الجمعة، 21 أغسطس 2020

Lura

 

اسم المترجم :أمين سعد

اللغة : الهوسا

التاريخ 2/1/1442هـ

Hudubar masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na 2/1/1442 na shaihk Ali dan Abdurrahman Alhuzaifi

 

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Masanin gaibi Mai juya zukata Mai yawan gafarta zunubai, kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi bisa ni'imominSa da wani bai iya kididdige su  in ba shi ba,  na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, da mulki da godiya na shi ne kuma mai iko ne ga dukkan komai, na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne, kuma manzonSa ne mai albishir mai gargadi, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka, bisa ga bawanka Muhammad da iyalansa da shabbansa wadanda Allah ya jibince su to madalla da Majibinci kuma madalla da Mataimaki.

Bayan haka, ku ji tsoron Allah Mai tsarki a boyenku da bayyanenku, domin ya jibinci lamuranku ya kuma gyara muku halayenku, Takawa ita ce tafarkin mutanen kwarai masu rabauta  rasa ta kuma shi ne bayyananniyar hasara .

 YA KU BAYIN ALLAH

Ku kasance daga ma'abota basira da imani, ku bi tafarkin ma'abota hankula  da kyautatawa, ma'abota hankula su ne wadanda  hankulan su ke lafiyayye mikakke, masu lafiyayyan fidira  su ne wadan da suke amfana da wahayi kuma suke fahimtar abin da Allah ya saukar,  bisa muradin Allah da kuma muradin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  suna aiki da maganar Allah domin fatar lada kuma suna tsoron ukubarSa   .

Allah Madaukakin sarki ya ce :-(Kuma wadan da suka  nisanci dagutu da su bauta masa suka koma zuwa ga Allah, su na da kyakkyawan bishara, to, ka yi albishir ga bayi Na, wadanda suke jin magana kuma su bi mafi kyau daga ciki, wadan nan su ne wadan da Allah ya shiryar da su kuma wadan nan su ne ma'abota hankula ).

Lura na daga cikin ayyukan masu hankali masu basira, na daga cikin ayyuka na basira kuma da gwanancewa  shi ne ; lura yana shiryarwa zuwa  ga rabauta da tsirata daga abubuwa dake halakarwa, kuma yana datar da ma'abotan shi zuwa aiki na kwarai  ya nusar da  ma'abotan shi  zuwa ga tafarkin mutane  na gari  masu neman gyara  karshen shi kuma yakan koma ne zuwa ga alheri,  wanda aka haramta mishi lura to wa'azi ma ba zai amfane shi ba, zai fada kuma cikin halaka kuma zai bi sha'awe -sha'awen ransa  zai bi tafarkin mabarnata kuma ya zama ya yi nadama.

Lura shi ne kaura daga hali na mushahada ko hali da ya shude wanda yake akwai ukuba da azaba zuwa hali mai kyau  abin a yaba a hankalce da a shar'ance, ta hanyar nisatar sabuban ukuba da kuma azaba, ko kuma kaura daga tarihin salihan bayi da abin da Allah ya karrama su da shi na aiki da ayyukan su da kuma bin  sawun su ko kuma tuntuntuni  cikin dabi'un halittu da sanin sirrin da ke ciki da sifofin su ,  da hikiman da ya sa mahaliccin su ya halicce su,  da kebantar da shi da tauhidi da da'a ga Allah  tabaraka wa ta'ala.

Hakika Allah Mabuwayi da daukaka ya halicci halittu  ya sanyawa duniya wata sunnan da take tafiya a kai, sai ya sanya biyayya  sababi ne na dukkan alheri a nan duniya  da lahira, ya sanya kuma saba mishi sababi ne  na dukkan sharri a duniya da lahira .

Shin akwai wanda za ka ga ya tsiyace sabo da biyayya wa Allah  ko kuwa za ka samu wanda ya samu rabauta sabo da sabon Allah, hakika Allah ya bamu kissa tsarki ya tabbata a gare shi  a cikin littafinSa  kuma Manzon Allah ma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kissanta mana , daga kissoshi na halayen Annabawa da Manzanni da muminai da abin da ke ciki na abin lura, da abin koyi ga wanda ke bayan su, da kuma tsirata daga ukubobi,  da rabauta da dukkan alhairu  wanda a cikin shi za ka samu kyakkyawan karshe,  da wanda a cikin su akwai akiba mafi kyau da kuma darajoji  Allah Madaukakin sarki ya ce :-    

(Hakika a cikin kissoshin su ya kasance akwai abin lura  ga ma'abota hankula ).

Ba zance ne na kage ba, sai dai gaskatawa ne ga abin da ya gabata  da kuma bayani daki-daki na dukkan  komai  da shiryarwa da rahama ga mutane masu imani .)

Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Sa'annan muka tseratar da ManzanninMu da wadan da suka yi imani  hakanan ne ya kasance hakki a gare mu da mu tsiratar da muminai).

Allah Mai tsarki ya fadi game da masu karyatawa ( Ya ce suka yi makirci muma muka mai da musu makircin su a halin ba su sani ba, to ka dubi karshen makircin su yanda ya kasance;   shi ne Mun rusa  su da mutanen su baki daya  wadancan gidajen su ne ba komai  sakamakon zalunci da suka yi lallai  a cikin wannan akwai abin lura ga mutane  da suka gane,  muka tsiratar da wadan da suka yi imani kuma sun kasance suna tsoron Allah).

 

Yayin da Allah ya bamu kissoshi masu yawa  na daga Annabawa amincin Allah ya tabbata a gare su a cikin suratul Al-shu'ara sai ya rufe kissan  bayan tsiratan Manzanni da muminai tare da su sai ya rufe kissan da fadinSa  (Lallai a cikin haka akwai abin lura amma mafi yawan su  ba su kasance suna  muminai ba•  lallai Ubangijinka shi Mabuwayi ne kuma mai jin kai.)

Ibnu Kasir Allah ya mishi rahama yake cewa  '' Lallai a cikin haka akwai aya, wato a wannan kissa din da abin da ke cikin ta na ban mamaki  da kuma nasara da karfafan bayin Allah muminai,  ta hanyar dalilai da hujjoji na yanke da kuma hikima wanda takai kololuwa".

Lallai Ubangijinku shi ne Mabuwayi ai Madaukaki da ya buwaya daga dukkan komai, kuma mai yin galaba akan abun kuma ya rinjaye shi, ga rahama kuma wato ga halittun sa baya gaggawa da  ukuba ga wanda ya saba mishi sai dai yana saurara mishi ya jinkirta mishi  sannan ya damke shi damka irin na Mabuwayi Mai iko.

 

 Sa'id bin Jubair ya ke cewa Allah Mai jin kai ne ga wanda ya  tuba zuwa gare shi  kuma ya komo zuwa gare shi , maganar ta tike.

 A fadin Allah Madaukakin sarki a kissan mutanen ludu  tsira da amincin Allah su tabbata a gare su.

 

(Lallai a cikin haka akwai ayoyi ga masu hankula).  Katada ya ke cewa ;  masu hankula ana nufin masu lura Albagawi shi ya ambata shi a cikin tafsirinsa ba masu amfana da abubuwan da ke faruwa na tarihi da hikimomi da ke ciki na yanayi face  wadanda suke  masu lura masu tunani  wadan da suke koyi da ma'abota na kwarai da mutane na gargaru,  masu neman gyara  suna kyale mutanen barna  da masu kawo barna, amma wanda baya lura baya wa'azantuwa baya muhasaba wa kanshi baya aiki don lahiransa, addinin sa baya hana shi hankalin shi baya hana shi yin abu mara kyau da laifuka to, wannan kamar dabba  ya ke,  Allah Madaukakin sarki ya ce:- ( Ko kana zaton cewa mafiya yawan su suna ji ne ko suna hankaltuwa ,  a'a  su dinnan ba komai ba ne  sai kamar dabbobi ne, kai sun fi ma dabbobi bata).

Ya zo a cikin Hadisi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  (Lallai mumini idan ya yi rashin lafiya ciwo ya same shi sannan ya mutu  zai kasance kaffara ne a gare shi game da zunuban shi cikin abin da ya shude idan ya bashi lafiya sai ya kasance kaffara ne  cikin abin da ya shude da kuma wa'azi ga abin da ya fiskanto lallai munafukai idan dayan su ya yi rashin lafiya sannan aka warkar da shi to sai ya kasance kamar rakumi ne da iyalan shi suka kunce shi sannan suka sake shi  bai san sabo da me aka sake shi ba,  bai san kuma sabo da me aka kunce shi ba Nasa'i ne ya rawaito).

 

Allah bai ambaci tarihin Annabawa ba da Manzanni da cikamakinsu Annabinmu Muhammad ba face don mu yi lura da tarihin nasu,  mu yi  koyi da shiryarwar su da halayen su mu bi tafarkin su hakika kuma Allah ya umarci Annabin mu Muhammad da ya yi koyi da su  sai yake cewa  wadannan su ne Allah ya shiryar to ka yi koyi da shiryarwar su Allah Madaukakin sarki ya ce :-(To ka yi hakuri kamar yanda ma'abota  azama suka yi hakuri na daga Manzanni)

 Allah Madaukakin sarki ya ce game da muminin Yasin  (Ya ku mutanena ku bi manzanni ku bi wanda bazai tambaye ku lada ba kuma su dinnan suna shiryarwa ne)

Cikamakinsu Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, wanda da shi ne Allah ya goge sauran shario'i gaba daya,ya turo shi da mafi kamalan addini da sharia ta har abada, kuma Allah ya dauki nauyin duk mutumin da ya yi riko da koyarwarsa da zai rayu  rayuwa daddada a duniya da lahira, kuma zai shigar da shi gidan aminci tare da mafi alherin halittanSa,  Allah Madaukakin sarki ya ce:(Duk wanda ya ke wa Allah da Manzo biyayya to wadannan suna tare da wadanda Allah ya yi wa ni'ima na daga Annabawa da siddikai da shahidai da salihan bayi, to madalla da wadannan abokan zama).

To wani irin karramawa ne ya fi wannan? Wani irin daukaka ne da zai yi kusa da wannan matsayi? Kuma kamar yadda Allah ya kissanta mana kissoshin Annabawa amincin Allah ya tabbata a gare su, da wadanda suka yi imani da su don mu yi koyi ne da su ne mu bi tafarkin tsira tare da su, kuma mu yi lura da tarihin rayuwarsu, mu san irin halin da suka shiga, kamar yadda ya bamu labarin wadanda suka karyata su, da wadanda suka ja da gaskiya suka yi girman kai daga binsu, wadanda suka fifita rayuwar duniya akan lahira, masu bin soye-soyen rayukansu da abubuwan jin dadin duniya, don mu yi lura da ukubar da aka musu, kuma mu dauki izina da abin da ya faru da su na walakancin duniya da azabar lahira, don mu kiyaye kanmu daga tsinuwar Allah da ta tabbata a kan su,   Allah Madaukakin sarki ya ce:(Da Adawa da samudawa alhali kuwa lalle alamun azaba sun bayyana a gare su daga gidajensu, kuma shaidan ya kawata musu ayyukansu, sabo da haka ya kange su daga hanyar Allah, kuma sun kasance masu basira. Kuma Karuna da Fir'auna da Hamana, kuma lalle Musa ya je musu da hujjoji, sai suka yi girman kai a cikin kasa, kuma basu kasance masu tserewa ba. Saboda haka kowannensu mun kama shi da laifinsa: wato daga cikinsu akwai wanda muka aiki iskar tsakuwa a kansa, kuma daga cikinsu akwai wanda tsawa ta kama, kuma daga cikinsu akwai wanda muka birkice kasa da shi, kuma daga cikinsu akwai wanda muka nutsar. Ba ya yiwuwa ga Allah ya zalunce su, amma sun kasance kansu suke zalunta.

 Allah Madaukakin sarki ya ce:(kowannensu ya karyata Manzanni sai Kyacewa ta tabbata).

  Allah Madaukakin sarki ya ce game da kissar Banu nadir :(To ku yi lura fa ya ma'abota basirori)

Tarihin Manzanni amincin Allah ya tabbata a gare su tare da masu karyata su, masu saba wa Allah da ManzonSa abu ne da mutane suka san shi, al'umar karshe sun san shi daga al'umar da farko, kuma yana cikin hujjojin Allah mafi girma ga halittunSa wurin karfafar gaskiya da ma'abotarta, sanin tauhidi da kira zuwa gare shi da taimakawa masu kadaita Allah, haka kuma hujja ne wurin rusa karya (bata) da shirka da yin gargadi game da shi, da ukubobi na mushrikai masu bijirewa, kuma tarihi shine bigere ko mahallin lura da daukan izina ga daidaiku da iyalai da dabakoki da al'umu da ma kasashe, duk wanda ya amfana da shi zai tsira, wanda bai amfana da shi ba kuma sunnar Allah zata bi ta kan shi sai ya samu tawaya, Allah Madaukakin sarki ya ce:(Sunnar Allah wacce hakika ta shude cikin bayinSa kuma kafurai sun yi hasara a wancanninka).

 Amma shi lura da dabiun halittu da binciko hikimomin da ke cikinsu da sifofinsu, da tunani game da farar da halittarsu to gayarsa da babbar manufarsa shine kadaita Allah  Mabuwayi da Daukaka da bauta masa da masa biyayya, wanda ya kadaita da halitta shine abin bauta da gaskiya Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma lalle ne kuna da abin lura a cikin dabbobin ni'ima muna shayar da ku daga abin da yake a cikin cikunansu daga tsakanin tukar tumbi da jini, nono tsantsa mai saukin hadiya ga masu sha.)

    Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma Allah yana juyar da dare da yini, lalle ne a cikin wannan akwai abin lura ga masu basira).

Allah Madaukakin Sarki ya ce : (ka ce ku dubi abin da ya ke cikin sammai da kasa, kuma ayoyi da gargadi basu wadatarwa ga wadanda basu yin imani).

    Lalle tunani cikin halittun Allah ibada ne ga musulmi, daukan izina ga wadannan halittu kuma yana kara imani ga musulmi da tabbatuwar yakini, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Lalle ne a cikin sammai da kasa akwai ayoyi ga masu imani).

To tunani da lura na tabbatar da mai shakku, kuma yana raya zukata, yana haskaka basira, yana daidaita halaye da dabiu, kamar yadda bijirewa tunani kan kekasar da zukata, kuma yana haifar da gafala, yana jan ragama zuwa ga nadama ya kuma jefa mutum cikin sabon Allah.   

   Daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi yace lalle Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a lokacin da ya yi isra'i ya ce : ( Yayin da na sauko saman duniya sai na dubi kasa da ni sai ga  wani irin iska da sauti da hayaki, sai nace : menene wannan ya kai jibrilu? Sai yace wadannan shaidanu ne suke kona wuta a idon dan adam wai don kar yayi tunani cikin mulkin sammai da kasa, ba don haka ba da sun ga abin al'ajabi).Ahmad ne ya rawaito.

Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Lalle ne wadanda suka ji tsoron Allah idan wani tashin hankali daga shaidan ya shafe su, sai su tuna Allah sai ga su sun zama masu basira. Kuma 'yan'uwansu shaidanu suna taimakonsu cikin bata Sannan basu gajartawa.)

Allah ya sa min albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma.

Huduba ta biyu

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah,  wanda ya haskaka zukatan masoyanSa da Alkur'ani, ya kuma haskaka basirarsu da Imani, ya kawata ayyukansu da kyautatawa, ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode masa, bisa ni'imominSa da ba mai iya iyakance su in ba shi ba, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bai da abokin tarayya, Mulki da godiya na shi ne, Mai jinkai Mai rahama, kuma na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, wanda aka kebantar da shi da dunkulallun kalmomi gamammu da cikan bayani, Allah ka yi dadin tsira da aminci bisa ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalan shi da sahabban shi da wadanda suka biyo su da kyautatawa, bayan haka:

To ku ji tsoron Allah Madaukakin sarki zai gafarta muku ya tattaro muku alheri a rayuwarku da bayan mutuwarku.

Yaku bayin Allah! Ku yi wa kanku hisabi kafin a muku hisabi, dayanku ya yi dubi zuwa ga akibar al'amura, da karewar ajali duk wanda luransa ya yawaita to kura-kuransa zasu karanta, wanda ya kiyaye sabawa Allah da laifuka to zai rayu cikin aminci, kuma za a datar da shi zuwa ga kyakkyawan karshe, mai rabauta shine wanda ya wa'azantu da waninsa, hasararre shine wanda da shi waninsa ya wa'azantu.

Hakika Allah Madaukakin sarki ya zargi wadanda suka bi son ransu ba su yi lura ba, basu wa'azantu da labarai da suka zo musu ba, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma suka karyata suka bi soye- soyen rayukansu, alhali kowani al'amari tabbatacce ne. Hakika labarai ya zo musu wanda cikinsa akwai abin gargadi)

  Ku saurara ! lalle Allah Madaukakin sarki yana da wasu sunnoni a rayuwa wurin sakayya da lada ko ukuba, wanda ya nemi ja da yin Allah sai sunnar rayuwa ta nesatar da shi ya dunkufe  ya fado ya kaskanta, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Hanyar Allah ga wadanda suka shude kafin nan kuma ba za ka samu sauyi ba ga hanyar Allah).   

Ya zo a hadisi :(ku yawaita ambaton mai katse jin dadi mutuwa).

Wanda ya tuna mutuwa aikinsa zai yi kyau, wanda ya manta mutuwa aikinsa zai munana.

Ya ku bayin Allah! (Lalle Allah da Mala'ikunSa suna salati ga Annabi yaku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce).

To ku yi salati da aminci ga shugaban mutanen farko da na karshe kuma shugaban manzanni.

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق