Hudubar Juma'a daga Masallacin Annabi 9/11/1437 Tare da Sheikh Abdulbari
Al subaiti
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata
ga Allah, Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, godiya mai yawa da
tsarkaka da albarka a cikinta,dukkan godiya da falala tasa ce, kamar yadda ya
tsarkake zukatan bayinsa da tausayawa juna, na shaida ba abin bautawa da
gaskiya sai Allah, shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, wanda ya sanya tunkudedeniya
sunna ta rayuwa,na shaida shugabanmu kuma Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma
Manzonsa ne, ya gargadi da jifan juna da kauracewa da alfahari, tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa, wadanda babban
sifa ta 'yan uwantakarsu akwai kawaici da yafiya ga juna,
Bayan haka:
Ina muku nasiha da ni kai na da tsoron Allah, Allah madaukakin sarki ya
ce :(ya ku wadanda suka bada gaskiya! Ku ji tsoron Allah ku kasance cikin
masu gaskiya) Tauba 119
Yayin da muka yi lura da koyarwar Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi da rayuwarsa za mu samu ya yi nesa da dorawa kai nauyi da
wuce gona da iri a maganganunsa da ayyukansa da abincinsa. kuma musulunci ya
koyar da mu : cewa duk yadda ayyuka suka daukaka suka yi kyau to ba zai dace a
yi alfahari da shi ba muddin ya rasa imani, Allah madaukakin sarki ya ce (: Shin
kun sanya shayar da mahajjata da rayar da masallaci mai alfarma kamar wanda ya
yi imani da Allah da ranar lahira, kuma ya yi jihadi a cikin hanyar Allah, ba
su daidaita a wurin Allah) Tauba :19
Amma yin alfahari da kai da ambaton
kyawawan halaye da matsayi na kabila ko dangi da tinkaho da ta'adodi da
ji da kai da bayyana niimomi da sunan isa, to sifofi ne ababan zarga, kuma naui
ne na rauni irin na dan adam, kuma dalili ne na raunin mutum da rashin cikan
hankalinsa, Allah madaukakin sarki ya ce : ( Lalle Allah bai son
dukkan mai takama mai alfahari) Lukman :18
Mafi hadarin sura na alfahari da ke
barazana ga akidar musulmi shi ne Riya, wanda Annabi ya siffanta shi da
karamar shirka, shi ne mutum ya tashi ya na sallah sai ya kawata sallarsa
sabo da sanin wani mutum na kallonsa, )
Na daga cikin sifofi na alfahari akwai bayyana sabo, wanda zai haifar da
mummunar karshe ga maabocinsa.
Alfahari da jiji da kai ya bata
sunan maana mai kyau da kararamci ke dauke da shi, ta hanyar sanya israfi da
almubazzaranci har ya kai shi ga wauta da musu da kafurcewa niima, da
almubazzaranci da musulunci ya hana.
Alfahari da isa ya hada da dagun kai da tinkaho, wanda ya ginu akan ji da kai da riya da girman
kai , Allah madaukakin sarki ya ce :(Alfahari da yawan dukiya da dangi ya
shagaltar da ku,*Har kuka ziyarci kaburbura) Takasur 1-2.
Masu alfahari sun ta'allaka ne da abubuwa na zahiri, sakamakon juyawan
maauni, da fadawa cikin wahamin cewa karfi na ga abubuwan shigowa na kayan masarufi
na rayuwan duniya mai juyawa da gushewa.
Ba ya boyuwa ga mai hankali cewa : dukiya da lafiya da kyau da matsayi
kyauta ne na ubangiji Mabuwayi da daukaka, kuma suna juyawa, to ya wajaba ga
mutum ya fiskance su da kankan da kai ba da tinkaho da alfahari ba.
Kur'ani ya bayyana halin wadanda
su ke alfahari da dukiyansu da 'ya'yansu sai ya ce :(Mu muka fi yawan dukiya
da 'ya'ya kuma mu ba abin azabtarwa ba ne.) saba'I 35. sai Allah mabuwayi
da daukaka ya maida martani a gare su :(dukiyoyinsu
da 'ya'yansu ba za su wadatar musu da komai ba daga Allah.) Ali Imran :10
Shuhura cuta ce mai tsanani, masu nemanta da kauna sune masu gudu bayan
kawawainiya, basu damu ba ko da kuwa zai kai ga sabawa addini da kyawawan
halaye, mai neman shahara na rayuwa ne a daure a gaban idunuwan wadanda zai
burge, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Duk
wanda ya sanya tufafi na shuhura ta Allah zai sanya mishi tufafi na kaskanci
ranar alkiyama).
Na daga cikin gurbi mafi hadari da alfahari ke haifarwa akwai lalatawa
musulmi addini : domin addini na iya
lalacewa sakamakon kwadayin daukaka na duniya. Musamman idan mutum ya nufi riya
ko neman a san shi ko a ji shi. Wannan dabiar na haifar da kaskanci da
walakanci da tozarci Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya ce :( Duk wanda ya nemi a ji shi to Allah zai sa a ji shi
kuma wanda yayi riya da aikinsa Allah
zai sa aga aikin nasa ) Bukhari ne ya rawaito
Kamar yanda alfahari a cikin ibada na tafiyar da albarkan aikin ya kuma lalatashi
Allah madaukakin sarki ya ce (shin dayanku na son cewa wani lambu ya
kasancewa a gareshi na dabinai da inabi koramu tana kwarara a cikinta yana da
dukkan ya‘yan itaciya acikinta alhali tsufa ya riskeshi kuma yana da zuri'a
rawnana kuma guguwa ta sameta da wuta take cikinta ta kone kurmus ) Bakara 266.
To wannan aiki na gari asalinshi
kamar gona ne me girma me yawan ya'yan itace, shi kuma bayyana aiki da
nufin alfahari da riya kamar iska ne mai wuta aciki da ya afka ma gona zai gama
da ita gamawa sai ya tafiyar da duk albarkatunta ya lalata ta.
Mutun ya kan zame a gidansa da kewayen iyalansa da wani abu na alfahari
da isa ta hanyan bijiro da wasu abubuwa na zamantakewa da barna a shimfidi da
kayayyakin gida da sura ko mutum mutumi, wanda haka ya kunshi ketare iyaka a wurin sadaki da bukukuwan
aure.
Alfahari yana zamar da mutum ya
fada zuwa ga mantuwan godewa mai ni'ima da yaba wa falalansa Allah madaukakin sarki ya ce ( idan
tsanani ya samu mutum sai ya roki ubangijinsa yana komar da alamarinsa zuwa gare shi sannan
ida ya bashi ni'ima daga gareshi sai ya mance abinda ya kasance yana kira zuwa
gareshi gabannin haka )Zumar 8. wato zai rika takama da alfahari da ni'ima sai
ya manta da ubangijinsa da ya kasance yana
bauta masa yana kankan da kai zuwa gare shi.
Alfahari : abu ne me tunkudawa zuwa ga rena wasu, kamar yadda haka ya bayyana
a halin iblis cikin Fadinsa (ni na fishi alheri ka halicceni daga wuta kuma
ka halicce shi da tabo)A'araf 12, to
sai ya jingina zalunci zuwa ga
ubangijinsa a nashi zaton cewa shi ne mafifici.
Dauka wa kai alfahari da tinkaho yana lalata tunanin musulmi game da sako
na cigaba da raya kasa : gudu bayan da'awar banza da kuma abubuwa na
zahiri wanda akwai yaudara a cikinsu
yana jefa mutun musulmi ne zuwa
ga sha'awe sha'awen rayuka da kuma nitso
cikin abin da bai da amfani na daga ayyuka.
Na daga cikin illolin alfahari yana rusa al'umma, Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gareshi ya ce (kawai Allah
yana taimakon wannan alumman ne saboda masu rawninta, kuma da adduoinsu da kuma
sallolinsu da kuma tsarkake niyyarsu ) nasa'I ne ya rawaito
Wannan yana bayyana cewa riya da
kwadayin abubuwa na zahiri sababi ne na galaba akan al'umma.
A cikin alfahari da tinkaho da aikin alkhairi akwai tunzura zuciyan musulmai daga marasa galihu cikinsu wanda suke cikin
kunci na rayuwa sakamakon rashin abin hanu, na daga cikin illoli na alfahari da
tinkaho yaduwar hasada yayin da mutum yake magana akan ni'imomin da Allah yayi
a gareshi ta hanyan takama da alfahari
da ruduwa, ko ta hanyan janyo hassadar mahassada.
saboda haka kuma da
waninsa musulunci ya gandaya ukuba mai tsanani akan yin alfahari da takama,da
tinkaho da duk surorin shi da nau'ukanshi,
har a tafiya Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata agare shi ya ce : (yayin da wani mutumi yana alfahari yana tafiya a cikin tufafinsa kansa na burge shi Allah sai ya nitsar da shi a
kasa yana nitso a cikinta har rana
kiyama ) muslim ne ya rawaito shi
Allah sa mini albarka ni da ku ya amfane ni da ku da abin da ke cikinsa
na ayoyi, da ambato mai hikima, iya abin da zan fadi ina neman gafarar Allah
mai girma ga ni da ku da sauran musulmai daga dukkan zunubai, ku nemi gafararsa
shi mai gafara ne kuma mai jinkai.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya yi halitta ya daidaita,
wanda ya kaddara kuma ya shiryar, ina gode masa – tsarki ya tabbata a gare shi-
ina godiya a gare shi bisa ni'imominsa da ba za su kidanyu ko akididdige su ba, Na shaida ba abin bautawa
da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, Madaukaki kuma
Mafi daukaka.Na shaida shugabanmu kuma Annabinmu Muhammad bawansa ne, kuma
Manzonsa ne, wanda aka turo shi da haske a shiriya, tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi,da iyalansa da sahabbansa, wadanda suka biyo sawunsa.
Bayan haka:
Ina muku wasiyya da ni kai na da jin tsoron Allah – Mabuwayi da
Madaukaki.
idan ni'imomi suka bayyana a tattare da mutum ba tare da nufin ya bayyana
su ba ko yayi dagun kai ga wasu ba to wannan ba laifi Allah ya ce : ( kace wanene ya haramta adon
ubangiji wanda ya fitar da shi saboda bayi da dada'da na arziki) A'araf 32
An umurci musulmi da ya ambaci ni'imomin da Allah ya yi masa kamar yadda
Ubangijinmu yake so ya ga alamar
ni'imarsa ga bawansa ta hanyan godiya a gareshi – Mai tsarki da daukaka
- da kyakyawan yabo ba wai ta fiskan alfahari ba Allah ya ce : (kuma amma ni'imomin
ubangijinka sai ka fada (domin godiya) Adduha 11
babu laifi a shari'ance a boye ni'ima, kai shi ne ma asali idan har
ma'abocinta yana tsoron hasada da kambun
ido, Allah ya ce game da Annabi ya'akub
(yace ya kai dan yaro na kada ka labarta mafarkinka ga yan uwanka kada su
maka kaidi, kaidi hakika shaidan ga mutum makiyi ne bayyanenne )Yusuf 5
kuma Manzon Allah tsira da
amincin Alla su tabbata a gare shi ya ce (ku nemi cimma bukatunku ta hanyar
boyewa domin duk wani ma'abocin ni'ima abin abin a yi mar hasada ne ).
Ku saura! Ku yi salati – ya ku bayin Allah- ga Manzon Shiriya, hakika Allah ya umarce ku
da hakan a cikin littafinsa sai ya ce: ( Lalle Allah da Mala'ikunsa suna
salati ga Annabi, ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da
sallama tabbatacciya.) Ahzab 56.
Ya Allah ka yi salati ga Muhammad da matayensa da zuriyarsa, kamar yadda
ka yi salati Ibrahim da Alayensa, ka sa albaka ga Muhammad da matayensa da
zuriyarsa, kamar yadda ka sa albarka ga Ibrahim da iyalansa.
Ya Allah ka yarda da khalifofi guda hudu shiryayyu: Abubakar da Umar da
Usman da Aliyu da Iyalai kuma da sahabbai masu daraja, ka game mu tare da su, a afuwarka da karamcinka da kyautatawanka, Ya Mafi
jinkan masu jinkai,
Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai, Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai, ka
kaskantar da kafurci da kafurai, Ya Allah ka rusa makiyanka kuma makiya addini,
Ya Allah ka sanyawa wannan garin aminci da natsuwa, da sauran garuruwa na
musulmai.
Ya Allah duk wanda ya nufe mu ko ya nufi musulunci da musulmai da mugun
nufi to ka shagaltar da shi da kansa, ka sanya halakarsa cikin mugunyar
shirinsa, ya Mai sauraron Adua.
Ya Allah mai saukar da littafi, Mai tafiyar da girgije, Mai ruguza
runduna,ka rusa makiya musulunci, ka taimake mu akan su ya ubangijin talikai,
ka taimake mu a kan makiyanka makiya addini, da rahamarka ya mafi jinkan masu
jinkai.
Ya Allah muna rokonka shiriya da
takawa da kame kai da wadata.
Ya Allah muna rokonka dukkan alheri na gaggawansa da na nesa, wanda mu
ka sani da wanda ba mu sani ba, muna neman tsarinka daga dukkan sharri, na kusa
da na nesa, wanda muka sani da wanda ba mu sani ba.
Ya Allah muna rokonka Aljanna, kuma muna neman tsarinka daga wuta.
Ya Allah ka gyara mana addininmu,wanda shi ne tsari ga al'amuranmu, kuma
ka gyara mana duniyarmu wanda rayuwarmu ke cikinta, ka gyara mana lahirarmu
wanda gare ta zamu koma, ka sanya rayuwarmu kari ne ga dukkan alheri. Ka sanya
mutuwa ta zama hutu ne gare mu daga dukkan sharri, ya ubangijin talikai.
Ya Allah ina rokon ka alheri mafarin shi da makuran shi,da matattarin
shi, da farkon shi da karshen shi, na bayyane da na boye, muna rokon ka
darajoji madaukaka a Aljanna, ya
Ubangijin talikai,
Ya Allah ka taimake mu kar ka taimaki wani akan mu, ka bamu nasara, kar
ka bawa wani nasara akanmu, Ya Allah ka shirya mana yadda zamu iya maida
makircin makiya akanmu, kar ka basu dama da zasu iya mana makirci, ka shirye mu
kuma ka saukake sharia gare mu, ka taimake mu a kan wanda ya zalunce mu.
Ya Allah ka sanya mu masu anbatonka, masu godiya a gare ka. Masu kankan
da kai gare ka, masu komawa da rusunawa gare ka.
Ya Allah ka karbi aduarmu.ka tafiyar da kullin zuci daga kirazanmu, ya
Ubangijin talikai, Ya Allah ka jikan matattunmu, ka bada lafiya ga marasa
lafiyanmu, ka jibinci al'amuranmu, ka yaye mana bakin-ciki.
Ya Allah ka kiyaye Mahajjata ga dakinka mai alfarma, Ya Allah ka kiyaye
Mahajjata ga dakinka mai alfarma, Ya Allah ka kiyaye Mahajjata ga dakinka mai
alfarma, ka nesantar da su daga sharri da zunubai.
Ya Allah ka maida su gidajensu lafiya, suna halin samun nasara da lada
ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka sanya shi Hajji ne mabruri Wanda aka yi wa Allah
biyayya a ciki. Kuma ka sa aikin su ya zama abin godiya zunubansu kuma abin gafartawa, da aiki na
kwarai karbabbe ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka datar da jagoran mu cikin abin da ka ke so kuma ka yarda da
shi, ya Allah ka datar da shi zuwa shiriyarka , ka sanya aikin shi cikin
yardarka ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka datar da dukkan jagororin musulmai zuwa ga aiki da
littafinka,da yin hukunci da shariarka, ya mai jinkan masu jinkai.
(Ya Ubangiji Mun zalunci kawunanmu muddin baka gafarta mana ka yi mana
rahama ba lalle za mu kasance cikin hasararru) A'araf 22
(Ya Ubangiji ka gafarta mana da 'yan uwanmu da suka riga mu da imani,
kar ka sanya kulli a cikin zukatanmu game da wadanda suka yi imani, ya ubangiji
lalle kai mai tausayi ne kuma mai jinkai) Hashr 10
( Ya ubangiji ka ba mu kyakkyawa a nan duniya kuma ka bamu kyakkyawa a
lahira
Kuma ka kare mu daga azabar wuta) Bakara 201.
(Lalle Allah na yin umarni da adalci da kyautatawa da bai wa ma'abocin
zumunta. Kuma yana hani ga alfahasha da abin da aka ki da zalunci, yana muku
gargadi ko zaku waazantu). Nahl 90
Ku ambaci Allah sai ya ambace ku, ku gode mishi bisa ni'imominsa zai
kara muku, ambaton Allah shi ya fi girma Allah ya san abin da ku ke aikata wa.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق