الخميس، 16 مارس 2017

Ba dabara ko iko sai ga Allah( Lahaula wala kuwwata illa billah

HUDUBAR JUMA'A NA MASALLACIN ANNABI 18/6/1438 AH,  NA SHEIK HUSAINI BIN ABDUL'AZIZ  AL- ASSHAIKH
A irin wannan zamani da ke cike da fitintinu ga musibu sun yawaita,  makiya na mulkan al'umar musulmai wanda hakan ke haifar da radadi da bakinciki mai yawa kuma daban- daban, to lalle bukatuwa na tsananta zuwa ga tunatar da musulmai game da mafita na dahir daga dukkan kowane bakinciki, da sabuba na hakika da zaa kubuta daga dukkan bacin rai da wahalhalu.
Ya ku Musulmai!
 Wannan rayuwa mai kare wa cike take da musibu da gajiyarwa  (Wahala) Allah ya ce: (Hakika  Mun halitta mutum cikin wahala)
Lalle tushe mai girma na fita daga wadannan musibu a wannan rayuwa ta duniya da kuma kubuta daga damuwowinta yana kasance wa ne cikin tabbatar da tsoron Allah a boye da kuma bayyane, da komawa  gare shi da dawowa zuwa ga kusancinsa dare da wuni , da bada lokaci na gabadaya don girmarsa cikin sauki da tsanani,  Allah madaukakin sarki ya ce ( Duk wanda  ya ji tsoron Allah zai sanya masa mafita.Kuma ya azurta shi daga inda ba ya zato, kuma wanda ya dogara ga Allah to Allah ne Mai ishinsa.) Allah Mai girma da daukaka ya ce :(To wanda ya ji tsoron Allah zai sanya masa wani sauki daga al'amarinsa).
Na daga cikin naui na rusunawa da kankan da kai da mika wuya ga Allah mai girma da daukaka akwai abin da Annabi ya shiryar da wasu sahabbai kuma ya musu wasiya da shi ciki da waje fadi da aiki da hali da dabia hakika ya shiryar da Abu Musa Allah ya yarda da shi da fadinsa a gare shi:  ( kace la haula wala kuwwata illa billahi domin ita taska ce daga cikin taskokin aljannah)Bukhari da Muslim ne suka  rawaito
Abu zarri Allah ya kara yarda a gare shi yace:(masoyina tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya min wasiya kan na yawaita fadin la haula wala kuwwata illah billahi
           Lallai ita din nan wasiya ce madaukakiya     mai girma da babbar  ambato, kalmomin ta dan kadanne amma ma'anoninta na da girma, zikiri wanda harshe ke furta shi zuciya ya sakankance da shi  lallai shaanin shine babu mai taimako game da tabbatar da maslahohin duniya da lahira face Allah mabuwayi da daukaka to duk wanda Allah ya taimaka shine abin taimako wanda kuma ya tabar shine tababbe.
Zikiri ne wanda bawa zai sakankance da shi cewa bashi da dabara shi ko wanin shi na ya fita daga wani halin zuwa wani halin haka nan bai da karfi bisa ga wani sha'ani daga cikin sha'anunnukansa ko tabbatar da manufa daga cikin manufofinsa face da tsoron ALLah mai karfi madaukaki mai girma.
Zikiri ne da bawa zai bayyana hakikanin talaucinsa da kankan dakai da kai ga ubangijinsa kuma yana cikin larura da bukatuwa zuwa ga mahaliccinsa mabuwayi mai rinjayi.
Zikiri ne da yake fita daga harshen bawa zuciyan shi na kadaita tilo mai girman shaani daga gunshi ake nemo nasara da galaba da yayewa da mafita ALLah mai tsarki da daukaka yace :(Allah zai sanya sauki abayan tsanani )zikiri dashi ake samun rabauta da nasara da mafita da kubuta Allah madaukakin sarki yace : (yaku wadanda sukayi imani idan kun hadu da wata kungiyar yaki to ku tabbata kuma ku ambaci ALLah da yawa ko kuna cin nasara )
Lallai zikiri ne da ya dace da ko wani musulmi da ya furta shi da harshen magana da aiki, tun da sirri ne na tauhidi, wanda ke hukunta rusuna wa mahalicci,da tare wa gare shi da kubuta daga dabara ko karfi sai daga gare shi, Mabuwayi da daukaka.
Ibnul kayyim Allah ya yi mishi rahama yace ;( Wannan kalmar tana da tasiri na ban mamaki wurin tafiyar da abubuwa masu tsanani, da dauke wahala da shiga ga masu mulki da ake tsoro, da dauke manyan wahalhalu).
Ya ku bayin Allah:
 ku saurara ga wannan kissa mai girma wanda hujja ce mai haske bisa ga karfin tauhidi wanda ke warware bakin ciki duk yanda ya girmama, kuma ke tafiyar da wahalhalu duk yanda  ta tsananta .
Wata kissa ce da da yawa daga cikin malaman tafsiri sun ambata ta, ta zo ta fiskoki daban –dabam, mafi karancin darajanta a ce hassan , ita ce Auf dan Malik al-ashja'I yana da da wanda ake cewa Salim mushirikai sun kama shi cikin fursunonin yaki sai ya zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai ya ce da shi ya Manzon Allah : lallai abokan gaba sun kama da na ( cikin kaman mun yaki) ya kuma koka mishi talauci , sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ( Ba abin da ya wuni a wurin iyalan Muhammadu sai mudu  to ka ji tsoron Allah ka yi hakuri ka yawaita fadin lahaula wala kuwwata illa billahi0)  
 A wata ruwaya kuma  ya zo cewa ya umarce shi ne  kuma ya umarci uwan dan da haka, sai mutumin ya akaita hakan , yayin da yake cikin gidan shi, sai ga dan shi ya zo mishi a halin makiya din sun gafala daga gare shi sai yasamo rakuma ya zo da su zuwa ga baban shi, da ma baban matalauci ne  baban sai ya zo gun Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai ya ba shi labarin Auf da labarin rakuma , sai Manzon Allah ya ce da shi: (  ka aikata abin da ka so da su ka yi abinda ka saba yi da rakumar ka  da su ).
 Fadin Allah:( ( Duk wanda  ya ji tsoron Allah zai sanya masa mafita.Kuma ya azurta shi daga inda ba ya zato, kuma wanda ya dogara ga Allah to Allah ne Mai ishinsa.) Allah Mai girma da daukaka ya ce :(To wanda ya ji tsoron Allah zai sanya masa wani sauki daga al'amarinsa). Daga nanne sahabbai suka tafi akan wannan wasiyyar din cikin fadi kuma da aikatawa.
 Ibnu Abiddunya ya rawaito cewa Abu Ubaida da aka katange shi sai  Umar ya rubuta zuwa gare shi: duk abin da ya sauka zuwa ga  mutum na tsanani Allah zai yaye bayan haka,  kuma hakika tsanani daya ba zai ci galaba akan sauki biyu ba , kuma yana ce mishi : ( ku yi hakuri kuma ku yi dauriya  kuma ku yi zaman  dako, kuma ku yi takawa ko za ku ci nasara).
 Lallai ta'alluki da Allah  da dogaro gare shi da ambaton sa a harshe ,  na daga cikin abin da yake tafiyar da bakin ciki duk yanda ya tsananta makomanta zai zama yayewa ne da mafita .
Fudail ya ce : wallahi da mutum zai yanke tsammani daga halittu ka ji ba ka bukatar komai daga gare su , to da majibincin ya baka du abin da kaake so.
Na daga cikin sabuba wanda yake yaye bakin ciki ya tafiyar da bacin rai shi ne dan Adam a duk lokacin da  yayewa ya yi jinkiri har ma ya yanke tsammani daga gare shi bayan ya yawaita rokon sa da kankan da kai zuwa gare shi kuma bai ga wani alama na amsa aduwar ba a gare shi, to ya wajaba ya koma ya zargi kan shi ya sake sabon tuba ya yi tuba na gaskiya ya dukufa zuwa ga Allah yana mai tsarkake niya yana mai rusunawa majibinci  kuma ya yi ikirari da cewa yana cikin wadanda  suka cancanci jarabawa ya sauka a gare su  kuma ba ya cikin wadanda suke ahlin amsar adu'a sai dai yana fatar rahamar Ubangijin sa   kuma yana neman afuwar sa,  to anan ne fa amsar adu'arsa za ta zo da yayewar bakin cikin shi sabo da Allah madaukaki yana tare da duk wadanda zukatan su suka  rusuna zuwa gare shi don shi kamar yadda Malaman  magabata suka tabbatar.
Ya ku Musulmai!
Ku kiyaye irin wannan zikiri mai girma a kowani lokaci da yanayi,don alherin sa nau'uka ne daban daban , falalolinsa na da yawa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Ba wani mutum a doron kasa da zai ce : La'ilaha illalah Wallahu Akbar wa subhanallah wala haula wala kuwwata illa billa, face an kankare masa kusakuran shi, ko da sun fi yawan tarukucen saman teku ne.) Ahmad ya rawaito, Tirmizi ya ce Hasan ne Hakim kuma ya inganta shi kuma zahabi ya mar muwafaka.
An karbo daga Ubada dan samit Allah ya yarda da da shi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Wanda ya tashi cikin dare sai yace : La'ilaha illallahu Wahdahu la sharika lahu lahul mulku wa lahul hamdu wa huwa ala kulli shai'in kadir, Alhamdu lillahi wa subhanallahi wa lailaha illallahu wallahu Akbar wala haula wala kuwwata illa billah, sai yace ya Allah ka gafarta mini, ko ya yi adua zaa amsa masa,  kuma in ya yi alwala ya yi sallah za a karbi sallar sa) Buhari ne ya rawaito.
Lalle adua ne na alheri ga bawa kuma kariya ne da katange wa ne ga maslahohinsa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (wanda ya ce- idan ya fita daga gidan shi - Bismillah na dogara gare shi ba dabara ko karfi sai gare shi, za a ce da shi :An isanmaka an baka kariya kuma shaidan zai yi nesa da shi).Abu Dauda da Tirmizi ne suka rawaito.
Sabo da wannan zikiri ne da ke hukunta mika wuya ga Allah da maida al'amari a gare shi, da yarda da rusuna wa gare shi,tsarki ya tabbata a gare shi, kuma ba mai maida al'amarinsa, kuma bawa bai mallaki komai ba na al'amarinsa,ragamar al'amura na hanun Allah madaukaki, al'amuran bayi na jawuwa ne bisa hukuncinsa da kaddararsa, ba mai maida al'amarinsa ko bin kadun hukuncinsa.
To kai musulmi ka kasance  mai natsuwar zuciya mai kwanciyan hankali mai sakankance wa da yaye wan bakinciki da samun mafita, duk abin da ke duniya na karkashin iko ne na Allah.
Duk abin da ke wannan duniya ko yaya karfinsa ya kai, ko tsananin ya kai to hakika tana karkashin karfin Allah ne da umarninsa, da hukuncinsa da kaddararsa, to duk wani mai karfi mai rauni ne a gun Allah mai girma da daukaka,ya kai bawan Allah ka shagaltar da kanka da sauran ayyukan da'a da nau'uka na alheri, ka lazimci ambatonsa da nau'uka na zikiri daban daban a yanayi na sauki da cuta ko tsanani da yelwa. Na daga cikin abin da ya inganta daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa:(Duk wanda yake son Allah ya amsa mishi adu'a yayin tsanani da bakin ciki to ya yawaita adu'a lokacin yalwa ).
 Aikata aiki na alheri mai yawa   da falala mai girma, duniya ba za ta yi dadi ba sai da ambaton Allah , lahira kuma ba za ta yi dadi ba sai da afuwar sa, aljanna kuma ba za ta yi dadi ba sai da ganinsa,  ka kasance mai yawan ambaton lahaula wala kuwwata illa billahi don tana taimakawa wajen dauke abubuwa masu nauyi kuma tana  tunkude abubuwa na ban tsoro da tsanani, da ita ake samun daukaka a dukkan  yanayi  Allah ne wanda ake neman taimako a gare shi , kuma a gare shi ake dogaro, babu dabara ko karfi sai ga Allah mai girma .

  HUDUBA NA BIYU :
 Ya ku Musulmai
 mumini mai kadaita  Allah  mai kiyaye dokokin Allah , mai lazimtar biyayyar sa da kuma biyayyar Manzonsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi Allah na tare da shi  da kiyayewar sa na musamman Allah madaukakin sarki ya ce :(  Allah yana tare da wadanda suka yi takawa  da kuma wadanda suke su masu kyautatawa ne  ).
Wanda Allah ya kasance tare da shi to lallai yana tare da bangaren da ba a yin galaba akansu,  kuma da mai kiyayewanda   ba ya yin bacci da mai shiryarwan da ba ya bacewa , kamar yanda katada ya ce: (  lallai ita mai taimakawa ne tana hukunta samun nasara da karfafa da kiyayewa da taimako da  fita daga zaure na bakin ciki da wahalhalu masu tsanani.
 Duk wanda ya kiyaye Allah ya kuma kiyaye hakkokin sa  zai same shi gaba gare shi  a duk halin da yake ciki  wanda ya nemi sanin Allah a lokacin yalwa to Allah zai kawo mi shi dauki a yayin tsanani,  sai ya tsiratar da shi a yayin tsanani ya kubutar da shi daga musibu,  wanda ya yi mu'amala da Allah  da takawa da biyayya   , cikin yardan sa to Allah zai masa mu'amala da tausasa wa  da taimaka wa  a yayin fadawarsa cikin  tsanani,   ya zo a Hadisil kudusi : (Bawa na ba zai gushe ba  yana kusanta na da nafilfilu har na so shi  idan na so shi sai  na kasance  jin sa da ya ke ji da shi,  da kuma ganin sa da yake gani da shi da hanunsa da yake damka da shi ,  da kafarsa da yake tafiya da itakuma  idan ya roke ni zan ba shi , kuma idan ya nemi tsari na zan bashi)  Buhari ne ya rawaito.
Sannan ku sani mafi tsarkin abin da rayuwarmu za ta mike  da shi shagaltuwa da salati da aminci ga Annabi mai girma,  ya Allah  ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga bawanka  kuma manzon ka Annabinmu Muhammad ,  ya Allah ka yarda da Al-kulafa'ur rashidun
Abubakar daUmar da Usman da Aliyu ya Allah ka  gyara halayenmu da halayen musulmai, ya Allah ka yaye bakin ciki  ka gusar da bacin rai , ya Allah ka tsiratar da bayin ka musulmai daga dukkan wata jarabawa da fitina , ya Allah ka yi maganin makiya musulmai domin su ba za su gagare ka ba   ya mai girma , ya Allah   ka kiyaye 'yan uwan mu musulmai a ko ina ya Allah ka kasan ce mai taimakon su da ba su nasara  ya  mabuwayi ya mai karfi,  ya Allah ka datar da kadimul haramaini  ash-sharifaini  cikin abin da ka ke so kuma ka yarda da shi ya Allah ka taimaki addini da shi ka daukaka kalmar musulmai da shi,  ya Allah ka gafartawa musulmai maza da musulmai mata rayayyu daga cikin su da matattu ya Allah ka bamu kyakkyawa anan duniya da kyakkyawa a lahira  kuma ka kare mu daga azabar wuta .  
         




ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق