Hudubar Juma'a na
Masallacin Annabi 4/6/1438 AH Tare da
sheikh Abdurrahman Bin Abdul'Aziz Assudais
Da
sunan Allah mai rahama mai jin kai
FALALAR
MADINA DA LADUBBAN MASALLACIN ANNABI
Huduban farko
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah , muna gode maka , Ubangijina muna neman taimakonka, muna neman gafararka
muna tuba zuwa gare ka, kuma muna sake
kyautata dukkan yabo a gare ka .
To dukkan yabo ga Allah ba yankewa ga
zamanin shi* iya adadin abinda ya bada na ni'ima a halin godiya ya
gajerta .
Ina yabo gare shi bisa ga ni'imominsa masu yawa kuma ina gode
mishi bisa falalolinsa masu yawa tsarki ya tabbbata a gare shi shi ne
ma'abocin baiwa da kadartawa, wanda ya
kebanta da halittawa da zabi wanda ya fada a cikin littafinsa mafi hikima , kuma Ubangijinka yana halitta abin da yake
so kuma yake zabi Alqasas 68.
Kuma na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai
Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya mabuwayi mai yawan gafara tsarki
ya tabbata a gare shi shi ne Allah guda daya mai yawan rinjayi, na shaida
Annabin mu Muhammad bawan Allah ne kuma Manzonsa ne zababbe mafi alherin wanda yayi taku a kasar
Daba ( Madina) gidajen ansarawa gurin hijiran sahabbai zababbu, Allah ya yi
salati da aminci da albarka a gare shi da iyalansa tsarkaka, da sahabbansa masu
biyayya da tabi'ai da wanda suka bisu da kyautatawa, muddin dare da wuni na bibiyan juna.
BAYAN HAKA:
Ya ku Musulmai: Daga mimbarin masallacin mafi
alherin halittu , ina muku wasiyya da ni kai na da wasiyya mafi alheri, ku ji
tsoron Allah mabuwayi da daukaka domin shi ne matattaran dukkan alheri kuma
mabubbugan dukkan albarkatu, kuma shi ne aminci daga dukkan musibu, kuma kariya
ne daga dukkan wasu bala'I (ya ku wadanda kuka yi imani ku ji tsoron Allah
hakikanin tsoronsa kada ku mutu face
kuna musulmai)
Tsoron Allah shi ne
tushen al'amari to ka sanya *** tsoron sa tattali don gyara al'amarinka
Kuma ka gaggauta
himmatuwa zuwa ga mishi da'a ***domin fa baka sani ba yaushe ne za a tafiyar da
rayuwarka
Bayin Allah , lallai
mai lura a yanayi na wannan duniya zai
samu mafi girman dalili na kadaituwan Allah, da kuma mafi girman shaida bisa ga
rububiyyarsa da cikan hikimarsa da iliminsa da kudurarsa kasantuan shi mabuwayi
da daukaka yana zaban abinda ya so na
daga mutane da wurare yakan kuma kebance
abinda yaso na daga abubuwa da zamani sabo da wasu manufofi masu girma da wasu manyan hadafi wanda maslahohi na bayi ke dore akansu bashi da abokin tarayya tsarki ya tabbata a
gare shi yana zaba kamar irin zabinsa , kuma yana gudanarwa kamar irin
gudanarwarsa ( kuma Ubangijinka yana halitta abin da
yake so kuma yake zabi Alqasas 68).
Lallai na daga cikin
mafi bayyana na wannan zabin, zabin sa da yayi tsarki ya tabbata a gare shi na
daibataddaiba Madina garin Annabi don ta kasance garin hijira na Manzonsa tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi , ita take biye wa Makkah mafi alherin
bigire kuma mafi daukakan guri da doron kasa mai biye mata wurin alfarma da
girmamawa, da daukakawa da mutuntawa
gari mafi kima , da sanyin idon garuruwa
da adon kasashe da hasken birane lallai ita ce gari na masoyi tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi matsira na
itaciya mai yabanya daular farko na musulunci,
a cikin ta ne ka'idodin addini ya
cika a kasanta ne mai tsarki a ka
dabbaka hukunce-hukunce na musulunci da sha'anoninsa , muna karantawa a tarihinta tarihin al'umma, wacce aka haifa tare da
bullowan alfijir rananta ta haska tare
da wanzuwansa tarihinsa ya haska , sai ga shi nan tattare da shi akwai tarihi
na daula wanda ke cike da dukkan ma'anoni da siffofi masu kyau na imani da akida , da raya kasa, da ilimi, da ci
gaba, lallai ita ne Almadinatul munauwara bata gushe ba da alheru da albarkatu
da suke kewaye da ita Daiba masoyiya , kuma daba mai hankali .
Allah ya sanya ta
mafarin sakon Musulunci madauwami kuma wurin saukan wahayinsa kuma mashinfidi na da'awar Annabinsa , kuma wani kango ne na daga kangoyen shiriya , kuma
dutse ne madaukaki , kifiyoyin makiya na
faduwa a gabansa , ita ce manara na musulunci kuma makwancin imani, kuma wurin
renon akida , kuma matattaran ci gaba ,
kuma daga inda jagoranci ya tashi da jan
ragama na duniyan musulunci bisa
haske na manhajin tsakatsakiya da
daidaito nesa daga fandarewa da ketare
iyaka, da kuma ta'addanci da bangaranci da tsoratarwa , da kuma tabbatar da bin littafin Allah da
sunna kamar yanda Allah madaukakin sarki ya ce : ( ku yi riko da igiyan Allah gaba daya kar ku
rarraba ).
Daga nan ne ci gaba na musulunci
ya taso ya busa alheri , da aminci da
rahama da adalci da rangwami da salama
, ( Ba mu turo ka ba sai rahama ga talikai) bisa ga tushen tauhidi da tsarkake addini a
gare shi da tabbatar da akida ingantacciya
da lafiyayyen kuduri , da manhaja mikakkiya da kuma
samun daukaka na alamomi na addini ,
aka daga tuta na sunna da lazimtar manhaja na magabata na korai
wanda wannan kasa mai albarka ta tafi a
kai .
A Daiba akwai zane na Annabi da kuma Ma'ahad ***
mai haskakawa hakika zanen kan goge asake
shimfida shi amma ayoyin ba sa goguwa
daga gida mai alhurma***
a gare ta akwai mimbari na
shiriya wanda ya kasance yakan haura da
ayoyi bayyanannu da sauran manya-manyan wurar***da guri na shi da yake salla da
sujjada
Akwai dakna wanda
yakasance a tsakiyar su yake sauka ***
wani haske daga Allah da ake haskakawa da shi kuma a kunna
Wasu manyan alamomi
bisa tsawon zamani ba a shafe alamomin su ba *** lalacewa ya zo musu amma an asake sabunta
alamomin na su
Ya ku jama'ar musulmi :
Lallai itane Madina da ake cewa Daibatuddaiba
garin hijira kasar sunna wanda ya ziyarce ta don neman kusanci da lada da kuma kauna na wadannan guraren Allah zai saka mishi ya kuma bashi lada, ase
ba ita ce masulalan imani ba garin
hijiran shugaban dan adnan amincin Allah da salati su tabbata a a gare
shi mafi cika da kamala Buhari da Muslim sun fitar a hadisin (Abu Huraira Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce lallai imani na
sulalewa zuwa ga Madina kamar yanda macijiya ke sulalewa zuwa raminta )
Wannan gaba gare kiu
Daiba ne da gidajenta *** hakika ansa albarka wa gidajen a cikin talikai
Wannan Madina
hakika an dora mata kambu samanta wanda aka sanya mata shiriya
Ita ce masulala na
imani a zamanin da yake koka tsagewan gini na ababan mutunci
Ya ku 'yan uwa na na
imani: na daga cikin falalanta Allah ya dada
kiwata ku , lallai Allah wanda sunan shi ya daukaka yabon shi ya girmama hakika
ya kara imani akanta inada ya ce: ( da wadanda suka zaunar da
gidajen su (ga
musuiunci) kuma (suka zabi) imani , a gabanin
zuwansu suna son wanda yayi hijira suwa
gare su kuma basa tunanin wata bukata a
cikin kirazansu daga abinda aka baiwa muhajirina , kuma suna fifita wadansu
akan kawunansu kuma koda suna da wata
lalura. Wanda ya sabawa rowar ransa , to
wadannan sune masu babban rabo ) Alhashr aya na 9
Imamu Malik Allah ya
mishi rahama yana cewa: a cikin siyakin
ambaton sa na falalan madina akan
watanta na daga sassan duniya( lallai Madina ambata masauki na imani da hijira , amma watanta na daga alkaryu an bude su ne
da takuba) .
Kuma na daga cikin
falalarsa lallai Allah ya umarci Annabin
shi da hijira zuwa gare shi an karbo daga Abi Musa ya
rawaito daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ya gaci cikin bacci y a ce lallai ni zanyi
hijira daga garin makka zuwa wata
kasa wanda ke da itatuwan dabino , sai
tunani na ya tafi kan Yamama ko Hajar
ase ita ce garin Madina Yasriba ) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
'Yan uawa Musulmai:
Ya masoya shugaban halittu- Allah ya kara
haske fiskokin ku , ku saurara na daga
cikin mafi daukakan falaloli na madina :- an gina masallaci na Annabi a cikinta
, wanda an assasashi ne akan tsoron Allah,
Allah madaukakin sarki ya ce : (Kada ka tsaya a cikinsa har abada.
Lalle ne Masallaci wanda aka yi harsashinsa akan takawa tun farkon yini , shi
ne mafi cancantar ka tsaya a cikinsa. A cikinsa akwai wadansu maza suna son su
tsarkaka. Kuma Allah yana son masu neman tsarkakuwa) Tauba :108
Muslim ya fitar a
sahihinsa na daga hadisin Abu sa'id Alkhudri yace : ( Na shiga wa manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a halin yana dakin wasu shashi na
daga matayensa : sai na ce ya manzon Allah wani masallaci ne cikin masallatayya
biyu aka yi harsashinsa a kan takawa? ya ce : sai ya dauki cikin tafi
na tsakuwoyi ya buga su ga kasa, sannan
yace : wannan masallacin naku ne," ga masallacin Madina .
Na daga cikin falala na
wannan masallacin mai albarka shi ne daya daga cikin masllatayya uku da ba ya
halatta a nika gari sai zuwa gare su. An karbo da Abu Sa'id Alkudri Allah ya
kara yarda a gare shi ya ce : na ji manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : Kada ku nika gari sai zuwa ga masallatayya guda uku:
Masallacin Makka da wannan Masallacin nawa da Masallacin Aksa) Bukhari da
Muslim ne suka rawaito shi.
Na daga cikin falalarsa
kuma ana ribanya ladan sallah a cikinsa na farilla ne ko na nafila, cikin zance
mafi inganci na malamai, An karbo daga Abu Huraira Allah kara yarda agare
shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi yace : Sallah a Masallaci na ya fi sallah dubu a
wani masallaci sai dai Masallacin Makkah) Bukhari da muslim ne suka rawaito
Kuma masallaci na ya
kasance kai bai ma gushe ba abin buri ****
Zukatan da suka bata
hanya na rarrafawa zuwa gare shi.
Akwai miliyoyi da ke
kwana bisa kauna ta su wayi gari ****
Cikin tunani na da
haukan kauna ta idan sun yi tafiya.
A cikin sa akwai bigire wanda Dausayi ne daga
cikin dausayi ne Aljanna, An karbo daga Abu Huraira Allah kara yarda a gare
shi, yace : Tsakanin gida na da minbari na dausayi ne daga cikin dausayin
Aljanna. Kuma minbari na na kan tabki na,) Bukhari da muslim ne ya rawaito. Kuma a riwayar Ahmad : Minbari na wannan
na kan tabki daga cikin tabkunan Aljanna,
a riwayar Nasa'i, kuma lalle kafafun Minbari na matabbata ne a Aljanna.
Ya jama'ar musulmi hakika Allah ya sanya wannan gari mai daukaka
harami amintacce ba a zubar da jini a
cikinta ba a daukan makami don yaki,
Muslim ya fitar a cikin Sahih nasa daga hadisin sahlu dan Hanif Allah ya
kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah ya sunkuyo da hanun shi zuwa ga
Madina sai ya ce :(Ita Harami ne
amintacce)
Madina na da Alhurma
tun daga tsakanin duwatsunta biyu da konannun duwatsunta biyu da Manyan
duwatsunta da hanyoyi tsakanin duwatsun. Daga Aliyu Allah kara yarda a gare shi
yace : ( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce: Madina harami ne tun daga dutsen Air
zuwa saur) Bukhari da Muslim ne suka rawaito
Ba a koran abin
farautar ta, baa kama tsuntsunta ko abin farautar, ba a yanke kayarta, ba a
tsinke itaciyarta, ba a cire ciyayinta, ba a cire danyen itacenta ba a cire
wata bishiya deaga ita sai dai idan mutum zai yi ciyayi wa rakumin ba a tsintan
tsintuwa a cikinta sai ga mai shelantawa
ba wan da zai yi makida ga mutanen garin
Madina ko ya nufe su da mummunan abu ko
sharri face ya narke kamar yadda
gishiri ke narke wa a ruwa Manzon shiriya tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi yake cewa: ( duk wanda ya tsorata da mutanen Madina bisa
zalunci mabuwa yi da daukaka Allah zai
tsorata shi kuma tsinuwan Allah ya tabbata a gare shi da Mala'iku da mutane baki
daya , Allah ba zai karbi daga gare shi ba ranar alkiyama , aiki na farilla ko
na nafila ). Imamu Ahmad ne ya rawaito
shi
YA KU MUSULMAI:
Wanda ya bayyana a
Madina wata bidi'a ya fari wata
barna ko ya bada mafaka ga mabarnaci to ya kai kan shi ga halaka mai
tsanani, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa :
( Madina harami ne tsakanin
dutsen air zuwa dutsen saur duk wanda
ya farar da abu a cikinta na fitina ko ya bada mafaka wa mabarnaci
to to tsinuwan Allah ya tabbata a gare
shi da Mala
Ikunsa da Mutane
baki daya ba za a karba daga gare shi ba
aikin farilla ko na nafila)
Buhari da Muslim ne suka rawaito .
YA KU BAYIN ALLAH:
Na
daga cikin falalan Madina ita ce
masoyiyar masoyi masoyiyar abin
kauna tsira da amincicin Allah su tabbata a gare shi wanda ya kasace yana cewa : ( Ya Allah ka
sanya son garin Madina zuwa gare mu kamar yanda kamar yanda muke son garin
Makka ko ma sama da haka ) Buhari da
Muslim ne suka rawaito .
Ita ce gidan shi wurin hijiran shi a nan ne ya kafa mihrabinsa kuma ya daga mimbarinsa a ciki ne kuma makoncinsa yake kuma a nan ne
za atada shi .
Wurin hijiranMusdafa mai shiryarwa kuma
makwancinsa*** wanda yake abin komawa ga jarumai idan tsanani ya tsananta
Abin
komawa ga zakuna idan yaki yayi tsamari***
Gari
ne na masoyi gari ne abin kauna ga mazauna daiba wurin masauki zamewa a cikinta tare da imani daukaka ne
kuma da yalwa zamewa dan garin tare da tsoron Allah daukaka ne kuma da kaiwa
kololuwa
Ya
jin dadin wanda suka zauna a cikinta***ya walwalan mazauna cikinta *** Ya
rabautan wanda ya jibinci zama acikinta har mutuwa ta zo mishi a kasanta
An karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara mishi yarda shi da mahaifinshi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : ( duk mutumin da zai iya ya mutu a garin Madina
to ya aikata haka domin ni zan yi ceto
ga duk wanda ya mutu acikinta) Imamu Ahmad ya fito da shi.
Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan ya dawo daga
tafiya yakan dubi kangonnin Madina da
kuma manya-manyan itatuwanta da kuma
darajojinta sai ya kafe abun hawarsa sai
ya kada dabbarsa sai ya ingizata ya sata
ta kara sauri don kaunan wannan gari na
Madina idan ya fiskantota sa ya ce : ( wannan garin Daba ne sai ya ce
wannan kuma Uhudu ne dutse ne da yana son mu , muna son shi ).
Na
daga cikin falalansa cewa tsoro na Dajjal ba zai shigo mata ba ko firgici ba
zai zo gare ta ba kafansa shi Dujjal ba
zai taka zuwa gare ta ba Mala'iku suna kofofinta suna bakin garin da kofofinta da hanyoyinta
da mashiganta suna gadinta suna bada kariya a gare ta an karbo daga Abu Huraira
Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce :( A bakin kofofin Madina akwai Mala'iku
wanda annoba ba zai shige ta ba ko kuma dajjal ) Buhari da Muslim ne suka
rawaito.
Ya
ku Musulmai:
Zama a cikinta akwai albarka wanda zai sa a
dauki watanta ba komai ba a wurin yalwa na rayuwa da rafahiyya , an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(
Wani lokaci zai zowa mutane
mutum zai kira dan baffansa da makusancin shi , taho zuwa ga yalwa , taho zuwa
ga yalwa , kuma Madina ne tafi alheri a gare su da sun kasance sun sani . )
Muslim ne ya rawaito shi
Ya
ku mazauna cikin Daiba ya ishe ku ***
daga tafiya zuwa neman daukaka kusantan Ahmadu
To
duk mai neman wanin ta zuwa wani gari ko
da ta daukaka*** game da wani a bin duniya to bazai samu shiryuwa ba.
'yan uwa na imani:
Madina na da albarka a sa'in sa
da mudun ta da kilonta da dabinon
ta da kadan nata da mai yawanta Annabi ya masa addu'a ya ce: ( Ya Allah ka sanya a madina ribi biyu na abinda kasanya a Makka na
albarka) Buhari da Muslim ne suka rawaito
YA
JAMA'AR MUSULMI :
Wannan
ita ce Daba garin shugaban halittu :
Falalolinta basa kirguwa, albarkatunta basa kididdiguwa , ya zauna a tsawon tarihi a shudewan
karnoni gini ne na kololuwa ta zamana
wuri ne katangange na imani da 'yan uwantaka
da kuma makoma ne na akida kuma masdari ne na da'awa .
Allah mai girma! a Daiba akwai kamsasan abubuwa na tunawa , na dindindin akwai kuma kamsasan abubuwa na gwarzanta na
daukaka.
YA KU MUSULMAI:
Lallai bada kulawa ga Madina madaukakiya ya doru a kanmu , da kuma bada kulawa ga
girman alfarmarta ga dukkan alheri da ta kunsan
kuma hanyar yada darajar ta abu ne mai kawo ceto, falalanta gami da tattaro wurarenta na daukaka ta dace da wuraren da aka raya su da wahayi
da saukarwa Jibrilu da Mika'ilu sun yi
kai koma a cikinta mala'iku sun haura
da Mala'ika Jibrilu dan a girmama
farfajiyarta a shaki kamshin iskarta a
ribaci lokutan cikinta a kuma yawaita ayuka na kwarai a cikinta .
Ya gidan mafi alherin Manzanni da wanda ke tare da
shi*** an shiryar da mutane kuma an kebe
shi da ayoyi
Ina da tsananin kauna a gare ki da matukar
so *** da kuma shauki mai kunna garwashi.
Ya
jama'a makusanta abin misali , ya dace
ga duk wanda ya nufi kusantar Madina ya zamana yana da saukin hali da tausasawa mai kiyaye alhurmar wurin
nata tare da la'akari da mazaunanta , ya
yi tarayya da su a majalisain su ba a kalacen su ba ya yi cunkoso tare da su a lokutan su ba a
abincin su ba , ya kuma ribaci halayensu ba arzikinsu ba ya tsinkaya daga biyayyansu ba daga alkamarsu
ba , kuma ya kwadaici kaunarsu ba kwayarsu ba .
Ya tawagan maziyarta zababbu :- ga ku kuna gabatowa
zuwa garin Musdafa Al-mukhta'; na bada fasan mahaifina da mahaifiya ta a gare
shi tsira da amincin Allah su tabbata a
gafre shi – ku tuna wajabcin bin sunnarsa
da taku kan tafarkin sa, da sha a koshi daga tarihin sa Allah madaukakin
sarki ya ce : ( in kun kasance kuna
son Allah to ku bini Allah zai so ku kuma ya gafarta muku zunuban ku) Ali Imran
31
Abinda da'ansa da kaunar sa ke hukuntawa shi ne neman sanin laduban ziyarar masallacin
sa da laduban yin sallama a gare shi da abokan shi biyu- yardan Allah ya
tabbata a gare su – da kuma laduban zama a garin sa Madina na Annabi abin haskakawa , bata gushe ba tana albarkatu
na kewaye da ita a katanganta da kuma
kadaita Annabi wurin bin shi, a
halayen sa irin na Muhammad , da kuma
dabi'unsa na zababbe da kuma rashin shan gabansa ko da ga sauti a wurinsa.
Ya ku wadanda
suka yi imani kada ku daukaka
sautunttukanku bisa sautin Annabi , sama
kuma kada ku bayyana sauti
gare shi a magana kamar bayyanawar sashinku ga sashi ,
domin kada ayyukan ku su baci alhali kuwa ku baku sani ba ).
AL'UMAR MUSULMI: Lallai wajibi ne a gare mu gaba daya da mukula
da laduba game da wannan gari na Madina mai tsarki sai dai-Allah abin neman
taimako!- Shin na daga ladabi bawa ya aikata acikinta abinda zai sabawa akida
ingantacce da sunna mikakkiya , ko kuma
ya kirkiri wata bidi'a ko wani abu na sabawa?!
Ku ji tsoron
Allah Ubangijinku-ya ku musulmai- ku kyautata ladabi tare da garin shugaban
halittu ku lazamci dukkan laduba na
Musulunci a masallacin mafi alherin halittu, lallai wajibi ne a gare mu gaba
daya da mu yabi Allah mu gode mi shi bisa abinda ya bamu na ni'ima a wannan bigire mai albarka , kuma
mu kula da ladabi a cikinta da zaman lafiya da bin tsari a gidaddajenta da kuma
tsakanin maziyartanta kuma
maziyartanta su kimtsa don ziyara , kada su shagaltu da barin ibada ta
hanyar amfani da wayan tafi da gidanka ko daukan hotuna ko makamantan su su
nisanci cunkokso da cutar da 'yan uwansu, kuma mace idan ta halarci wannan
masallacin mai daraja ya da ce ta siffantu da hijabi da kame kai kuma rashin
cakudaidainiya da maza .
muna rokon Allah da ya azurta mu da ladabtuwa da laduba na musulunci kuma ya azurtamu da
binsunnan shugaban halittu da baiwansa da karamcin sa kuma ya azurta Musulmai da ladabi na kusanci
da kyautata zama a kusa da shugaban
halittu mafi girman salati da mafi
tsarkin aminci a gare shi kuma
bisa ga iyalansa da sahabbansa masu
karamci .
Ina neman tsarin
Allah daga sharrin shaidan abin jefewa
(Lallai abin
koyi mai kyau ya kasance gare ku daga manzon Allah ga wanda ya kasance yana fatan
rahamar Allah da ranar lahira kuma ya
ambaci Allah da yawa )
Allah ya sa mini albarka ni da ku a wahayi biyu kuma ya amfane ni da ku da
shiryarwan shugaban haliyttu (aljanu da mutane) ina fadi na wannan kuma ina neman gafaran
Allah da ni da ku da kuma dukkan Musulmai , ku nemi gafaransa domin shi mnai
yawan gafara ne mai jin kai.
HUDUBA TA BIYU:
Dukkan yabo sun tabbata ga Allah mai wadatarwa da
ni'ima da baiwa na shaida ba bu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai
yake ba shi da abokin tarayya ya korara
mana daga ni'imomin shi masu yawa cikin
aminci da imani, kuma ya yalwata a gare mu na daga karamcin ludufinsa, na baiwa da kyautata na shaida cewa Annabinmu Muhammadu bawan
Allah ne kuma Manzon sa ne Allah ya yi dadin tsirada aminci da albarka a gare
shi da ilansa da sahabbansa , da tabi'ai
dawanda suka bisu da kyautatawa zuwa
ranar sakayya
BAYAN HAKA:
Ku ji tsoron Allah- bayin Allah- ku gode mishi bisa
abinda yayi na baiwa a gare ku game da wadannan wurare masu tsarki da bigire madaukaka.
'Yan uwa na
musulunci ku saurara : na daga cikin falalan Allah madaukakin sarki wannan gari na Musdafa ya rabauta da karin
kulawa daga jagorori na wannan gari mai
albarka tunda a ka kafa har zuwa yau .
Mafi hasken hujjoji dake furta haka da dalilai
masu nuna hakan :
wannan fadadawa na gini na tarihi mai bankaye mai jan hankali wanda ake kidanya shi cikin
abin alfahari ga duk wani Musulmi kuma haske ne mai haskakawa a fiskan tarihi
ta yanda zai bada daman tattaro adadin
mafi girma na masu nufo wannan masallaci na Annabi da kuma masu ziyarar sa daga sassan
duniya don hidima ga masallacin Musdafa amincin Allah ya tabbata a
gare shi da neman hutu ga maziyartan
shi da masu nufo shi da basu dama don
yin ibadansu da biyayyan su cikin tsari na hidima na musamman , acikin wani yanayi wanda ke kunshe da sauki da natsuwa , hakika a maganan gaskiya ta dace a nada mata
kambu na hedkwata na har abada na wurin shakatawa da kuma wayewa na
musulunci .
Ya 'yar uwar
makka a sama ki yi haske*** ki yi
alfahari cikin dimuwa kina ma adontawa dai haskakawa Allah
ya sakawa jagororin wannan gari mai albarka- garin tauhidi da sunnu- mafi
alherin sakayya ya sakawa kadimul haramaini da alheri bisa ga wannan kokari madaidaici
wurin hidimawa harami biyu masu
daraja da masu fiskantosu, da kuma
abinda ya gabatar kuma yake gabatarwa ga musulunci da musulmai Allah ya sanya
shi a mizanin ayyukan shi na kwarai.
Wannan kenan ku yi salati da aminci-Allah ya muku
rahama- bisa ga mai shiryarwa mai albishir kuma fitila mai haskakawa kamar yanda mai tausayi gwani ya umarce ku
da sai ya ce : ( Lallai Allah da
Mala'ikunsa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a
gare shi da aminci tabbatacce )
Ya ku masu fatan ceto mafi alheri *** daga Ahmadu ku
yi salati a gare shi da aminci
Ma'aboci daukaka yayi salati a gare shi da aminci
muddin mai talbiya na talbiya ko mai
ihrami na tahalluli .
ya Allah ka yi
dadin tsira da aminci ga wannan rahama da ka bamu shi, da kuma ni' ima da ka
bamu kyautansa : Annabinmu Muhammad dan
Abdullahi , ya Allah ka yarda da kalifofinsa masu shiryarwa Abubakar da Umar da
Usman da Ali da sauran sahabbai da tabi'ai da wanda ya bi su da kyautatawa har
zuwa ranar sakayya kuma ka game rahamarka da mu tare da su ya mafi tausayin masu tausayi.
Ya Allah ka
daukaka musulunci da Musulmai, ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai , ka bada aminci ga masu umura da ziyara ka
sanya wannan gari cikin aminci da kwanciyar
hankali cikin kyauta da yalwa da
sauran garuruwan musulmai ya Allah ka bamu aminci a garuruwan mu kuma ka gyara kuma ka datar
kuma ka kiyaye jagororinmu da shuwagabanninmu, ka karfafi shugaban mu da gaskiya kuma jagoran al'amuran mu , ya
Allah ka datar da shi da mataimakan shi biyu da 'yanuwansa zuwa ga abinda akwai
daukaka na musulunci da gyaruwa na
musulmai .
Allah ka datar da dukkan jagororin musulmai don su yi
hukunci da shari'anka da bin littafinka da sunnan Annabin ka tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
Ya Allah ka sanya su rahama bisa ga bayin ka muminai.
Ya Allah ka
gyara halayen musulmai a ko ina , Ya
Allah ka gyara halayen musulmai a ko ina , Allah ka kare jinannakin su, Allah
ka kare jinannakin su ya Ubangijin talikai ya Allah ka bamu kyakkyawa anan
duniya da kuma kyakkyawa a lahira ka kre mu daga azabar wuta .
( Ya Ubangiji ka karba daga gare mu domin kai
mai ji ne masani kuma ka karbi
tubanmu don kai mai karban tuba ne kuma mai jiin kai .
karshen adu ar mu shi ne dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin
talikai tsira da amincin Allah su
tabbata ga shugabanmu Muhammadu da iyalansa
da sahabbansa baki daya.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق