الأحد، 29 يناير 2017

TUNANI GAME DA AYOYIN ALLAH(RANA) SHAIKH ABDUL MUHSIN ALKASIMI (17 SHAWWAL 1437 AH)

Hudubar Juma'a na  Masallacin Annabi 17/10/1437 tare da sheikh Abdulmuhsin Alkasim.
Hudubar farko.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacciya mai yawa.
Bayan haka, ku ji tsoron Allah yadda ya dace a ji tsoron shi – ya ku bayin Allah- ku yi murakabarsa a boye da bayyane,
Ya ku musulmai:
Abu mafi kyau da mutum zai sadaukar da rai don shi, shine tunani a ayoyin Allah da abubuwan ban mamaki na aikinsa, da kaura zuwa taallakan zuciya da himmatuwa da Allah ba wani abu cikin halittansa ba,
Ayoyin  ubangiji sune dalilai da hujjojin da bayi zasu san Ubangijinsu da su da sunayensa  da siffofinsa da ayyukansa, da kadaita shi,
 Kuma Tunani a halittun Allah ibada ne, kuma shiriya ne, kuma  shine mafarin alheri da mabudinsa, da shi ne bawa zai girmama Ubangijinsa, kuma ya kara imani da sakankancewa, kuma ya bude basira ta zuci, ya fadakar da shi daga gafalarsa, ya gadar mishi da rayuwa da lura da kauna ga Allah da tunani.
Tunani a ayoyin  Allah na daga cikin abu  mafi daraja daga cikin ayyukan zuci kuma mafi  amfani, yana kira ga aiki kuma ya sanya ma'abocinsa mika - wuya,
 Sufyan dan Uyaina Allah jikansa yace: "Tunani mabudi ne na rahama, ase ba ka gani mutum kan yi tunani ya tuba"
Shi ne abu mafi Alherin abin da zaa yi wa'azi ga bayi da shi. Allah madaukakin sarki yace : ka ce ni kawai ina yi muku gargadi da kalma guda wato ku tsayu domin Allah, bibbiyu  da dai dai, sa'an nan ku yi tunani )Saba'I 46
Idan mutum na tunani  to a komai zai zama yana da abin lura, Alkur'ani mai girma na cike da kiran halittu zuwa ga tunani bisa ayoyin Allah, da dubi ga halittunsa, Allah madaukakin sarki ya ce:  ( shin basu yi dubi ba a cikin mulkin sammai da kasa da kuma abin da Allah ya halitta daga komai). Araf 185
A cikin halittun Allah akwai  abin lura da wa'azi  Allah ya yi umarni da tunani game da su, sai yace: "ka ce ku yi dubi me ke cikin sammai da kasa" yunus 101
Shekul  Islam Allah ya mishi rahama ya ce : '' kuma  dubi zuwa ga halittun sama da na kasa don yin tunani da lura  abu ne da aka yi umarni da shi kuma mustahabbi ne''
 Hankula cikakku masu wayo su ke gane abubuwa bisa hakikanin yadda suke,  Allah ya yabi masu tunani cikin halittunsakuma lalle suna cikin masu zurfin hankali,Allah madaukakin sarki yace : ( Lalle ne a cikin halittar sammai da kasa da sabawar dare da yini akwai ayoyi ga ma'abuta hankali. Wadanda suke ambaton Allah a tsaye kuma a zaune a bisa sasaninsu, suna tunani akan halittar sammai da kasa, ya Ubangiji baka halitta wannan a kan banza ba, Tsarkin ka sabo da haka ka tsare mu daga azabar wuta. ) Ali Imran 190-191.
Allah ya yi zambo ga masu kauda kai daga tunani sai yace  : (kuma da yawa wata aya a cikin sammai da kasa suna shudewa a kanta kuma su suna bijirewa daga gare ta.) yusuf 105
Na daga cikin ukubobin  Allah karkatar da ayoyin shi daga masu girman kai, sai ya ce:
:( za ni karkatar da wadanda suke yin girman kai a cikin kasa ba da wani hakki ba daga ayoyi na kuma idan sun ga dukkan aya ba za su yi imani da ita ba).A'araf 146
 Hasanul Basri yace :( Abin da ya  hana su tunani a ciknta.)
Rana na cikin manyan ayoyin Allah na yau da kullum, Allah madaukakin sarki ya ce:( kuma akwai daga ayoyinsa dare da wuni da rana da wata,) Fussilat 37
 Allah ya sanya ta ga duniya haske a sama kuma fitila mai tsananin haske. tana gudu ba tare da sauti ba duk da girman gangan jikinta, tana tafiya bisa kididdiga mai zurfi  cikin yalwataccen falaki, zuwa ajali abin ambato, (Rana ba ya kamata a gare ta ta riski wata kuma dare ba ya kamata a gare shi ya zama mai tsere wa yini, kuma dukkansu a cikin sarari guda suke yin  iyo) yasin 40
Allah ya hore ta ga bayin sa,  to hudowarta da faduwarta ke bada tsayuwar  dare da yini, ba don samuwarta ba da al'amuran wannan duniya ya rikirkice, a cikinta akwai hikimomi da maslahohin da halittu ba za su iya iyakance su ba, Allah ya kafa hujja da shi bisa kadaicinsa da uluhiyyarsa sai ya ce : (kuma lalle  Idan ka tambaye su wane ne ya  halitta sammai da kasa,kuma ya hore rana da wata ? lalle suna cewa ; Allah ne.) Ankabut 61
Kuma ya sanya ta aya ga mutane masu hankali, Allah madaukakin sarki ya ce :
(kuma  ya hore muku dare da wuni, da rana da wata,kuma taurari horarru ne da umarninsa, lalle ne a cikin wancan, hakika akwai, ayoyi ga mutane wadanda suke hankalta.)Nahli 12
Ya kuma kirayi bayi zuwa ga dubi  ga horewarta da yayi na ban al'ajabi.sai ya ce : ( Ashe ba ku ga lalle Allah, yana shigar da dare a cikin rana ba, kuma yana shigar da rana a cikin dare, kuma ya hore rana da wata.) lukman :29
Kuma da su ne halittu ke kidanya lokutansu, kuma su san  manyan alamomi na al'amuransu na yau da kullum (kuma ya sanya dare mai nitsuwa, da rana da wata bisa lissafi) An'am 96
Kuma  Allah yahalicci inuwa, ya kuma sanya rana ta zama mai nuni a gare ta.
Imamul Baghawi  - Allah mishi rahama ya ce : " Ma'anar nuni a gare shi shi ne  cewa : Ba don rana ba da ba a san inuwa ba, kuma ba don haske ba da ba a san duhu ba, abubuwa ana gane su ne da kishiyoyinsu." Allah ya ta'allaka tafiyarta a matsayin  alama na da yawa daga cikin ibadoji kamar sallah sai yace : ka tsayar da sallah a karkatar rana zuwa ga duhun dare) Isra 78
Game da mafificin lokuta na Ambaton Allah yace : ( Kuma ka yi tasbihi game da gode wa Ubangijinka a gabanin fitowar rana da gabanin bacewarta) K 39
 A azumi kuma mai azumi zai yi buda baki idan ta bace.., na daga cikin alamomin lailatulkadri (Rana tana bullowa  wayan garin daren lailatul kadri tana halin bata haske mai karfi, a wannan wunin nata.)Muslim ne ya rawaito.
A ranakun (Ayyamuttashrik) Alhaji zai yi jifa ne na jamara bayan zawali.
  Lokaci na datsewar ibada na tuba  na  na fara wa ne da bullowar rana daga yamma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Allah na shimfida hannayensa da dare don mai laifin wuni ya tuba, kuma yana shimfida hannunsa da rana don mai laifin dare ya tuba har zuwa  rana ta fito daga yamma)  Muslim ne ya rawaito,
Lalle Allah na shimfida  hannayensa da dare don mai laifin rana ya tuba, kuma yana shimfida hanunsa da rana don mai laifin dare ya tuba, har rana ta fito daga  mafadanta, Muslim ne ya rawaito,
Da salla kafin hudowar rana da kafin faduwarta Allah ya sanya lada  gare ta mai yawa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (lalle za ku ga ubangijinku kamar yadda ku ke  ganin wannnan wata.ba ku tumurmusa, a  wajen ganinsa, idan za ku iya kar sallah ta kubce muku, kafin hudowar rana (Asuba) da faduwarta(sallar la'asar) to ku aikata hakan). Buhari ne ya rawaito.
Kisfewarta tsoratarwa ne na Allah ga bayinsa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :( Lalle rana da wata ba su kisfewa  sakamakon mutuwar wani ko rayuwarsa, sai dai suna cikin ayoyin Allah ne. Allah na tsoratar da bayinsa da su, idan kun ga kusufi ku ambaci Allah har sai ya yaye).Muslim ne ya rawaito
Sabo da girman  halittarta da yawan amfaninta  Allah ya rantse da ita sai yace: ( Ina rantsuwa da rana da hantsinta).  Shams 1
Tare da wannan girma kuma Allah ne ke tafiyar da ita, ita tana tasbihi gare shi, Allah madaukakin sarki yace :(Ashe baka gani ba lalle Allah wanda ya ke acikin sammai da wanda ya ke a cikin kasa yana yin sujjada a gare shi da kuma rana da wata da taurari,da duwatsu da itace da dabbobi da kuma masu yawa daga mutane.) Hajj 18
A kowani rana tana sujada ga Allah bayan  faduwarta, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce ; ya Abu zarri! Ko ka san a ina rana ke faduwa? Sai nace : Allah da Manzonsa ne suka fi sani, sai yace : lalle Tafiya ta ke yi har ta yi sujada a karkashin Al'arshi) wannan shine fadin Allah madaukaki. (Kuma rana tana gudana zuwa ga wani matabbaci nata, wannan kaddarawar mabuwayi masani.) Yasin 38
Buhari ne ya rawaito.
Kuma  Baiwa ce ga Allah ba'a bauta mata, na daga cikin shirka a yi mata sujada  Allah ya ce yace:( kar ku yi sujada ga rana ko wata  ku yi sujada ga Allah in kun kasance shi kadai ku ke bautawa)Fussilat 37.  
Faduwarta salo ne daga cikin salon da Annabawa suka rika na kira zuwa ga tafarkin Allah.
 Annabi ibrahim  Amincin Allah su tabbata a gare shi ya kafa hujja bisa uluhiyyar Allah da rushewar bauta mata da faduwanta. Allah  madaukakin sarki yace:( sa'annan a lokacin da ya ga rana tana bayyana yace ; Wannan shine ubangiji na, wannan ne mafi girma) sa'annan a lokacin da  ta fadi yace : ya mutane na lalle ne ni barrantace nake daga abinda kuke yi na shirka)  Lalle ne na fuskantar da fuskata ga wanda  ya kaga hallitar  sammai da kasa ina mai karkata zuwa ga gaskiya kuma ba ni cikin  masu shirka ) Al An'am 78-79
An fitini da yawa da ga cikin halittu  sai suka bauta mata koma bayan Allah, Huda huda tace da Annabi sulaiman, tana mai hakaitowa, game da sarauniyar saba'I da mutanenta,  (Na same ta  ita da mutanenta suna yin sujada ga rana baicin Allah, Kuma shaidan ya kawata musu ayyukansu saboda haka sai ya karkatar da su daga hanya  sa'anan su basu shiryuwa)   Annaml  24.
Musulmi bai kirdadan faduwan rana ko hudowarta da sallar sa,  a wannan lokacin ne wasu kafurai ke mata sujada, a dalilin sujadan wasu mutane gare ta sai shaidan ya kafa bauta gare ta yayin bullowarta da yayin faduwarta, yana nuna shi suke yi wa sujada, sabo da toshe kofar bauta mata aka hana musulmi  da ya kirdadi sallah kafin  fitowar rana ko faduwarta,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: (kar ku kirdadi fitowar rana ko faduwarta da sallarku domin tana hudowa ne a kahon shaidan) Muslim ne ya rawaito.
A yayin zawali na rana a kowani wuni  akwai wa'azi ga mumini, domin ana zuga wuta a ruruta(ana kunna ta a cika ta) to sai aka hana sallah a wannan lokaci, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : A wannan lokaci ne ake zuga jahannama) Muslim ne ya rawaito.
 Fitowar rana daga ta inda ba ta nan ta saba fitowa ba alama ne na kusancin Tashin Alkiyama. Kuma umarni ne daga Allah da rushewar duniya. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Alkiyama ba za ta tsaya ba har sai rana ta fito da mafadarta, ida ta fito mutane suka ganta duk sai su yi imani,  wannan shine lokaci da imani ba zai amfanar da rayi ba.) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
Kuma  farkon ayoyi da zai fito, fitowan rana daga yammacinta da fitawar dabba ga mutane da hantsi, kuma duk wanda ta riga dayanta fita to dayan ma na biye a kusa .
 kuma a matattara Allah yana hada mutanen  farko da na karshe a farfajiya guda,
  mai kira  na jiyar da su, kowa na ganin kowa, rana zata matsa kusa da halittu har ta kai tsakaninta da su kwatankwacin (Mel). Sulaim dan Amir Allah mishi rahama ya ce: "To wallahi ban san wanne yake nufi ba da mel na na auna kasa,ko  tsinken kwallin da ake sawa a ido ?"
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Mutane za su kasance cikin zufa kowa gwargwadon aikinsa, akwai wanda zai kai zuwa idon sawunsa, wani kuma zuwa guiwarsa, wani kuma zuwa kwankwasonsa, akwai wanda zai nuta cikin zufa, gumi ya kai  har zuwa bakinsa, ) Muslim ne ya rawaito,
  Mutane bakwai Allah zai musu inuwa a ranar da ba inuwa sai inuwarsa, son Allah ne da girmama shi ya hada su, sai Ubangiji ya yi yekuwa ya na cewa :(Duk wanda ya kasance yana bautawa wani abu to ya bi wannan abin, masu bautan rana sai su bi rana,sai a jefa su cikin jahannama, a wannan lokaci ne rana za ta dunkule haskenta ya tafi,kuma a jefa ta cikin jahima)
Allah madaukakin sarki ya ce: (Kuma idan aka shafe hasken rana)Takwir 1
Ibnu kasir –Allah mishi rahama- ya ce : "Abin da ake nufi da (kuwwirat):an tattaro sashenta aka hade da sashen sa'annan sai a nade ta a wurga ta, to idan an yi hakan da ita sai haskenta ya tafi.
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Rana da Wata za'a shafe haskensu ranar alkiyama,) Bukhari ne ya rawaito.
A cikin Aljanna babu rana ko jaura, don ana haska ta ne da hasken Allah. Mafi girman ni'ima ga 'yan Aljanna  ita ce ganin Allah, za su gan shi -Tsarki ya tabbata a gare shi- kamar yadda mutane a duniya suke kallon rana a tsakiyar wuni ba tare da girgije ba.
Sahabbai sun ce ga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: shin ko za mu ga Ubangijinmu ranar alkiyama? Sai ya ce: ( shin kuna cutuwa ga (Kallon) rana yayin da babu gajimare? Sai suka ce : aa ya manzon Allah. Sai ya ce : ( To kamar hakan zaku gan shi)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Bayan haka .. ya ku musulmai!
Dukkan halittu tun daga kwayar zarra har ya kai ga Al'arshi suna nuni ne akwai Allah,Duniya kuma na furuci ne da kadaitakarsa. Kallo  mai amfani shine wanda aka yi da idon basira ba da  tsurar ido kawai ba. Musulmi na aiki da hankalin sa da tunaninsa don ya yi wa kansa hisabi ya kuma gyara zuciyarsa.
Ku ambaci Allah ku girmama shi, ku fiskance shi da biyayya ku kadaita shi. Ku kiyaye daga gafala da bijirewa ku yi tasbihi a gare shi.
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa, (Wannan shi ne halittar Allah. To ku nuna mini , "Mene ne wadanda ba shi ba suka halitta? Aa, azzalumai suna cikin bata bayyananna") Lukman 11      
    Allah sa mini albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma, Allah  ya amfane ni da ku da abin da ke cikinsa na ayoyi, da ambato mai hikima, iya abin da zan fadi ina neman gafarar Allah ga ni da ku da dukkan musulmai daga dukkan zunubai, ku nemi gafararsa shi mai gafara ne kuma mai jinkai.



Huduba ta Biyu

Dukkan yabo ya  tabbata ga Allah bisa kyautatawarsa, godiya a gare shi bisa datarwarsa da baiwarsa, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya sha'aninsa abin girmamawa  ne. Na shaida Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne,tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa  da aminci tabbatacce mai kari.
Ya ku Musulmai:
Hikimar Allah ta hukunta ya sanyawa rana daguwa da sauka wanda ke haifar da zafi da kuma sanyi, ya a zafin bazara akwai wa'azi ga muminai, tsananin zafin shi daga tururin jahannama ne, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Wuta ta koka wa Ubangijinta sai tace: sashi na na cin sashe, sai ya mata izini da numfasawa biyu, Numfasawa a cikin hunturu numfasawa a lokacin bazara, shine tsananin zafi da kuke ji a bazara da tsananin sanyi da kuke ji na jaura.) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Duniya na gauraye ne da radadi da ni'ima, radadinta zai tuna mana radadin wuta kamar yadda ni'imarta zai tuna mana da jin dadi na aljanna. Jujjuyawarta daga sanyi zuwa zafi da kuma daga dare zuwa wuni dalili ne na karewarta da gushewarta.
Mumini wani abu ba zai raba shi da Allah ba, to zafi ba zai hana shi sallah ko azumi ba da biyayya da alheri, Allah ya zargi masu cewa :(kar ku fita a lokacin zafi) ya amsa da narko na azaba,(ka ce wutar jahannama ta fi tsananin zafi da sun kasance suna fahimta) Tauba 81
Abin mamaki ga mutumin da ya ke kare kansa daga zafin wutan duniya amma kuma bai karewa daga wutar Jahima?
Sannan ku sani Allah ya muku umarni da salati da aminci ga Annabinsa sai yace: a cikin Muhkamin littafinsa da ya saukar :(Lalle Allah da Malaikunsa suna salati ga Annabi. Ya ku wadanda suka yi imani ! ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi).Ahzab 56.
Ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga Annabinmu Muhammad,ya Allah  ka yarda da khalifofinsa shiryayyu, wadanda suka yi hukunci da gaskiya, kuma da shi suke adalci: Abubakar da Umar da Usman da Aliyu, da sauran sahabbai baki daya.mu ma ka yarda da mu tare da su da kyautarka da karamcinka, ya mafi karamcin masu karamci.
Ya Allah ka daukaka Musulunci da musulmai, ka kaskantar da shirka da mushrikai, ka ruguza makiya addini, ya Allah ka sanya aminci ga wannan gari da kwanciyar hankali da yalwa da sauran garuruwa na musulmai.
Ya Allah duk wanda ya nufe mu ko ya nufi gidajen musulunci da musulmai da mugun nufi, to ka shagaltar da shi da kan shi, ka maida mishi makircinsa cikin halakarsa, ka jefa tsoro cikin zukatansu, ya mai karfi mabuwayi.
(Ya ubangijika ka bamu mai kyau cikin duniya,da kuma mai kyau a cikin lahira, kuma ka tsare mana azabar wuta.) Bakara 201.
Ya Allah ka gyara halayen musulmai a ko ina, ya Allah ka sanya gidajensu gida ne na Aminci da yalwa, ya ma'aboci daukaka da karramawa.
(Ya Ubangijinmu! Mun zalunci kanmu, kuma idan ba ka gafarta mana ba, kuma ka yi mana rahama, hakika muna kasancewa cikin masu hasara.)Araf 23.
Ya Allah ka datar da jagoranmu da shiryarwarka,ka sanya aikin shi cikin yardarka.
Ka datar da dukkan jagorori na musulmai da aiki da littafinka, da yin hukunci da shariarka Ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka amintar da iyakokinmu, ka sanya gidajenmu gidaje ne na imani da karfi da tauhidi ya ma'aboci daraja da daukaka. Ya Allah ka taimaki sojojinmu ka hada zukatarsu ka tabbatar da diga digansu, ka taimake su a kan makiya ya Mai karfi Mai buwaya.
Ya ku bayin Allah:
(Lalle Allah na yin umarni da adalci da kyautatawa da baiwa ma'abocin zumunta, kuma yana hani da alfahasha da abin da aka ki, da zalunci, yana muku gargadi ko za ku na tunawa.) Nahli 90.

Ku ambaci Allah Mai girma da daukaka zai ambace ku,ku gode mishi bisa ni'imominsa zai kara muku. Ambaton Allah shi ya fi komai, Allah ya san Abin da ku ke aikatawa.      

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق