shi ya ce:- (Mafi
dacewan mutane gare ni ranar alkiyama
shi ne wanda yafi yawaita min salati )
Ku raya zukata ya ku bayin
Allah da ambaton sa ku yi salati a gare
shi don bin umarnin Allah da koyi da
sunnarsa da wafa'I da hakkin sa da
kusanci zuwa ga Allah da girmamawa da kauna da girmamawa ga Manzon Allah tsira
da amincin Allah su tabbata a gare
shi da kari wurin kyawawan ayuka da kuma
kankare laifuka .
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan
abin jefewa (lallai Allah da mala'iku suna salati ga Annabi, Ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da
aminci tabbatacce mai yawa.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai wanda ya turo
cikin ummiyyai Manzo a cikin su wanda
yana karanta musu ayoyin sa kuma yana
tsarkake su yana sanar da su littafi da
hikima ko da da can sun kasance kafin
haka cikin bata bayyananne .
Ya ku taron Musulmi:
Lallai yana daga cikin mafi
tsadan adu'o'i da zikiri kayan ado mafi
haske shi ne yawaita salati da aminci ga
Annabi zababbe a safiya da maraice da hantsi da yammaci ana yinta ne ga masu kauna alama ce wata sima ce wata shi'ar ne kamar a ranar Juma'a domin shi
ne mafificin ranaku , an karbo daga Aus dan Aus Allah ya kara yarda a gare
shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (lallai
na daga cikin mafificin ranakun ku shi ne ranar juma'a a ciki ne aka halicci Adamu kuma a ciki ne aka dauki ransa a ciki ne kuma za a yi busa a ciki ne kuma za a yi tsawa to, ku yawaita salati a gare ni , domin
salatin ku ana bijiro min da ita Abu
Dauda ne ya rawaito Albani ya kyautata
shi)
Duk wanda yake son Allah ya
yabe shi kuma ya girmama shi kuma ya daukaka shi ya kambama shi Mala'iku masu daraja su ambace shi a daga ambaton shi da darajojin shi da kuma
matsayin shi to ya yawaita salati ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi a ko wani yanayi da ko wani
lokaci da sauran ranakunsu , musamman idan ya zo wurin ambaton shi a magana ne
. An karbo daga Aliyu dan Usaini daga Baban sa cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce :- (lallai
mai rowa shi ne wanda aka ambace ni a gaba gare shi bai yi salati a gare ni ba
Tirmizi ne ya rawaito )
Ya ku bayin Allah:
Lallai salati ga Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
kusanci ne ba tare da kaidi da
lokaci ko kuma wuri ba, sai dai tana
wajabtane a wasu lokuta daga ciki
akwai lokacin da aka ambaci sunan
shi a harshe ko kuma lokacin da ka ji ya yin kiran salla.
An karbo daga Abdullahi dan Amru dan As
cewa ya ji Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa
(idan kun ji mai kiran
salla na kiran salla to ku fadi abin da ya ke fada , sannan ku min salati , duk wanda ya min salati Allah zai mishi
salati da ita guda goma sannan ku nema
min wasila domin wani matsayi ne
a aljanna domin bata dace ba ga kowa sai
wani bawa daga cikin bayin Allah ina
fata kuma in kasance ni ne shi wanda ya
roka min wasila to cetota ta tabbata a
gare shi Muslim ne ya rawaito)
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara mi shi
yarda ya ce Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- ( Hancin shi ya dumbuli kasa duk
mutumin da aka ambace ni bai yi salati a
gare ni ba Tirmizi ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah:
Yin salati ga Annabi yana
zama dole a wurare da dama daga ciki akawai
tahiyan karshe ,da yayin shiga
masallaci, da kuma yayin fita daga gare
shi da yin adu'a da kuma yayin musiba na bakin ciki da yayin haduwa da mutane
da taruwan mutane da kuma
tsakanin kabbarori na idi , da bayan kiran ladani, da wasu wurare daban
da ba wannan ba da lokutan da aka samu
ya zo daga sunna .
Ya ku bayin Allah!
Salati ga Annabi na yiwuwa
da ko wace siga aka yi, da kuma kowace jumla aka hada shi, sigogi daban- daban
sun zo kuma dukkansu suna isarwa ga abin bukata, kuma sun gamsar wurin salati
ga Annabi abin kauna,
An karbo daga Abu Mas'ud Al0Ansari Allah ya
kara mi shi yarda ya ce Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya zo mana muna majlisar sa'ad bin
Ubada, sai Bashir bin Sa'ad ya ce :Allah ya mana umarni da mu maka salati ya
Manzon Allah, to yaya za mu maka salati? Sai ManzonAllah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya yi shuru har muka yi fatan ina ma da baa tambaye shi
ba, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : ku ce ya Allah ka yi dadin tsira ga Muhammad da iyalan Muhammad, kamar yadda ka
yi dadin tsira ga iyalan Ibrahim ka yi albarka ga Muhammad da iyalan Muhammad
kamar yadda kayi albarka ga iyalan Ibrahim a cikin talikai, kai abin godewa ne kuma abin girmamawa, shi
kuma sallama shi ne kamar yadda kuka sani )
An karbo daga Abu Humaid Assa'idi cewa sun ce ya Manzon Allah, yaya zamu yi salati a gare ka sai ya ce ku ce:- '' Ya
Allah ka yi dadin tsira ga Muhammad da
matayen sa da zuri'ar sa , kamar yanda
kayi dadin tsira ga iyalan Ibrahim ka sa albarka ga Muhammad da matayen shi da
zuri'ar shi , kamar yanda ka sa albarka ga iyalan Ibrahim lallai kai abin
godiya ne abin girmamawa .)
Ya ku masoya ga manzon Allah :
Lallai salati ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi na da faidoji da basa kididdiguwa suna da kuma tasiri da amfani da ba
a iya iyakance su, a ciki akwai maslahohi na duniya da lahira wanda ba a iya kwalkwale su a duk lokacin da masoyi ya yawaita ambaton
abin kaunarsa da halarto da shi a zuciyarsa da bijiro da kyawawan sa da ma;anonin sa masu janyo kaunarsa , sai son
ya ribanya , sai shaukinsa kuma ya karu
hakan sai ya kasance abu ne mai karfafa guiwa zuwa ga binsa
, ba abin da ya fi kawo sanyin ido ga masoyi kamar ganin abin kaunarsa,
ba abinda ya fi kawo mishi kwaciyar zuciya
kamar ambaton shi da halarto da
kyawawan sa .
Kuma duk lokacin da mutum ya juya baya daga ambaton sa sai
kaunar sa ya ragu daga zuciyarsa.
Sa'annan ku sani cewa
salati ga Annabi tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi kusanci ne da da'a
da ake bijiro da shi gare shi ku
yi fatan su kasance sun dace da manhajinsa wurin bi , ku yi nesa daga wuce gona da iri da bin son
rai da kirkiran bidi'o'i, duk wanda ya
yi wani aiki wanda babu umarnin mu a
ciki to an maida mishi.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق