الجمعة، 14 أبريل 2017

LURA DA DAUKAN IZINA

HUDUBAR JUMA'A NA  MASALLACIN ANNABI NA SHEIKH ALIYU ABDURRAHMAN ALHUZAIFI  17 RAJAB 1438 AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Masanin gaibi, mai juya zukata, Mai yawan gafarar zunubai, ina yabon Ubangijina da godiya a gare shi bisa ni'imominsa da ba mai iya kididdige su sai shi, Na shaida ba abin bauta wa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, mulki da kyakyawan yabo na shi ne, kuma shi ne mai iko ga dukkan komai,
Na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne, kuma Manzonsa ne, Mai albishir kuma Mai gargadi, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma Manzonka  Muhammad da iyalansa da sahabbansa  wadanda Allah ya jibince su, to madallah da majibinci kuma madalla da mai taimako,
Bayan haka ku ji tsoron Allah Mai tsarki, a sirracenku da a bayyanenku, don ya jibinci al'amuranku ya kuma gyara halayenku, domin takawa hanya ce ta mutanen kwarai da masu rabauta, rashin takawa shi ne  bayyanannen hasara, ya ku bayin Allah ku kasance daga cikin ma'abota lura da imani, ku bi tafarkin masu hankula da kyautatawa, ma'abuta lura su ne masu lafiyayyen hankali mikakke, kuma  masu lafiyayyen fidira, kuma suke amfana da wahayi,  suna fahimtar ma'anonin abin da Allah ya saukar bisa manufar Allah da Manzonsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, suna aiki da maganar Allah don  fatan ladarsa da tsoron ukubarsa, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma wadanda suka nisanci shaidanu ga bauta musu, kuma suka maida al'amari ga Allah, suna da bushara ,to, ka bayar da bushara ga bayi na . wadanda ke sauraron magana sa'annan su bi mafi kyaunta . wadancan sune Allah ya shiryar da su  , kuma wadancan su ne masu hankali)
Lura  na daga ayukan masu hankali   mai haskakawa      kuma yana daga cikin ayyukan masu basira masu gogewa  lura yana shiryarwa zuwa ga rabauta da tsira daga ayuka masu halakarwa, kuma yana datar da ma'abocin shi zuwa ga ayuka na kworai , kuma ya shiryar da shi zuwa ga hanyar mutanen kirki masu  neman  kawo gyara  kuma karshen shi yana zamewa zuwa ga alheri , wanda ya rasa lura  tunatarwa bazai mishi amfani ba  zai fada cikin halaka kuma zai bi sha'awe-sha'awen rayuka, kuma ya bi ta hanyar mabarnata sai ya zame cikin masu nadama ,  lura shi ne kaura daga wani hali da ya shude  ma'abocin ukuba da azaba  zuwa ga kyakkyawan yanayi ta hanyar nisantar sabuban ukuba da azaba  ko kuma kaura daga tarihin mutanen kworai  da abinda Allah ya karrama su da shi , zuwa da aiki da ayukan su da bin sawun su , ko kuma tunani cikin abin halittu da sanin tsirrin da suka kunsa da sifofin su da hikimar samar da su don bautawa mahaliccin su  da kebance shi da tauhidi da biyayya  albarka da daukaka ya tabbata agare shi  .
Hakika Allah mabuwayi da daukaka ya halicci halittu  kuma ya sanyawa duniya hanyoyin da suke tafiya a kai sai ya sanya da'a sababi ne na dukkan alheri a duniya  da lahira  ya sanya sabo sababi ne na dukkan sharri a duniya da lahira  shin akwai wanda ya taba zama shakiyyi sabo da biyayya ga Allah?  Ko kuma akwai wanda ya rabauta  sabo da sabawa Allah? Hakika Allah mai tsarki ya bamu kissa a littafinsa haka ma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bamu kissoshi  da wasu halaye  na Annabawa da Manzanni da muminai wanda a cikin shi akwai abin lura  da kuma abu na koyi ga wanda ke bayan su , da abinda akwai tsira daga ukubobi a cikin shi  da kuma rabauta da alheri  ,  da abinda akwai kyakkyawan karshe tare da shi da daga darajoji  Allah madaukakin sarki ya ce: (Lallai ne hakika abin kula ya kasance ne acikin kissoshin su  , ga masu hankali. Bai kasance kirkirarren labari ba, kuma amma shi gaskatawa ne ga abin da yake a gaba gare shi, da rarrabewar dukkan abubuwa , da shiriya da rahama ga mutane wadanda suka yi imani)  Allah madaukakin sarki ya ce  :( Sa'annan kuma muna kubutar da manzanninmu da wadanda suka yi imani  , kamar wannanne, tabbatacce ne a gare mu mu kubutar da masu imani )  Allah mai tsarki ya ce game da masu karyatawa :( Kuma suka kulla makirci, kuma muka kulla sakamakon makirci alhali su ba su sani ba . ka duba yadda akibar makircin su ta kasance  lallai mu mun darkake su da mutanen su gaba daya  . wadancan gidajen su ne wofintattu sabo da zalunci da suka yi   lallai ne a wancan akwai aya ga mutane da  suke sani).Muka  tsirar  da wadanda suka yi imani ,  kuma sun kasance suna  takawa).
Yayin da Allah ya ambaci dewa daga cikin kissoshin Annabawa tsira da amincin Allah su tabbata a gare su  a cikin suratul Shu'ara'I  ya ciken kissan  da fadin sa madaukakin sarki , bayan tsiran Manzannin sa da muminai tare da su :(  Hakika  lallai  akwai aya a cikin wancannanka, yawancin su ba su kasance muminai ba . Hakika Ubangijinka lallai shi ne mabuwayi mai jinkai )
Ibn kasir Allah ya mishi rahama ya ce: Hakika  lallai  akwai aya a cikin wancannanka.
Ai a wannan kissan da abunda ke cikinta na ban al'ajabi da taimako da karfafa ga  bayin Allah muminai akwai nuni da hujja na yanke  da hikima na kololuwa ( lallai Ubangijinka shi ne mabuwayi  )  wato wanda ya buwayi dukkan komai  kuma yayi galaba a kansa kuma ya fi karfinsa mai jinkai da halittunsa baya gaggawa ga wanda ya saba mishi sai dai ma yana sarara mishi kuma ya jinkirta mishi , sa'annan ya damke shi damka irin na mabuwayi mai iko,  Sa'id Dan Jubair  Allah ya kara mishi rahama ya ce  mai jinkai ga duk wanda ya tuba zuwa gare shi , maganan ta tike  a fadin Allah madaukakin sarki a kissan mutanen Ludu  amincin Allah ya tabbata a gare shi  lallai a cikin hakan a kwai ayoyi ga masu lura  katada yake cewa  ga masu lura Bagawi ya ambaci haka a cikin tafsirin sa mafi amfana da  abubuwan da suke faruwa na tarihi , da hikimomi na yanayi ,sai masu lura masu tunani wadanda suke koyi da  mutane na kwarai   masu neman gyara , kuma sukan bar ma'abota barna da fasadi amma shi wanda baya lura baya wa'azantuwa !  baya wa kanshi hisabi baya aiki don lahiransa addinin shi baya hanashi aikata komai , ko hankalin shi baya hana shi aikata munanan aiyuka  da laifuka wannan kamar fa dabba ne  Allah madaukakin sarki ya ce: (  ko kana zaton cewa ,  mafi yawansu suna ji , ko kuwa suna hankali ?  su ba su zama ba  face dabbobin gida  suke . A'a, su ne mafi bacewa ga hanya.)
A cikin Hadisi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gashi : (Lallai ne idan mumini yayi rashin lafiya sai cutar ta buge shi har ya mutu ,to zai zama  kaffara ne ga  zunubansa da suka shude, idan Allah ya sauwaka mishi to zai zama kankara ne ga zunubansa da suka shude, kuma wazi ne ga lokaci mai fiskantowa. Idan kuma munafuki ya yi rashin lafiya, sannan ya samu sauki to zai zama kaman rakumi ne da masu shi suka daure shi sannan suka sake shi, to bai san don me aka daure shi ba kuma don me aka sake shi ba.)  Nasa'I ne bya rawaito



 Allah bai ambaci tarihin Annabawa ba da Manzanni  da cikamakin su  Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  face don  ayi izina da tarihin su  a yi kuma koyi da shiryarwar su da halayen su  mku bi tafarkin su  hakika Allah ya umarci Annabinsa Muhammada tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da yayi koyi da su  sai mai tsarki ya ce :(  Wadancanne Allah ya shiryar sabo da haka  ka yi koyi da shiryarwar su . )  Allah madaukakin sarki ya ce :( Sabo da haka ka yi hakuri kamar yadda masu karfin niyya daga Manzannai suka yi hakuri).
 Allah madaukakin sarki ya ce game da  muminin yasin  :( Ya mutane na ku bi Manzannin nan ,  ku bi wadanda  ba su tambayarku wata ijara  , kuma su shiryayyu ne ).  Cikamakin su Annabin mu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wanda  Allah ya goge sauran shari'u da shi  kuma ya aiko shi da   shari'a mafi kamala   da addini , Allah ya dauki nauyi ga duk wanda ya yi riko da shi zai shiryar da shi ya bashi  kyakkyawar rayuwa  a duniya da lahira ya shigar tare da shi mafificin halitta gidan aminci  Allah madaukakin sarki ya ce : (Kuma wadannan da suka yi da'a ga Allah da Manzon sa , to wadannan suna tare da wadanda Allah ya yi ni'ima a kansu , daga Annabawa da masu yawan gaskatawa , da masu shahada da saliha  kuma wadannan nan sun kyautatu da zama abokan tafiya )  
To wani girmamawa ne ya fi wannan , to wani daukakane ya ke kusa da wannan  matsayi?, kamar yanda Allah  ya kissanta mana  kissoshin Annabawa amincin Allah ya tabbata a gare su da wadanda suka yi imani da su don muyi  koyi da su  kuma mu bi tafarkin tsira tare da su  muyi lura da tarihinsu mu kuma san halayen su  ,Allah ya kuma bamu kissan labaran masu karyata su kuma masu  musu da  gaskiya kuma masu girman kai daga binsu  wanda  suka fifita rayuwan duniya akan na lahira  masu bin sha'awe – sha'awen su da jin dadi , don fa mu yi izina da ukubar su, kuma mu wa'azantu da abinda ya faru da su  na walakacin duniya da azabar lahira kuma mu gargadu daga tsinuwan da aka tabbatar a gare su .
Allah madaukakin sarki ya ce :(Da Adawa da Samudawa ,  alhali kuwa lallai alamun azaba sun bayyana a gare su , daga gidajen su  kuma sahidan ya kawata musu ayukan su . sabo da haka ya kange su daga hanyar Allah  kuma sun kasance masu basira  .
Kuma Karuna da Fir'auna da Hamana . kuma lallai Musa ya zo musu da hujjoji, sai suka yi girman kai acikin kasa kuma ba su kasance masu tserewa ba , sabo da haka ko wannan su mun kama shi da  laifinsa: wato daga cikin su akwai wanda muka aika iskar tsakuwa a kansa ,  kuma daga cikin su akwai wanda tsawa ta kama , kuma daga cikin su akwai wanda muka birkice kasa da shi , kuma daga cikin su akwai wanda muka nutsar, ba ya yiwuwa ga Allah ya zalunce su , amma sun kasance kansu suke zalunta .
Allah madaukakin sarki ya ce :( ko wannan su ya karyata Manzanni  sai narko ya tabbata a gare su )  Allah madaukakin sarki ya ce a kissan Banu ndir :( To ku lura fa ya masu basirori,)  tarihin manzanni tsra da amincin Allah su tabbata a gare su tare da masu karyatawa na daga masu sabawa Allah da  Manzanni  mutane sun san su zamani bayan zamani , na karshe ya karba a gun na farko , wannan na daga cikin manyan hujjojin Allah akan bayinsa wurin karfafan gaskiya da sanin tauhidi  da taimakawa masu kadaita Allah  a cikin bata da shirka da gargadi daga gare  shi  amma lura da dabi'un halittu  da gano hikimanta da siffofinta  da tunani akan kirkiran da Allah ya mata da  tunani cikin  aikin  Ubangiji gayarsa da kuma fa'idansa shi ne kadaita Allah madaukakin sarki mabuwayi da daukaka da kuma bauta masa da mishi da'a , to wanda ya kebanta da halitta shi ne abin bautawa bisa cancanci . Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma lallai ne da abin lura a cikin dabbobin ni'ima; muna shayar da ku daga   abinda yake a cikin cikunansu  daga tsakanin tukar tumbi da jini, nono tsantsan mai saukin hadiya ga masu sha ) Aallah madaukakin sarki ya ce :( Allah yana juyar da dare da yini , lallai ne a cikin wannan akwai abin kula da ma'abota gannai)
  "ka ce ku yi dubi me ke cikin sammai da kasa, kuma ayoyi da gargadi ba za su yi amfani ba ga mutanen da basu ba da gaskiya da Allah ba "
To shi tuntuntuni cikin halittu ibada ne ga musulmi, amma daukan izina cikin wadannan halittu yana kara wa musulmi imani, kuma yana kara mishi zurfi cikin yakini, Allah Madaukakin sarki ya ke cewa :( Lalle ne a cikin sammai da kasa akwai ayoyi ga masu imani)
Tunani da lura na tabbatar da mai shakku, yana kuma raya zukata, yana haskaka gannai, yana mikar da halaye, shi kuma kauda kai daga tunani da lura yana kekasar da zukata, yana haifar da gafala,yana ja zuwa ga nadama, yana kuma jefa mutum cikin sabo    An karbo daga Abu Huraira Allah kara yarda a gare shi ya ce : ( Lalle Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce a isra'I : yayin da na sauko zuwa sama ta duniya sai na dubi kasa ta, to sai ga wata iska da kara da hayaki, sai na ce : me ye wannan ya kai Jibrilu? Sai yace : wadannan shaidanu ne ake kona su a gaban dan Adan basu tunani ga mulkin sammai da kasa ba don haka ba da sun ga abin mamaki) Ahmad ne ya rawaito
Aallah madaukakin sarki ya ce :( Lalle ne wadanda suka yi takawa idan wani tashin hankali daga shaidan ya shafe su, sai su tuna (Allah) sai ga su sun zama masu basira. Kuma 'yan uwansu (shaidanu ) suna taimakon su a cikin bata  sa'anan kuma ba su takaitawa).
Allah sanya albarka a gare ni da gare ku cikin Alkur'ani.
 Huduba ta biyu :
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya haskaka zukatan masoyansa da Alkur'ani, ya haskaka gannansu da imani, ya kawata ayyukansu da kyautatawa,
Ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi, bisa ga ni'imominsa da ba mai iyakance su koma bayansa,
Na shaida ba abin bauta wa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, mulki da yabo duka na shi ne, Mai rahama mai jinkai.
Na shaida cewa Annabinmu kuma shugabanmu bawansa ne kuma manzonsa ne, wanda aka kebantar da shi da dunkulallun kalmomi masu kamalar ma'ana da cikan bayani, Ya Allah ka yi salati da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma manzonka  Muhammad da iyalansa da sahabbansa, da wadanda suka bi su da kyautatawa
Bayan haka. Ku ji tsoron Allah Madaukaki zai gafarta muku,zai tattaro muku dukkan alheri a rayuwanku da bayan mutuwarku,
Ya ku bayin Allah ! Ku yi wa kan ku hisabi kafin a yi muku hisabi, kowannen ku ya duba game da karshen al'amari, da karewar ajali, to wanda ya yawaita lura to kurakuransa za su karanta, wanda duk ya kiyaye sabawa Allah da zunubai to zai rayu cikin aminci, kuma a datar da shi zuwa ga kyakkyawan karshe, mai samun sa'ada shi ne wanda ya waazantu da waninsa, mai hasara kuwa shi ne wanda waninsa ya waazantu da shi.
Hakika Allah ya  yi zambo ga masu bin son rai wadanda basu yi lura ba suka wa'azantu da abin da Allah ya basu na labarai, Allah Madaukakin sarki ya ce :( Kuma suka karyata kuma suka bi son zuciyarsu, alhali kuwa kowane al'amari (wanda suke son su tare daga Annabi ) an tabbatar da shi.  Kuma lalle abin da yake  akwai tsawatarwa a cikinsa na labarai ya zo musu.)
Ku saurara Allah Madaukakin sarki na da wasu hanyoyin da ya saba bada lada da alhaki akan su to duk wanda ya ci karo da sunnar Allah to za ta tambadar da shi ta tarwatsa shi ya fado ya kaskanta, Allah Madaukaki ya ce : (A kan hanyar Allah (ta gyaran jama'a) a cikin wadanda suka shude gabaninka , kuma ba za ka sami musanya wa ba ga hanyar Allah.)
Ya zo a hadisi (ku yawaita ambaton mai katse jin dadi mutuwa)

Ya ku bayin Allah : Lalle Allah da Mala'iku na salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi.
  
  

 vv

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق