الأحد، 29 يناير 2017

TAUSASA ZANCE NA SHAIKH SALAH MUHAMMAD AL BUDAIR ( 24 SHAUWAL 1437 AH)

Hudubar Masallacin Annabi 24/10/4137 Tare da sheikh Salah dan Muhammad Albudair
HUDUBAR FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Mai karamci Mai yawan kyauta, Ya fifita tsakanin halittunsa cikin fahimta da ilmuka da hankula da laduba, Ya haramta alfahasha da batsa da zagi,Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, gare shi nake kira, kuma zuwa gare shi makoma ta.Na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma ga Alaye da Sahabbai baki daya.
Bayan haka, Ya ku musulmai!
Ku ji tsoron Allah, to duk wanda ya ji tsoron Allah ya rabauta a ranar sa ta yau da ta gobe, kuma Musulmi shi ne wanda musulmi suka kubuta daga sharrin harshensa da na hanunsa, ( Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi magana madaidaiciya) Ahzab 70.
Ya ku Musulmai: 
Mumini na tunkudo alheri , kuma yana tausayawa halittu,
 Sauki a zance  da tattausawa a magana, da Taushi cikin tattaunawa, tafarki ne mikakke da ake karkato da zukata, ta kan janye soye soyen rayuka daban daban, kuma ta dawo da zukata da suka yi nesa, da ra'ayoyi mabanbanta,
 Allah madaukakin sarki yace ga musa da Harun : ( Ku ce da shi zance mai taushi ko zai fadaka ko ya ji tsoro)
Ibnu kasir Allah ya mishi rahama yace:  "wannan aya akwai abin lura mai girma, wanda ita ce Fir'auna ya kai kololuwa cikin sabawa Allah da dagun kai shi kuma Musa zababben Allah ne na cikin halittu a wancan lokaci, amma duk da haka aka yi mishi umarni da kar ya fiskanci fir'auna sai da magana mai taushi da kuma tausasawa".
Ya ku Musulmai :
Zagi kan yada fitintinu,kuma  zagi bai dawo da gudajje, kuma bai janyo abokin musu, sai dai kawai ya haifar da gaba da kiyayya da kullin zuci, kuma ya kara wa mai jayayya dogewa da musu.
Duk wanda yake zagin abokin adawarsa  yana jifansa da alfahasha, ya munana zance game da shi,ya aibata shi da kalamai marasa kyau,  to ya dada kwambala ruwa akan tabo ne,  ya kuma karawa cuta rashin lafiya ne (ma'ana ya dada kamari da rikita al'amura kamar wanda ya karawa wuta fetur ne).
Ma'aboci mummunan hali da zafin harshe mai yawan cin mutunci, mai sukan jama'a, mai kazafi ga wadanda basu ji ba ba su gani ba, mai cin zarafin bayin Allah, mai yawan aibata mutane da cin namansu, wanda bai furuci sai da alfahasha da zagi, ba zai taba zama mai kawo gyara ko nasiha ba, ko malami ba.
Abubuwa na gaugawan faruwa cikin al'uma, ba wani kara da mutane zasu ji ko faduwan wani abu, ko wata wakia  ta kusa ko ta nesa, face sun garzaya ga yanar gizo wato internet, suna rikan wannan wakiar  abin zagi da za su rika zagin juna da shi suna bibiyar shi suna yada shi. Suna masu gaggawa zuwa ga hanyoyin sadarwa na sada zumunta  suna kai hari tsakanin mai jifa da mai harbi , da mai suka da mai tsinuwa da mai zagi sai kadan daga cikinsu wadanda Allah ya tarfawa garin su nono.
Ya ku wadanda ku ke rubuta tsinuwa da zagi da sake tuhume –tuhume da hukunce – hukunce! Ku sani zaa tambaye ku game da abinda ku ke rubutawa, a ranar da halittu za su tattaru a cikinta, kuma a auna dukkan ayyuka, da mintuna da ka sarayar, ko wace rai za ta zo da mai shaida da mai kora ta.
Ya wanda ya buya bayan fiskar wayarsa ko naurarsa, ya wanda ya fake da suna na karya, ya yi nesa daga idanuwa! Ya zame yana auna wa waninsa zagi da tsinuwa! Ka manta Allah ya na ganinka ne? A halin kuwa yana sane da sirrinka da ganawarka.
Mumini ba mai suka ne ko tsinuwa ko batsa da mummunar magana ba.
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bai kasance mai zagi ba ko mai maganar alfahasha ko tsinuwa ba, ya kuma ce : (Lalle ni baa turo ni mai tsinuwa ba sai dai ni an turo ni rahama ne.)
zagin musulmi fasikanci ne) kuma yace ( Masu zagin junansu su biyu shaidanu ne, suna cin zarafin junansu, kuma suna karya akan junansu).
 Daga Jabir bin sulaim Allah yarda da shi lalle  yace ga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi,: A sanar da ni abin da zan kiyaye shi na kuma lizimce shi, : sai yace (kar ka zagi wani! ) yace :" Bayan haka ban sake  zagin kowa ba, da ne ko bawa, rakumi ko akuya ba".
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da shi: ( Idan mutum ya zage ka, ya aibata ka da wani abu da ya sani game da kai, to alhakin hakan na kan shi,)Abu Dauda ne ya rawaito.
Ya kai bawan Allah!
Ka tuba daga abin da hannayenka suka rubuta, ka goge zaginka da cutarwarka da ka yi wa wani.ka tuna fadin Mahaliccinka Majibincinka :(kuma kace wa Bayi na , su fadi kalma wacce take mafi kyau. Lalle ne shaidan yana sanya barna tsakaninsu. Lalle ne shaidan ya kasance ga mutum makiyi bayyanane.)Isra'i  53.
Ya Allah ka mana ilhaman shiriyarmu ka kare mu daga sharrin kawunanmu.
Ina neman gafarar Allah ku ma ku nemi gafararsa, don shi Mai gafartawa masu komawa a gare shi ne.



Huduba ta biyu
Dukkan yaba da godiya sun tabbata ga Allah da yace : ( kuma ku  fadi magana mai kyau ga  Mutane) Bakara 83. Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya, shahadar da muke  fatan samun rabauta da maikyau a dalilinta, Na shaida kuma Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad Bawansa ne kuma Manzonsa ne, zababben Annabi,kuma Manzo zababbe, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa, salati mai wanzuwa da aminci mai biyo wa da yawa.    
Bayan haka, Ya ku musulmai:
Ku ji tsoron Allah hakika mai tsoron Allah ya rabauta, shi kuma Mai sabo ya yi hasara.
(Ya ku wadanda ku ka bada gaskiya ku ji tsoron Allah, kuma ku kasance tare da masu gaskiya)Tauba 119.
Ya ku Musulmai:
Hakika Allah ya hani muminai  zagin abin bautan mushrikai, sabo da kar zagin nasu ya zama sanadin zagin Allah madaukakin sarki.
To zagin abin bautansu zai kara musu kafirci da sangarcewa da gujewa, to sai zagin nasu ya zama ya sabawa manufan Allah game da kira da manufa na sakonsa. 
Allah madaukakin sarkin yace : (kuma kada ku zagi wadanda suke kira, baicin Allah, har su zagi Allah bisa zalunci,ba da ilimi ba.)An'Am 108.
Lallai a kiyaye dukkan kiyayewa! Kada ku riski bayin Allah da kaushi da tsanani, da suka da tsinuwa da zagi har ku kai su su guje wa gaskiya da sunnah da halaye masu kyau.
Ku bayyana gaskiya ta hanyar hujja da dalili, da bayani cikin hikma da tausasawa tareda  basira, kawai abin da ya wajaba a gare ku shi ne : Nasiha, da umarni da hani, baakan ku shiryar da su da tankwara su ba da  gyara su ba, ,Hisabinsu na gun Allah ba a kanku ba,haka ma sakayyansu.
Ku yi salati da sallama bisa ga Ahmad Mai shiryarwa, mai yi wa dukkan mutane ceto, duk wanda ya mishi salati guda to Allah zai mishi salati goma dalilinta.
Ya Allah ka yi salati da aminci ga bawanka kuma Manzonka Muhammad, Ya Allah ka yarda da dukkan iyalai da sahabbai, mu ma ka hada da mu tare da su ya mai karamci ya Mai yawan kyauta.
Ya Allah ka daukaka musulunci da Muslmai , ka kaskantar da shirka da mushrikai, ka rusa makiya addini,ka sanya aminci da kwanciyan hankali ga wannan gari da sauran garuruwan Musulmai.
Ya Allah ka datar da shugabanmu jagoran al'amarinmu cikin abin da ka ke so kuma ka yarda da shi, ka ja shi zuwa ga biyayya da tsoron Allah, Ya Allah ka datar da jagororin al'amuran Musulmai su yi hukunci da shariarka, kuma su bi sunnar Annabinka Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
Ya Allah ka tseratar da masu rauni cikin Musulmai ya Ubangijin talikai, Ya Allah ka tseratar da masu rauni cikin Musulmai ya Ubangijin talikai, Ya Allah ka tseratar da masu rauni cikin Musulmai ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka kashe kafurai da suke saddu ga tafarkinka, masu gaba da masoyanka, ka sanya musu azabarka, Ya abin bauta na gaskiya Ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka bawa marasa lafiyan mu sauki,ka bada lafiya ga wanda ka jarabce shi a cikinmu, ka saki  kamammu na gurin yaki, ka jikan matattunmu, ka taimake mu kan wanda ya yi gaba da mu, Ya Allah ka kawo aminci a iyakokinmu, ka kiyaye sojojinmu, ka basu karfin guiwa, ka taimake su kan makiyin ka kuma makiyinsu, Ya Ubangijin talikai, Ya Allah ka karbi matattunsu cikin shahidai, ka kawo waraka ga wadanda suka ji rauni a cikin su.ya Mai karbar adua. Ya Allah ka sanya aduarmu ta zama karbabbiya, ka sanya kiranmu ta samu daukakuwa, Ya Mai girma ya mai jinkai ya mai karamci.

  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق