HUDUBAR JUMA'A A
MASALLACIN ANNABI 13/05/1438AH, NA
SHAIKH SALAH BIN MUHAMMAD AL-BUDAIR.
HUDUBAR FARKO:
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah, wanda falalolinsa sun game a wurin yalwa, ni'imominsa
kuma sun kasu iri iri a rabe ko a tare, Na shaida ba abin bauta wa da gaskiya
sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, wanda ya ce :Duk wanda ya
kusanc ni da kwatankwacin taki to zan kusance shi da zira'I, na shaida
Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne, falalarsa na da yawa tamkar girgije,kimarsa ya fi karan
hanci,kyawawan halayensa ya fi cikakken wata
haske, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da iyalansa da
sahabbansa da suke tsinkaya daga haskensa, da kuma bin sawunsa, salati na har
abada mudin sama na haskakuwa da wata kasa na kawatuwa da ruwa.
Bayan haka , Ya ku
Musulmai:
Ku ji tsoron Allah don shine abu mafi daraja da zaka samu,
biyayya gare shi ke kai wa kololuwa. (Ya ku wadanda suka bada gaskiya ku ji
tsoron Allah hakkin tsoronsa kar ku mutu face kuna musulmai) Al-Imran 102
Ya ku musulmai :
Hakkoki tsakanin
ma'aurata biyu ya ta'allaka ne da Kulla aure, wanda kuma ke lazimta kyakkyawar
muamala da juna, kada daya ya jinkirta bawa daya hakkin shi, ko ya ki bada abin da ke kan shi. Kyautata muamalarsa
ga abokin zamansa da tausaya masa da juriya bisa ga cutarwarsa sabo da fadin
Allah (su matayen suna da hakki akan maza irin wanda mazan suke da shi
akansu, da abin sani.)
Ita kyakkyawar mu'amala
da kyakkyawan zama ta fi kawo sanyin ido, da kwanciyan hankali da daddadan
rayuwa, Allah madaukakin sarki ya ce :- ( ku yi mu'amala da su da kyakkyawa)
ma'ana ku yi cakudedeniya da abota
da su, da bishara da kuma sakin fiska , da bada hakkoki da aka farlanta, kamar
na daga sadaki da ciyarwa da raba kwana, da barin cutar da ita da kakkausar
magana , da bijire mata, da karkata zuwa
ga watanta, da rashin hada mata fiska,
da turmuke mata ba tare da wani laifi ba , sa'annan Allah na ladabtar da
bayinsa da fadin sa ( sa'annan kuma
idan kun ki su , to, akwai tsammanin ku ki wani abu, alhali kuwa Allah ya sanya wani alheri a cikinsa mai
yawa) a cikin ayan akwai kwadaitarwa
bisa rike su da kyautata zamantakewa da su, ko da mazajen sun tsani wani abu
daga cikin halayen su, domin rai ya ki abu ba ya nuni da kore alheri ga wannan abu,
ta iya yuwuwa abinda rai ya ki ya zama
shi ya fi amfani a addini, kuma ya fi zamewa abin godiya a karshe , sau da yawa
abin ki kan komawa abin yabo, kuma abin yabo kan koma wa abin zargi, Hakika miji kan tsani mata sabo da wata sifa daga cikin sifofinta, amma
kuma a rike ta din akwai wani alheri da yawa da bai sani ba, kuma ba zai gane hakan ba, Abdullahi dan
Abbas Allah ya yarda da shi da mahaifin
shi ya ce: "Ta iya yiwuwa Allah zai
azurta shi da Da daga gare ta , sai Allah ya sanya alheri mai yawa acikinsa."
Ya ku musulmai:
Lallai mutum yana da
wahala ya samu wanda ya ke kauna wanda
bai da wani abu da ya ki tare da shi ,
to yayi hakuri da abin da ya ki sabo da abin da ya ke so, yana da wahala ka samu mutane biyu suna mu'amala ko wannensu ya yarda da dukkan
dabi'un junansu, ba wasu mutane biyu da za su yi mu'amala da junan su fa ce daya na kawaici ga dan
uwansa, An karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- ( Kada mumini ya tsani mumina, idan ya ki
wani hali na ta to zai so wani hali nata ) Muslim ne ya rawaito .
Wato kada mutum ya ki matar sa ki na gaba daya wanda
zai sanya shi ya rabu da ita ya sake ta ya warware kullin aure, to idan ya
tsani wani hali nata mara kyau to kuwa zai samu wani hali nata abin yarda.
To ya ku mazaje :
ku riki matayenku kar ku yi gaggawan kosawa
ko fada, kar ku yi gaggawan rabuwa kada
ku yi gaggawa zuwa ga shika , kar ku kambama abu wurin nuna tsana da
kiyayya sau da yawa rauni na
hankali yakan yi galaba a kan mutum, fushi ya rinjaye shi sai ya yi aiki na wauta da shirme ya yi gaggawa
ya yi shika sannan daga baya kuma ya dawo yana nadama a halin kuma wato
komai ya tsere mishi ya wuyata ta koma gare shi.
Ya ke mata mumina:
kar ki zama cikin masu ci don tarawa, kuma ki
zama kina yawaita zargi, mai yawan hayaniya da saurin fushi, wacce bata bin
umarnin mijinta , kuma in ya yi rantsuwa bata biye mishi , ki kyautatawa mijinki , ki kasance kusa da
kaunarsa, mai taimaka masa yayin bukatarsa
mai amsa kiransa, mai sauka zuwa
ga bukatarsa mai ambaton falalarsa da
kyautatawarsa, kar ki zama mai munana mishi mu'amala , kar ki yi musu da shi yayin fushin sa da
fusatan shi, kar ki tsawwala mishi yayin da ya cije ko ya harzuka .
Mu'awiya Allah ya kara mishi yarda ya ce da Akil
dan Abu talib : " A cikin mata wacce tafi soyuwa a gareka ? sai ya ce :-
mai biyewa abin da mu ke so, sai yace
" To waccece kuma ka fi ki acikinsu ?sai ya ce :" wacce tafi nesa da
abin da kake so ", sai Mu'awiya ya ce :- wannan suka na duniya kenan, sai ya ce:-Da ma'auni na
adalci .
An karbo daga abu Uzaina Assadafi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce:- (Mafi alherin matanku sune, masu tsananin kauna masu yawan haihuwa , mai aikta (abin da ka ke so) mai share ma hawaye, muddin suka ji tsoron
Allah , mafi sharrin matayen ku kuma sune masu bayyana tsiraici , masu alfahari
sune munafukai, ba wanda zai shiga aljanna a cikin su, face kamar farin
hankaka.) Baihaki ne ya fito da shi,
Farin hankaka wato mai farin fiffike da
kafafuwa: yana nufin karancin masu shiga aljanna a cikinsu, don samun wannan
sifa na da wahala a cikin hankaki.
An karbo daga Husain dan Mihsan daga wata gogon shi cewa ta shiga wurin Manzon Allah sai
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
agare shi , sai ya biya mata
bukatar tata , sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce mata ( ko ke kina da miji ? sai
ta ce e, sai ya ce
yaya kike a gun shi? sai ta ce bana gajartawa ( a hakkinsa) sai abinda
ya gagareni, sai Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- to, ki duba matsayinki a gunshi domin shi ne
aljannan ki kuma wutanki) . Nasa'I
ne ya rawaito shi
Idan rayuwa ta kasance
ana rayata cike da kyawawan halaye ba kiyayya ba gaba, to ya
haramta akan mace ta nemi shika , ko kuma ta nemi kul'i, a daya daga cikin
zantuka mafi inganci a maganganun malamai,
An karbo daga saubana
Allah ya kara mishi yarda ya ce:- Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gareshi ya ce ( Dukkan matan da ta tambayi mijinta saki ba
tare da wani laifi ba to, kamshin aljanna ya haramta a gare ta ) Abu Dauda
da Tirmizi ne suka rawaito.
An karbo daga Ukubata
dan Amir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :-( Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- lallai mataye wadanda suke neman fansa, da masu neman warware auren su sune munafukai ) Dabarani
ne ya rawaito shi Ibnu kudama ya ce :-
wannan yana nuni cewa haramun ne yin
khul'I ba tare da bukata ba sabo da akwai cutarwa ga ita da kuma mijin nata
, da kuma gusar da maslahohin aure ba tare da bukata
ba, sabo da haka ya haramta.
Mustahabbi ne a sulhunta tsakanin ma'aurata biyu wadanda suke rikici da junansu
An karbo daga Abdullahi
dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su shi da mahaifinsa cewa mijin
barira ya kasance bawa ana ce da shi
Mugisu, kai ka ce ina kallo zuwa
gare shi yana shawagi a bayanta yana
kuka hawaye na zuba a gemun sa,
sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ga Abbas :- ( Ya
Abbas baka mamaki irin kaunar da mugisu yake yi wa barira da kuma irin kin da
barira take yiwa shi Mugisu? sai ya ce
da ita da kin koma mishi, sai ta ce ya Manzon Allah umarni ne ka ke min? sai ya ce: a'a sai dai kawai ina nema mishi alfarma ne, sai
ta ce bani da bukata zuwa gare shi ).Buhari ne ya fito da shi.
Ibnu Hajar –Allah ya
rahimce shi - yace : " wannan Yana nuni cewa idan mace ta ki miji bai
kasance wa ga waliyinta da ya tilasta mata kan zama da shi. Idan ta so shi kuma
bai kasance wa ga waliyinta da ya raba su,
Allah ya amfanar da mu da Alkur'ani da sunna
da abin da ke cikin su na daga ayoyi da shiriya bayyanannu da wazi da hikima.
Ina neman gafaran Allah
ku nemi gafararsar sa, Ubangiji na Makusanci ne Mai amsawa.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah Mai shiryar da wanda ya nemi shiriyarsa, Mai bada kariya
ga wanda ya nemi kariyarsa, Mai isarwa ga wanda ya kirdadi yardarsa, na shaida
ba abin bauta wa da gaskiya sai Allah ba wanda ya cancanci a bauta wa da gaskiya
koma bayan shi, Kuma na shaida Annabinmu
kuma shugabanmu Muhammad bawansa
ne kuma manzonsa ne, Allah ya yi dadin tsira a gare shi da iyalansa da
sahabbansa da wanda ya bi sunnarsa ya
nemi shiriya da shiryarwarsa.
Bayan haka Ya ku
Musulmai !
Allah ya sanya shika da
warware igiyar da aka kulla tsakanin ma'aurata biyu a hanun miji, sai dai ya haramta ya munana amfani da hakkin nasa
cikin sakin da rikon sa wata hanya don ribatar ita matar da firgita ta, ya
sanya shi kamar wata bulala ce a fiskar ta don ya bautar da ita da tsorata ta,
da walakanta ta, Allah madaukakin sarki ya ce : ( To ku rike su da
kyautata wa ko ku sake su da kyautata wa.) An karbo daga ASSUDI kan fadinsa (ko a sake su da kyautata wa) " Da ya
bata cikakken hakkinta kada ya cutar da ita, ko ya zage ta, "
Wanda ya katange
matarsa bai sake ba bai kuma barta ta yi aure ba idan iddarta ya kare, ya cutar
da ita da duka, da kuntata mata, ko ya hana ta hakkokinta na daga ciyarwa da
kason kwana, da makamancinsu don ta fanshi kanta daga gare shi, sai ta yi, to
khulin ya baci kuma zaa maida mata abin da ta bada don fansan.
Allah madaukaki ya ce: ( Kuma kada
ku hana su aure domin ku tafi da sashen
abin da kuka basu ).
Idan ta zo da alfahasha
sai ya hana ta aure don ta fanshi kanta daga gare shi sai ta yi hakan to
khul'in ya inganta. Sabo da fadin Allah Madaukaki: (kuma kada ku hana su
aure domin ku tafi da sashin abin da ku ka ba su, face idan suka zo da wata
alfahasha bayyananniya.)
Ba ya dace wa rike
wacce ba ta kamun kai, sabo da tawaya ne ga mijin a addinin shi da dabiunsa da
bata sunansa da zubar da mutuncinsa, bai da amincin kada ta bata mishi
shimfidinsa da jingina mishi wani da da ba nashi ba, kuma mace mai sakaci da
hakkokin Allah na wajibi kamar sallah da makamancinta, wacce ba ta jin nasiha Mustahabbi ne a sake ta.
Ya ku Musulmai :
Daga cikin mazaje akwai
wanda ya sanya furta shika da yawaita
shi abin ambato a bakinsa kuma abin sabon shi da al'adan shi,da abu mafi soyuwa
a gare shi a abu mai kima da mara kima da babba da karami da mai girma da abin
da bai taka kara ya karya ba.
Na daga cikin al'adu
mara kyau akwai rantsuwar shika
kamar yace : In kiyi
magana da wane to mata ta ta saku,ko saku ya tabbata a gare ni idan na ci
abincin wane. Ko shika ya tabbata a gare
ni muddin kika yi tafiya da wane, ko
shika ta tabbata a gare ni muddin mata ta ta shiga gidan wane, ko yace wa bako:
Shika ta tabbata a gare ni muddin baka ci abinci a gu na ba, wannan dare , ko
kuma in gobe baka ci abincin dare a guna ba, amma ba shikan yake nufi ba, ko
rabuwa ba, sai dai ya yi hakan ne kamar rantsuwa, don yana nufin kwadaitarwa ko
hanawa,ko tilastawa.
Wadannan lafuza ne
haramtattu da ayyuka ne na laifi, da walakanta rayuwan zamantakewa da rena hakkokin
mace da yara da wasa da shika da hukunce
– hukuncenta.
Ya wajaba ga miji ya
kiyaye harshensa daga yawaita furucin shika, da tsoratarwa da ita da jirwaye da
kamar ruwa game da aukar da ita.
Ibnul Arabi yace a
cikin Ahkamul Kur'an : (Na daga cikin rikan ayoyin Allah da izgilanci
abin da aka rawaito daga Abdullahi dan Abbas kan cewa an tambaye shi game da
mutumin da yace da matarsa : Ke sakakkiya ce sau dari, sai yace : Ukun ya isan
maka a gare ta, sauran casa'in da bakwai ka riki ayoyin Allah da su bisa izgili
).
Ku ji tsoron Allah ya
ku Musulmai kada ku riki ayoyin Allah abin izgili kar ku ketare iyakokin Allah
madaukaki,(Duk wanda ke ketare dokokin Allah to ya zalunci kansa) ,(
kuma duk wanda ke katare dokokin Allah to wannan yana cikin azzalumai.)
Ku yi salati da sallama
ga Ahmad Alhadi mai ceton talikai gaba daya to duk wanda yayi salati guda agare
shi Allah zai mishi salati goma.
Ya Allah ka yi salati
da aminci ga bawanka kuma manzon ka Muhammad da kuma dukkan Iyalai da sahabbai
ka yarda da mu tare da su da baiwanka da karamcinka ya Mai karamci Ya Mai yawan
kyauta.
Ya Allah ka daukaka
musulunci da musulmai,ka kaskantar da shirka da mushrikai,ka ruguza makiya
addini, ka sanya wannan gari cikin aminci da natsuwa, da wadata da yalwa da
sauran kasashen musulmai.
Ya Allah ka datar da
jagoranmu shugabanmu cikin abin da ka ke so kuma ka yarda da shi, ka riki
makwarkwadan shi zuwa ga biyayya da takawa, ka datar da dukkan jagororin
musulmai cikin yin hukunci da shariarka,
da bin sunnar Annabinka Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Ya Allah ka sanya
arzikinmu cikin yelwa, kar ka sa wani ya mana dariyan keta, kar ka bawa wani
azzalumi karfi akanmu.
Ya Allah ka warkar da
marasa lafiyanmu, ka bada waraka ga wanda aka jarabta a cikinmu, ka jikan
matattunmu, ka kwance kamammunmu, ka taimake mu a kan wanda ya yi gaba da mu,
ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka dayyaba mu
don haduwa da kai, ya Allah ka dayyaba mu don haduwa da kai, ka azurta mu da
yarda da hukuncinka,ka sa mu wadatu da kyautarka, ka sa mu wadatu da halal naka
akan haram naka.mu wadatu da falalarka akan waninka.
Ya mai girman afuwa, ya
mai girman afuwa, ya mai yalwan gafara ya mai yalwan gafara, ya makusancin rahama, ka gafarta mana baki daya, ka gafarta
mana baki daya, ka sa mu walwala da takawarka, ka sanya mu ji tsoronka kamar
muna ganinka.
Ya Allah ka bamu ruwa,
ya Allah ka bamu ruwa, ya Allah ka bamu ruwa, ya Allah ka saukar mana da ruwa kar ka sanya mu cikin masu yanke
kauna.ya Allah ka sanya aduar mu karbabbiya ce, kiran mu daukakakkiya ce.
Karshen aduarmu shi ne dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah
Ubangijin talikai.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق