الخميس، 30 مارس 2017

Istigfari (Neman gafar)

Hudubar Masallacin Annabi  na shaikh Aliyu  Abdurrahman Alhuzaifi 3/7/1438 Ah
Da sunan Allah mai rahma mai jin kai
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mai rahma Mai jin kai masani mai hikima ma'boci mai falala may girma ina keawtata yabo da ubangijina kuma ina gode mishi ina tuba zuwa gare shi ina neman gafararsa,  na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya ma'aboci al'arshi mai girma. na shaida Annabinmu  kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma manzonsane ma'abocin  halaye masu girma, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci ga bawanka kuma manzonka  Muhammad da iyalansa da sahabbansa masu da'awa(kira zuwa ga Allah)Masu shiryarwa zuwa ga tafarki mikakke, bayan haka,
Ku ji tsoron Allah da aiki don neman yardarsa da kauracewa abin da ya haramta don ku rabauta da yardarsa da ni'imar aljannarsa kuma ku tsira daga fushinsa da ukubarsa,
Ya ku musulmai! Lalle ubangijinmu Allah mai girma da daukaka ya yawaita kofofin alheri, da hanyoyin ayyuka na da'a da falala da rahama da kyauta da karamci daga Ubangiji Mabuwayi da daukaka, don musulmi ya shiga daga kowane kofa na alheri, kuma ya bi kowane tafarki na da'a, don Allah ya gyara masa duniyarsa kuma ya daga darajarsa a lahirarsa, don Majibinci Mai daukaka  ya karrama shi da daddadar rayuwa, da walwala a rayuwarsa kuma ya samu ni'ima zaunanniya, da yardar Ubangiji bayan mutuwarsa. Allah Madaukakin sarki ya ce :(sai ku yi tsere zuwa ga ayyukan alheri, inda kuka kasance duka Allah zai zo da ku gaba daya, Lalle ne Allah akan kome mai ikon yi ne.)
Allah Madaukakin sarki yace game da Annabawa wadan da su abin koyi ne  ga mutane tsira da amincin Allah su tabbata a gare su gaba daya : (Sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri. Kuma suna kiran mu akan kwadayi da fargaba. Sun kasance masu saunar (aikata sabo) gare mu.
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da Mu'az : ( Ase ba zan nusar da kai ga kofofin alheri ba, Azumi garkuwa ne, sadaka na tunkude kusakurai, kamar yadda ruwa ke kashe wuta,da  sallar mutum cikin dare, sai ya karanta : ( Sasanninsu na nisanta daga wuraren kwanciya, suna kiran Ubangijinsu bisa ga tsoro da tsammani kuma suna ciyarwa daga abin da muka azurta su.Sabo da haka wani rai bai san abin da aka boye musu ba na sanyin idanu, domin sakamako ga abin da suka kasance suna aikatawa).sannan yace ase ba zan baka labari ba ga tushen al'amura da ginshikinsa, da kololuwar tozonsa? Sai na ce : E, a bani labari ya Manzon Allah.sai ya ce : Tushen al'amari shine musulunci, ginshikinsa shine salla kololuwar tozonsa shi ne Jahadi a tafarkin Allah ) Tirmizi ne ya rawaito ya kuma inganta shi.
Na daga cikin kofofi na alheri da hanyoyi na ayyukan kwarai da da'a da sabuba na kankare munanan zunubbai  akwai neman gafara (Istigfari), Istigfari sunna ne na Annabawa da Manzanni  tsira da amincin Allah su tabbata a gare su, Allah Madaukakin sarki yace  game da mahaifa biyu na mutum  amincin Allah da rahamarsa  da albarkarsa ya tabbata a gare su, :
(suka ce ya Ubangijinmu ! Mun zalunci kanmu. Kuma idan ba ka gafarta mana ba, kuma ka yi mana rahama, hakika muna kasancewa daga masu hasara)
Nuhu amincin Allah ya tabbata a gare shi ya ce : (ya ubangiji na ka yi mini gafara (ni) da mahaifa na biyu, da wanda ya shiga gida na yana muminai maza da mata).
Allah mabuwayi da daukaka yace game da Ibrahim amincin Allah ya tabbata a gare shi, : (ya Ubangijinmu ! ka yi gafara gare ni, kuma ga mahaifana, kuma da muminai, a ranar da hisabi ya ke tsayawa).
Allah madaukaki yace game da Musa amincin Allah ya tabbata a gare shi :(Yace : Ya Ubangiji na ka gafarta mini ni da dan'u wa na , kuma ka shigar da mu a cikin rahamarka alhali kuwa kai ne mafi rahamar masu rahama.!)
Allah madaukai yace : Kuma Dawuda ya tabbata cewa mun fitine shi sabo da haka ya nemi Ubangijinsa gafara kuma ya fadi yana mai sujada, kuma yana maida al'amari ga Allah.)
Allah Madaukakin sarki yace yana mai umarni ga Annabinsa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, (saboda haka ka sani cewa babu abin bautawa face Allah kuma ka nemi gafara ga zunubinka, kuma sabo da muminai maza da muminai  mata).  
Na daga cikin koyarwar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yawan istigfari, tare da cewa Allah ya gafarta masa abin da yan gabata na daga zunuban shi da abin da ya jinkirta, an karbo daga Abdullahi dan umar رضي الله عنهما (ya ce: mun kasance muna kirga wa annabi صلى الله عليه وسلم  a majlisi daya fadinsa ya ubangiji ka gafarta mini ka karbi tubana domin kai mai yawan karban tuba ne har so dari ) Abu Dawuda ne ya rawaito da Tirmizi kuma yace hadisi ne hasan kuma ingantacce,
  kuma an karbo daga A'isha رضي الله عنها  ta ce (Annabi ya kasance yana yawaita cewa  subhanallahi wa bi hamdihi  astagfirullaha wa atubu ilaihi"  kafin mutuwarsa ) Buhari  da Muslim ne suka rawaito,  kuma an karbo dagaAbu Huraira رضي الله عنه  yace : (Ban ga wanda yafi manzon Allah  صلى الله عليه وسلم yawaita fadin  cewa Astagfirullaha wa atubu ilaih ba )  Nasa'i ne yarawaito
 (mai tsira da amincin Allah sutabbata a gareshi ya kasance yana cewa bayan sallama daga salla: Astagfirullah sau  uku) Muslim ne ya rawaito daga hadisin Sauban Allah ya kara yarda a gare shi.   
Sa'annan daga bisani sai ya fadi zikirorin da aka shar'anta fadinsu a bayan sallolin farilla.

Kuma lallai NEMAN GAFARA Dabi'ar salihai ne, kuma aiki ne na mutane masu biyayya, da takawa, kuma alama ce ta muminan mutane,    Allah (تعالى) yana cewa:
"Ya Ubangijinmu! Ka gafarta mana zunubanmu, kuma ka kankare mana munanan aiyukanmu, kuma ka dauki rayukanmu tare da masu yin biyayya" [Ali-imrana: 193].
Kuma Allah (تعالى) yana cewa:
"Wadanda suke cewa: Ya Ubangijinmu! Lallai mu mun yi Imani; sai ka gafarta mana zunubanmu, kuma ka katange mu daga azabar wuta   *   Masu hakuri, da masu gaskiya, da masu kankan da kai, da masu ciyarwa, da masu yin istigfari a lokutan asuba" [Ali-imrana: 16-17].
Alhasan yace: Sun yi ta sallah har zuwa lokacin sahur, sannan suka fiskanci ibadar neman gafara.
Kuma Allah (تعالى) yana cewa:
"Sune kuma Wadanda, idan suka aikata wata alfasha, ko suka zalunci kayukansu su kan tuna Allah; sai su nemi gafarar zunubansu, Kuma wanene zai gafarta zunubai idan ba Allah ba, kuma basa dogewa akan abinda suke aikatawa, alhalin suna sane" [Ali-imrana: 135].
Ibnu-rajab yace: ((Shi kuma neman gafara daga zunubai shine: Neman lullube su.    kuma lallai bawa yana da matukar bukata zuwa ga hakan; saboda ko-yaushe ya kan yi kuskure cikin dare da rana. Kuma lallai ambaton TUBA DA NEMAN GAFARA ya maimaitu a cikin alkur'ani, da kuma yin umurni da su, da kwadaitarwa zuwa gare su)). … Maganarsa ta kare.

            Kuma lallai NEMAN GAFARA DAGA Ubangiji mabuwayi da daukaka Allah ta'alah yayi alkawari da cewa zai amsa, kuma zai yi gafara.

            Kuma lallai an shar'anta cewa Bawa ya rika neman gafara a kan zunubi aiyananne, sananne; saboda fadin Annabi (صلى الله عليه وسلم):
"Lallai bawana ya aikata wani zunubi, Sannan yace: Ya Ubangijina, lallai ni na aikata wani zunubi; sai ka gafarta mini shi, Sai Allah yace: Bawana lallai ya san cewa  yana da Ubangijin da yake  gafarta zunubai, ya kuma tafiyar da shi, to lallai na gafarta wa Bawana", Bukhariy da Muslim suka ruwaito shi daga hadisin  Abu-hurairah (رضي الله عنه).

            Kamar yadda shari'a ta zo da cewa: Bawa ya rika neman gafara, a sake ba kaidi; sai yace: Ya Ubangijina! ka gafarta min, kuma kayi mini rahama. Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma ka ce: Ya Ubangijina! Ka yi gafara kuma ka yi rahama, domin kai ne mafi alherin masu rahama" [Mu'uminuna: 118].
Kuma lallai Annabi (صلى الله عليه وسلم) ya kasance yana sanar da mutumin da ya musulunta da cewa ya rika yin addu'a da wadannan kalmomin :
"Ya Allah ka yi gafara a gare ni, ka yi mini rahama, ka shiryar da ni, ka bani lafiya, ka azurta ni", Muslim ya ruwaito shi daga hadisin Darik dan Ashyam (Allah ya kara yarda a gare shi).

            Kamar yadda aka shar'anta: Bawa ya rika nema daga Ubangijinsa cewa ya gafarta masa zunubansa gabadayansu; wadanda ya san su da wadanda bai sansu ba; wannan kuma saboda zunubai dayawa babu wanda ya sansu sai Allah, kuma lallai bawa za a kama shi akansu;    Ya zo daga Abu-Musa al'ash'ariy (رضي الله عنه) daga Annabi(صلى الله عليه وسلم) lallai shi ya kasance yana yin addu'a da wannan addu'ar:
"Ya Allah! Ka gafarta min kurakuraina da jahilcina, da ketare iyakana cikin lamari, da abinda kai ne ka fini saninsa. Ya Allah! Ka gafarta mini gaskena da wasana, da kuskurena da gangancina, kuma dukkan haka, akwai shi a wurina. Ya Allah! Ka gafarta mini abinda na gabatar da wanda na jinkirta, da abinda na boye da abinda na bayyanar, da abinda kai ne ka fi ni saninsa, kai ne Mai gabatarwa, kuma kai ne Mai jinkirtarwa, kuma lallai kai akan kowani abu mai iko ne", Bukhariy da Muslim suka ruwaito shi.
Da kuma saboda fadin Annabi (صلى الله عليه وسلم):
"Shirka a cikin wannan al'ummar tafi buya fiye da tafiyar tururuwa, Sai Abubakar (رضي الله عنه) yace: To ta yaya za a kubuta daga gare ta, ya Manzon Allah? Sai yace: Ka rika cewa: Ya Allah ina neman ka tsare ni kan yin shirka a gare ka alhalin ina sane, Ina kuma neman gafararka daga zunubin da ban sani ba", Ibnu-Hibbana ya ruwaito shi, daga hadisin Abubakar, Da kuma Ahmad, daga hadisin Abu Musa.
An ruwaito daga Abu-hurairah (رضي الله عنه), daga Annabi (صلى الله عليه وسلم) lallai shi ya kasance yana yin addu'a:
"Ya Allah! Ka gafarta min zunubaina dukkansu; kananansu da manyansu, na kuskurensu dana gangancinsu, na sirrinsu dana bayyanansu, na farkonsu da na karshensu", Muslim ya ruwaito shi, da Abu-dawud.
            Idan bawa ya rokiUbangijinSa gafarar zunubansa; wadanda ya sani daga cikinsu da wadanda bai sani ba, to lallai an datar da shi; dace mai girma.

            Kuma bawa ya roki Ubangijinsa gafarar zunubai cikin ikhlasi da naci da roko mai tattare da kankan-da kai yana kunsan TUBA DAGA ZUNUBAN, Shi kuma ROKON A DATAR DA MUTUM ZUWA GA TUBAN yana kunsan NEMAN GAFARAR; saboda haka, kowanne daga cikin ISTIGFAAR da TUBA idan aka ambace shi ba tare da dayanba to yana kunsan ma'anan dayan.  Idan kuma ambatonsu ya hadu a cikin nassoshin Kur'ani ko hadisi to Ma'anan: ISTIGFAARI sai ya zama: Neman shafe zunubi da gusar da alamarsa ko gurbin da ya bari, tare da bada kariya kan sharrin da ya gabata na zunubin, da kuma suturce shi. Ita kuma TUBA sai ma'ananta ya zama: Komawa zuwa ga Allah; ta hanyar barin aikata zunubai, da kuma kare bawa daga abinda ya ke tsoro; na munanan aiyukansa a rayuwar da yake fiskanta, tare da yin azama ko niyyar ba zai sake aikata zunubin ba.
Kuma lallai AyarAllah ta ambaci ISTIGFAARI da TUBA a hade, a inda Allah yake cewa:
"Kuma ku nemi gafarar Ubangijinku, sa'annan ku tuba zuwa gare shi, zai jiyar da ku dadi jiyarwa mai kyau, zuwa ga wani lokaci ambatacce, kuma ya baiwa dukkan ma'abocin girma girmansa, Idan kuma kuka juya to lallai ni ina tsoron azabar yini mai girma akanku" [Hud: 3].
Da wassu ayoyin wadanda ba wannan ba.
Kuma lallai Annabi (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Ya ku mutane! Ku tuba zuwa ga Ubangijinku, kuma ku nemi gafararSa; saboda Ni na kan tuba zuwa gare shi, ina kuma neman gafararSa; a kowani yini sau dari", Annasa'iy ne ya ruwaito shi, daga hadisin Al'agarri Almuzaniy (رضي الله عنه).

            Kuma lallai bawa yana da matsananciyar bukatar YIN ISTIGFAARI, a ko-da-yaushe,      musamman kuma a wannan zamanin saboda yawaitan ZUNUBAI da FITINTINU,    wannan kuma domin Allah ya datar da shi a rayuwarsa, da kuma bayan mutuwarsa, ya kuma gyara masa sha'aninsa.    Saboda yin istigfaari ya kan bude kofofin alherori,   ya kuma tunkude sharrori da ukubobi.
            Kuma lallai itama al'ummar musulmai tana da matsananciyar bukata zuwa ga dawwama kan neman gafara; domin Allah ya yaye mata ukubobi da suka sauka a gare ta, ya kuma tunkude mata ukobobin da za su sake sauka a gare ta.
            Kuma babu wanda zai yi sakaci KAN NEMAN GAFARA sai wanda ya jahilci amfanoninsa da albarkokinsa,     saboda falolinsa sun zo dayawa a cikin ALKUR'ANI da SUNNAH; Allah (تعالى) yana cewa dangane da annabi Salihu (عليه السلام):
"Ya ku mutanena! Don me kuke gaggawan aikata mummuna gabanin kyakkyawa, Da dai kun nemi gafarar Allah; da tsammanin za a yi rahama a gare ku" [Naml: 46].   Saboda da yin istigfaari ne ake yin rahama ga al'ummah.
Kuma Allah (تعالى) yana fada dangane da annabi Nuhu (عليه السلام):
"Sai nace: KU NEMI GAFARAR UBANGIJINKU lallai shi ya kasance mai yawan gafara   *    Zai saki ruwan sama akanku; mamako   *     kuma ya karfafe ku da wata dukiya, da 'ya'ya, kuma ya sanya muku gonakai, kuma ya sanya muku koguna" [Nuh:10-12].
Kuma Allah (تعالى) yake fadi dangane da annabi Hudu (عليه السلام):
"Kuma, ya mutanena! Ku nemi gafarar Ubangijinku, sa'annan ku tuba zuwa gare shi; sai ya saki ruwan sama akanku, ya kuma kara muku wani karfi akan karfinku, Kuma kada ku juya baya kuna masu laifi" [Hudu: 52].
Allah (تعالى) yace:
"Allah bai kasance zai azabta su ba alhalin kana cikinsu, kuma Allah bai kasance mai azabta su ba; matukar suna neman gafara" [Anfaal: 33].
Abu-Musa yake cewa (رضي الله عنه):
((Lallai wannan al'ummah a cikinku akwai abubuwan samun aminci guda biyu;   Amma dangane da wannan annabin –صلى الله عليه وسلم- to shi kam ya shude, Yayin da shi kuma NEMAN GAFARA zai ci gaba da wanzuwa a cikinku har zuwa tashin kiyama)).
            Don haka; Wannan al'ummar; Idan ta yawaita istigfaari = zai dauke mata musibun da suka sauka ko suka auku, sannan ya tunkude mata wadanda za su sauka a gaba;     saboda bala'i baya sauka sai idan an yi ZUNUBI,  kuma ba a yaye shi sai da yin TUBA da ISTIGFAARI,     An ruwaito daga Abdullahi dan Abbas (رضي الله عنهما) yace: Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Duk wanda ya lazimci yin istigfaari Allah zai sanya masa mafita daga kowani kunci, da kuma yayewa daga kowani bakin ciki, ya kuma azurta shi ta yadda baya tsammani", Abu-dawud ya ruwaito shi.

            Kuma lallai KALMOMI DA AKA KIYAYE SU MASU ALBARKA na ISTIGFAARI sun zo daga Annabi (صلى الله عليه وسلم),     kuma lallai cikin fadin wadannan kalmomin akwai lada mai yawa;
            Yana daga cikinsu:
            Fadinsa (صلى الله عليه وسلم):
"Duk wanda ya fadI: ASTAGFIRUL LAHAL ALZIY LA ILAHA ILLA HUWAL HAYYAL KAYYUMA, WA ATUBU ILAIHI, Duk wanda ya fadi haka to an gafarta zunubansa, koda kuwa ya gudu a wurin yaki". Abu-dawud da Tirmiziy suka ruwaito shi, da Hakim, kuma yace: hadisi ne ingantacce, akan sharadin Bukhariy da Muslim.
An ruwaito daga Abu-Sa'id alkhudriy, daga Annabi (صلى الله عليه وسلم), lallai yace:
"Duk wanda ya fada a lokacin da ya tafo zuwa ga shumfudinsa: ASTAGFIRUL LAHA ALLAZIY LA ILAHA ILLA HUWAL HAYYUL KAYYUMU, WA ATUBU ILAIHI, sau uku, to Allah zai gafarta zunubansa, koda sun kai kumfan teku", Tirmiziy ne ya ruwaito shi.
An ruwaito daga Ubadah dan As-samit (رضي الله عنه) yace: Annabi (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Duk wanda ya tashi daga barcinsa, a cikin dare' Sa'annan yace: LA ILAHA ILLAL LAHU, WAHDAHU LA SHARIKA LAHU, LAHUL MULKU WA LAHUL HAMDU, WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN KADIR, SUBHANAL LAHI, WALHAMDU LILLAHI, WA ILAHA ILLAL LAHU, WALLAHU AKBAR, ALLAHUMMAG FIR LIY, Sai yayi addu'a to an amsa masa, idan kuma ya tashi yayi sallah to an karbi sallarsa", Bukhariy ne ya ruwaito shi.
Ya zo cikin wani hadisin cewa:
"Duk wanda a gabanin ketowar alfijir din juma'a yace: ASTAGFIRUL LAHAL ALZIY LA ILAHA ILLA HUWAL HAYYAL KAYYUMA, WA ATUBU ILAIHI, sau uku, an gafarta zunubansa koda sun kasance misalin kumfar teku ne".
Kuma an ruwaito daga Shaddad dau Aus (رضي الله عنه) daga Annabi (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Jagoran laffuzan neman gafara shine bawa yace: ALLAHUMMA ANTA RABBIY LA ILAHA ILLA ANTA; KHALAKTANIY, WA ANA ABDUKA, WA ANA ALA AHDIKA WA WA'ADIKA MASTADA'ATU, A'UZU BIKA MIN SHARRI MA SANA'ATU, ABU'U LAKA BI NI'IMATIKA ALAYYA, WA ABU'U BI ZANBIY; FAGFIR LIY; FA INNAHU LA YAGFIRUZ ZUNUBA ILLA ANTA, Duk wanda ya fadi kalmomin nan cikin yini yana mai samun yakini akansu sai ya mutu a wannan yinin nasa, gabanin yayi yammaci ya shiga aljannah. Wanda kuma ya fade su cikin dare, alhalin yana da yakini akansu sai ya mutu gabanin yayi yammaci to yana cikin 'yan aljannah", Bukhariy ya ruwaito shi.
An ruwaito daga Anas (رضي الله عنه) yace: Na ji Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yana cewa: Allah (تعالى) yana cewa:
"Ya kai dan Adam! Da zunubanka za su cika sashen sama gabadaya, sannan sai ka nemi gafarata sai in gafarta maka, ba zan damu ba!", Tirmiziy ya ruwaito shi, kuma yace: hadisi ne mai kyau.

            Kamar yadda kuma ake shar'anta neman GAFARAR ALLAH  a lokacin yin wata ibada ko bayan kammala ta; wannan kuma domin ta magance abinda ya kasance a cikin ibadar na tawaya ko nakasa, tare da nisantar da mutum daga ji-da kai, ko riya;    Allah (تعالى) yana cewa:
"Sa'annan ku tafo ta wurin da mutane suke gangarowa, kuma ku nemi gafarar Allah, lallai Allah Mai gafara ne Mai rahama" [Bakarah: 199].
Kuma Allah (سبحانه) yana cewa:
"Kuma ku tsayar da sallah, kuma ku bada zakka, ku bada rance wa Allah rance mai kyau,    kuma duk abinda kuka gabatar ga kayukanku na alkhairi za ku same shi a wurin Allah, zai kasance mafifici kuma zai fi girma ga sakamako, Kuma ku roki Allah gafara; lallai Allah Mai gafara ne Mai rahama" [Muzammil: 20].
Sai Allah yayi umurnin a nemi gafararSa a lokacin da ake yin wadannan aiyukan da'an, da kuma bayan kammala su.

            Haka kuma an shar'anta musulmi ya rika neman gafara ga 'yan'uwansa muminai; maza da mata, da musulmai maza da msulmai mata, rayayyu daga cikinsu da wadanda suka mutu,    wannan kuma a matsayin kyautatawarsa ne a gare su, da bayyanar da soyayya, da lafiyar zuciya, tare da amfanar da musulmai, da kuma (tsoma baki) don neman cetonsu a wurin Allah;    Allah (تعالى) yana cewa:
"Da kuma wadanda suka zo a bayansu, suna cewa: Ya Ubangijinmu ka yi mana gafara, tare da 'yan'uwanmu da suka rigaye mu da Imani, kuma kada ka sanya wani kulli a cikin zukatanmu dangane da wadanda suka yi imani, Ya Ubangijinmu lallai kai Mai tausayi ne, Mai rahama" [Hahsri: 10].
An ruwaito daga Ubadah dan Assamit (رضي الله عنه) daga Annabi (صلى الله عليه وسلم) lallai shi yace:
"Duk wanda ya nemi gafara ga muminai maza da muminai mata to lallai Allah zai rubuta masa lada a madadin kowani mumini namiji da mumina mace", Alhaisamiy yace: Isnadin wannan hadisin yana da kyau (jayyid).
Wannan kuma kamar nema musu gafara kenan a lokacin yin sallar janaza a gare su, da kuma nema musu gafara a makabartai idan musulmi ya ziyarce su.
Hakan kuma koyi ne da Mala'ikun da suke dauke da al'arshi, da kuma sauran Mala'iku makusanta,   Allah yana cewa:
"Wadanda suke rike da al'arshi, da wadanda suke kewayensa suna yin tasbihi da gode wa Ubangijinsu, kuma suna yin imani da shi, suna kuma neman gafarar Allah ga wadanda suka yi imani (suna cewa) Ya Ubangijinmu! Lallai ka yalwaci kowani abu da rahama da kuma ilimi; sai ka yi gafara ga wadanda suka tuba, suka kuma bi hanyarka, kuma ka kare su daga azabar wutar jahim" [Gafir: 7].  
Yin haka kuma yana daga cikin manyan hakkokin muminai!

            Ya ku bayin Allah… !
            Ku amsawa umurnin Ubangijinku,    Allah yana cewa a cikin hadisin kudusiy:
"Ya ku bayina ! lallai ku, kuna yin laifi dare da rana, Ni kuma ina gafarta zunubai gabadaya; sai ku nemi gafarata; zan gafarta muku", Muslim ya ruwaito shi daga hadisin Abi-zarrin.

Sai ku fiskanci Ubangijinku da neman gafararSa, za ku ga karamcinSa da kyautarSa da falalarSa, da albarkokinSa, kuma za ku sami shafe aiyukanku munana, da daukaka darajoji,      Hadisi y azo daga Abu-hurairah (رضي الله عنه) yace: Manzon Allah (صلى الله عليه وسلم) yace:
"Na rantse da wanda raina yake hannunsa! Da ace bakwa yin zunubi to da Allah ta'alah ya tafiyar da ku, kuma da ya zo da wassu mutanen wadanda suke yin zunubi; sai suna neman gafarar Allah ta'alah sai ya gafarta musu", Muslim ya ruwaito shi.
Kuma saboda kasancewarsa Allah madaukaki Mai yalwar gafara ne, mai baiwa da kyauta da karamci, yana son a rika neman gafararSa, ana rokonSa    Allah (تعالى) yana cewa:
"Kuma duk wanda ya aikata mummunan aiki, ko ya zalunci kansa, sa'annan sai ya nemi gafarar Allah, to lallai zai sami Allah Mai yawan gafara Mai rahama" [Nisa'i: 110].


            Allah yayi mini albarka Ni da KU, cikin alkur'ani mai girma, ya kuma amfanar da mu da abinda ke cikinsa na ayoyi da tunatarwa mai hikima,      kuma ya amfanar da mu da shiriyar shugaban manzanni, da kuma maganganunsa mikakku,    Ina fadar maganata wannan, kuma ina neman gafarar Allah Mai girma Mai daraja wa Ni da Ku, da kuma sauran musulmai da muminai,     Ku nemi gafararSa; lallai shi Mai gafara ne Mai rahama.        

Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata Allah Mai gafara abin godiya, Ga Ubangiji na na da sunaye kyawawa da sifofi madaukaka, ina godewa Ubangiji na bisa ga ni'imominsa masu girma, kuma na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, kuma na shaida shugabanmu kuma Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne, zababbe, ya Allah ka yi salati da aminci ga bawanka kuma Manzonka Muhammad da iyalansa da Iyalansa da sahabbansa masu tsoron Allah, bayan haka,
Ku ji tsoron Allah Madaukaki, ta hanyar  neman yardarsa da aiki da biyayyarsa da nesatan abin da ya haramta, hakika Ubangijimu ya baku iko na aiki na kwarai ya kuma sanya wannan duniya gida ne na aiki, lahira kuma gidan sakayya, Hakika masu aiki da ikhlasi a wannan gida da kyautatawa sun rabauta, masu barna wadanda suka bijire sun yi hasara, kai kace ka ajali ya zo muku, ga buri ya juya baya, kuna da abin lura daga wadanda suka shude, kuma game da labarunsu da tarihinsu kuna da izina a ciki, na cikin  kabari dayansu na fatan ya dawo duniya don ya yi salla raka'a biyu,kuma ya nemi gafara da yawa, sai dai faufau da a amsa masa, Allah madaukakin sarki ya ce : ( Har idan mutuwa ta je wa dayansu sai yace : ya Ubangiji na ku mayar da ni (duniya)* Tsammani na in aikata aiki na kwarai cikin abin da na bari, kayya lalle ne ita kalma ce shi ne mafadinta alhali kuwa a baya gare su akwai wani shamaki har ranar da zaa tayar da su.)
Kar ka rena kadan na daga alheri ko kadan na sharri, ya zo a hadisi : (Na hore ku rena kananan zunubai, don suna taruwa ga mutum har su halka shi,
Ya zo a hadisi ( kar ku rena wani abu na aikin alheri,
Ya ku bayin Allah : Lalle Allah da Mala'iku na salti ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi.       

   

     

هناك تعليقان (2):

  1. Mimi Tamara Johnson kwa jin. Ninaishi Marekani, kati ya hii Nataka Kutum ili kuwaonya washauri Wote sana wa mkopo Kuwait Makin sababu kuna kashfa Kwa Kila Mahal. Nimeshambuliwa på wakopaji kadhaa mtandaoni. Nilikuwa nimepoteza Tumaini Kwa Hadi RAFIKI yangu alipokuwa akanipeleka wakopaji sana wa kuaminika aitwaye Collins Williams Loan Company Ambay alinipa mkopo usio wa Salama ya Chini 75.000 Dola tabel 24 Shida yoyote bold. Ikiwa en Haja Aina ya ya yoyote mkopo du wasiliana Naye sasa kupitia Barua pepe: hii Nitumia bigloan15@gmail.com kati ili kuwaonya Kwa Wote wanaotafuta mkopo sababu ya ya Jahannamu niliyopita katika mikono wakopaji bandia.Mimi vi Tamara Johnson Kwa Jina. Ninaishi Marekani, kati ya hii Nataka Kutum ili kuwaonya washauri Wote sana wa mkopo Kuwait Makin sababu kuna kashfa Kwa Kila Mahal. Nimeshambuliwa ikke wakopaji kadhaa mtandaoni. Nilikuwa nimepoteza Tumaini Kwa Hadi RAFIKI yangu alipokuwa akanipeleka wakopaji sana wa kuaminika aitwaye Collins Williams Loan Company Ambay alinipa mkopo usio wa Salama ya Chini 75.000 Dola tabel 24 Shida yoyote bold. Ikiwa en Haja Aina ya ya yoyote mkopo du wasiliana Naye sasa kupitia Barua pepe: hii Nitumia bigloan15@gmail.com kati ili kuwaonya Kwa Wote wanaotafuta mkopo sababu ya Jahannamu niliyopita katika wakopaji Mika Band.

    ردحذف
  2. Treba li vam kredit? Ovo je registrovana, garantovana i sertifikovana kreditna kompanija, odobravamo kredite pojedincima, kompanijama, ustanovama, poslovnim organizacijama i ljudima svih vrsta širom sveta. Da li vam je potreban kredit za bilo koju svrhu? Da li ste u finansijskom problemu, da li vam trebaju finansijski asistenti, firma Fred Larry je rešenje svih vaših finansijskih problema, naši krediti su laki, jeftini i brzi. Kontaktirajte nas danas za taj kredit koji vam je potreban, možemo dogovoriti bilo koji zajam koji odgovara Vašem budžetu sa samo 2% kamate. zainteresirani podnositelji zahtjeva trebaju nas kontaktirati putem e-pošte: (petercolmanloancompany@gmail.com) ili Call / Whatsapp: +2347053278874

    ردحذف