اسم المترجم : أمين سعد عبد الله
اللغة : الهوسا
التاريخ : 17-12-1441هـ
Hudubar Juma'a a
masallacin Annabi na Shaikh Abdul Muhsin
Al kasim 17-12-1441AH / 7-8-2020AD
Hudubar farko:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah
Madaukakin sarki muna gode mishi kuma
muna neman taimakonsa, muna neman gafararSa, kuma muna neman tsarin Allah daga
sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu
mai batar da shi , duk wanda ya batar kuma babu mai shiryar da shi, na shaida
ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya,
kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne, tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi da iyalansa
da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.
Bayan haka: ku
ji tsoron Allah-
Ya
ku bayin Allah,- cancancin tsoronSa, takawa ita ce mafi alherin abin ribata
kuma kyauta mafi yawa.
Ya
ku musulmi!
Na
daga cikin juyawan watanni da shekaru ga bayi na daga cikin ni'imomin Allah
masu yawa ga bayi, Allah Mai tsarki ya ce ; (Kuma ya
hore muku rana da wata suna madawwama biyu, kuma ya hore muku dare da wuni.
Kuma ya baku dukkan abin da kuka roke shi, kuma idan kun kidaya ni'imar Allah
ba za ku lissafe ta ba. Lalle ne mutum, hakika, mai yawan zalunci ne mai yawan
kafurci)
Allah
ya tsawatar ga duk wanda bai ribaci lokacinsa ba da abin da zai amfanar da shi a lahira Allah mai tsarki ya ce:- (Ase bamu baku tsawon rayuwa ba wanda ya ci ace mai wa'azantuwa ya wa'azantu? Kuma ga mai
gargadi ya zo muku)
kuma ni'imomi biyu idan mutum bai ribace su
ba yayi asara kuma zai yi nadama game da
su.
Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Ni'imomi guda biyu mutane
suna asara a cikin su, su ne ; lafiya da kuma lokaci ) Buhari ne ya rawaito
Allah
ya yi rantsuwa a ayoyi da dama a cikin littafinSa da wani yanki na lokaci na daga dare da yini
da alfijir da asubahi da la'sar da walaha, hakika ga shi muna kusa da
bankwana da shekara wacce ta tattaro wani abu na rayuwarmu, muna bankwana da ayyukan mu a cikinta, wanda
za a shimfida su a ranar taro a gaba
gare mu, abin mamaki da irin saurin abin
da ya shude ya tafi, kuma abin mamaki da girman abin da ya tattaro
.
Dararraki
da ranaku wasu taska ne na ayyuka kuma
matakai ne na rayuwa na shekaru ana tsofar da abin da ya ke sabo a kusantar da abin da ya ke nesa ranaku na shudewa ga shekaru suna tafiya al'uma
suna bin bayan juna , bisa tafiya
zuwa ga lahira wannan na fiskantowa
wancan kuma na juyawa, wannan na samun
lafiya wani kuma na samun cuta, duka
zuwa ga Allah za su koma. Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Dukkan mutane suna wayan gari akwai mai saida kanshi,
to, sai ya 'yantata ko kuma ya halaka ta ) Muslim ne ya rawaito
A
cikin zamani akwai wasu radadi da ke
juyawa farin ciki, akwai kuma farin ciki
da ke juyawa bakin ciki ranaku na wucewa
ga ma'abotanta , kaman shekaru , shekaru kuma na wucewa ga ma'abotanta kamar
ranaku mai hankali shi ne wanda ya riki wannan a matsayin abin lura, kuma abin
wa'azantuwa Allah Madaukakin sarki ya ce
:-(Allah na juya dare da yini lallai a hakan akwai abin lura ga masu basira
) Shekara kan tafi da abin da ke cikinta abin da bayi suka aikata a cikinta na ayyuka,
za a bijiro musu da ayyukansu , (Ana bawa mutum labari game da abin da ya kaddamar ko ya
jinkirta a wannan ranar) Ka yi dubi zuwa ga takardun ranakun ka da suka shude wani
abu ne ka adanawa kanka a ciki don
lahiran ka? Ka kebanta da kanka ka mata hisabi, hisabi amintacce wanda akwai
matsi a ciki, Maimun dan Mihran -
Allah ya mishi rahama- ya ce :-(Bawa ba zai zama
mi takawa ba har sai ya kasance yana mai
tsanani ga rayinsa fiye da aboki ga abokin shi).
Dare da yini na wucewa ne don su nesatar daga duniya su kusantar zuwa lahira, madalla da bawan da
ya amfana da rayuwarsa ya tsaya tare da
ransa tsayawa na hisabi da kuma zargi yana gyara tafiyarsa kuma yana riskan kusakuransa, yakan bude shafi da daddare na daga abin da ya aikata a wuninsa , idan ya kasance abubuwa ne masu kyau sai
ya doge a kan su, idan kuma ya kasance ayyuka ne na zargi sai ya
tuba daga gare su sabo da shi matafiyi ne
tafiyan da ba komawa
Abu Hatim Dan Hibban - Allah ya mishi rahama -
ya ce:- ( Mafifitan masu hankali matsayi su ne
wadan da suka dimanci yiwa kansu
muhasaba .
Tsinkaya
bisa ga aibobi na rayi da kuma abubuwan da suke tawaya gare ta da laifukanta zai mata linzami daga zalunci,
bawa ya san kan shi kuma ya san makomar shi zuwa ga kabari yana haifar mishi da kankan da kai da kuma
bautawa Allah, ba zai yi alfahari da
aikinsa ba duk yanda abu ya girmama, ba
zai kuma raina zunubai ba komin kankantan su.
Abu Darda Allah ya kara yarda a gare shi yana
cewa :- '' Mutum ba zai zama cikakken fakihi ba har sai ya kama mutane da
laifi a hakkin Allah , sa'annan
kuma ya koma zuwa ga kanshi sai ya
kasance ya fi mata tsanani.
Idan
ka zauna da mutane ka kasance mai wa'azi
ga zuciyarka , domin halittu suna
murakaban zahirin ka ne , Allah kuma yana
murakaban badinin ka , duk wanda badinin
sa ya yi kyau ta hanyar murakaba da ikhlasi to Allah sai ya zayyana zahirin shi da kyau da rabauta.
Sanin
hakkin Allah da girman falalarSa da
baiwarSa da tuna yawan ni'imominSa yana kira zuwa ga Allah , yana sa mutum kuma ya gane gajartawarsa
wurin godewa ni'imomin Allah kuma
lallai ya san cewa babu tsira sai
da komawa zuwa gare shi, ya dace a mishi
da'a ba za a saba mishi ba a gode mi shi
ba za a butulce mishi ba.
Ibnul
Kayyim Allah ya mishi rahama ya ke
cewa:- '' Farkon muhasaba shi ne mutum ya yi
kiyasi tsakanin ni'imarSa mabuwayi da kuma
laifukansa a wannan lokacin ne
zai bayyana mishi lallai akwai banbanci
kuma ya san cewa lallai ba don
wani abu na afuwar Allah da rahamar sa ba
da halaka za a fada da kuma
musiba, nemar laifukan rayi yana
tsarkake ta kuma ya gyara ta Allah Madaukakin sarki ya ce:-(Hakika wanda ya tsarkake ta ya rabauta, hakika kuma yayi
asara wanda ya turbude ta )
Malik dan Dinar ya ce :-''Allah ya yi rahama wa bawan da ya
ke cewa ransa ase ke ba ma'abociya kaza-da – kaza ba? Ase ba ke ce mai kaza-da-kaza ba? Sannan sai ya sa mata linzami sannan ya sa
mata birki sannan ya lizimtar da ita da
littafin Ubangijinta sai ya kasance shi
ne mai jan ragamar ta .
Ba
wani mai nisata wanda zai nisanci Allah
face sai da gafalarsa da mantuwarsa daga muhasabar sa ga Allah , Allah Madaukakin
sarki ya ce (Lallai sun kasance ba su fatan
hisabi) wanda ya fada cikin
munanan ayyuka kuma ya dogara bisa afuwar Allah da rahamarSa to hakika ya yaudari kan sa lallai mai karamci baya fuskantar ayyuka munana (Ya kai mutum
me ya rude ka game da Ubangijin ka Mai karamci )?
Ibn
Kasir Allah ya mishi rahama ya ce:- (Me ya rude ka ya kai dan Adam game da Ubangijin ka wanda ya ke mai karamci
wato mai girma har ma ka je zuwa ga saba
mishi ka fiskance shi da abin da bai
dace ba ).
Hisabi yana yin sauki ga mutanen da suka yiwa kansu hisabi tun a duniya kuma ya
kan yi tsauri ga mutanen da suka riki
wannan al'amari ba tare da muhasaba ba.
Hasanul-Basari Allah ya mishi rahama ya ce :-
'' (Baya dacewa ga mumini face da ya rika yiwa kan shi zargi yana mata mu'ataba sai ya ce da ita me kike nufi da kalma ta, me kike nufi da abinci na, amma
fajiri zai shude ne zai tafi ne da kafansa baya zargin kansa, shi kuma
mumini yana mai tsayuwa a kansa yana
mata hisabi).
Allah
Madaukakin sarki ya ce :-(Lallai ne wadanda suka yi takawa idan wani tashin
hankali daga shaidan ya shafe su, sai su
tuna (Allah) sai ga su ,
sun zama masu basira .
Taka-tsantsan wurin afkawa cikin kuskure da barin zunubai shi ne ya fi sauki akan neman tuba kuma da zargin rayi bisa ga gajartawa
cikin da'a domin ranaku a gare ka basu dauwama kuma ba ka sani ba yaushe ne za
ka kaura daga duniya kuma ka yiwa kan ka
magana menene kika gabatar a ranakun da su ka shude kuma
wani shiri kike yi don ranaku masu fiskantowa?
Umar
Dan Khaddabi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce:-
'' Ku yiwa kan ku hisabi kafin a yi muku
hisabi ku aunata kafin a auna ku
ka rika bibiyan ranka a farkon
ko wani rana wurin kiyaye
sallolin nan guda biyar a masallatayya
cikin jam'i tare da musulmai kana neman guzuri na ilimi mai amfani tare da
kai-komo wurin yada shi da kuma ilmantar
da shi da kiyaye harshen ka daga
abubuwan da suke muharramai da karya da rada
da batsa da alfasha kuma ka
kasance kana da tsantseni cikin abin da ka ke ci da abin da kake sha, ka nisaci abin da baya halatta ka yi kwadayin biyayya wa iyaye ka sada zumunci, ka yawaita
ma'arufi da makusanta da na nesa ka
tsarkake zuciyan ka daga hasada da gaba
da kiyayya ka kiyaye daga aukawa cikin
mutuncin musulmai ka yi kokari wurin
tashi da wato sha'ira na umarni da
kyakkyawa da hani ga mummuna da bada hakkokin
yara kuma da iyali bisa ga fiskan da ya
dace mafi kamala ka rintse idanuwan ka daga kallon abin da ya
ke muharramai sawa'un a hanyoyi ne ko
wanin su.
To dare da wuni suna nesantarwa ne daga duniya kuma suna kusantarwa
ne zuwa ga lahira, madalla da bawan da ya amfana da rayuwarsa
dukkan wayan gari rana na
faduwa yana maka gargadi ne cewa fa
wani abu na shekarunka ya ragu mai hankali shi ne wanda ya wa'azantu a
jiyansa ya yi kokari a yau dinsa ya
shirya don gobensa ka dauki mataki na shiri
domin tafiyan da take gaban ka,
yi guzuri domin tafiyan ta kusanto ,
mafi alherin guzuri shi ne wanda a ka hada da tsoron Allah, mafi darajan mutane a wurin Allah shi ne wanda ya fi su tsoron shi .
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan abin jefewa
(Ya ku wadan da suka yi imani ku ji tsoron Allah kuma rayi ta yi
dubi zuwa ga abin da ta gabatar don gobe . ku ji tsoron Allah lallai Allah Mai
bada labarin abin kuke aikatawa ne).
Allah
ya sa mini albarka ni da ku a cikin Alkur'ani mai girma.
HUDUBA
TA BIYU
Dukkan
yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa
kyautatawanSa, godiya ta tabbata
gare shi bisa datarwanSa da baiwanSa, na shaida babu abin bautawa da
gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya ina mai girmama sha'aninSa na shaida Annabi
Muhammad bawanSa ne kuma Manzon sa ne
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban
shi da aminci tabbatacce mai kari .
Ya
ku musulmi:-
Shekarun dan adam a nan duniya na
rayuwarsa su ne kasonsa, idan ya
kyautata ribatarsu a nan duniya cikin
abin da zai amfane shi a gidan lahira to ya ci riba a kasuwancinsa, to idan
kuma ya munanta ribatan su ya yawaita sabo da laifuka to ya yi hasara a
kasuwancinsa, mai dace shi ne wanda ya yi hisabi wa kansa kafin Allah ya masa,
ya ribaci lokacinsa ya san maganinsa daga cutarsa, bai yi sake ba har a yi
mishi sakiya, alheri na cikin da'a sharri kuma na cikin sabo.
Rayuwa
fage ne mai fadi na kyawawan ayyuka, jinkirta aiki da cewa sai nan gaba bai
haifar da wani abu sai nadama, tuba na goge kuskure, mai samun walwala shine
wanda ya adana ayyuka na kwarai a tsawon rayuwarsa. Shakiyyi shine wanda
gabbansa suka shaide shi da munanan laifukansa.
To
ku kiyaye ranakun rayuwanku kafin ku kadaita a kabarinku, ku ribaci ranakun rayuwarku
kafin kwacewar lokaci, ku girmama masaukinku na sabon rayuwa da da'a.
Sannan
ku sani Allah ya umarce ku da salati da aminci ga AnnabinSa.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق