السبت، 28 يناير 2017

FALALAR GARIN MAKKAH NA SHAIKH ABDULMUHSIN ALKASIMI(HUDUBAR 23 Zulkida 1437

Hudubar Masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na 23/11/1437 Ah
Da sheikh  Abdulmuhsin Bin Muhammad Alkasim
Hudubar farko
     Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma wanda Allah ya batar da shi babu mai shiryar da shi, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
Shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, kuma na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne,tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da iyalansa da sahabbansa  da aminci tabbatace mai yawa.
Bayan haka:
 ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah yadda ya cancanci a ji tsoronshi, ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci,
Ya ku musulmai!
Allah ya kebanta da halittawa, da gudanarwa da zabi, zabinsa na nuni ne ga rububiyyarsa  da dayantakarsa madaukaki,da cikar hikimarsa da iliminsa da ikonsa, Hakika  Allah madaukaki ya fifita tsakanin wurare da zatuttuka, da ayyuka da wattanni, da dararraki da ranaku.
Mafi alherin halittu shi ne Annnnabi muhammmad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mafi alherin aiki shine kadaita Allah da bauta , mafi daraja daga cikin  watanni shine watan ramadan, kuma mafi daukakan  dare shi ne daren lailatul kadri, mafi alherin  rana shine ranar suka (Babbar sallah) kuma mafi alherin wuri a gun Allah kuma mafi soyuwa a gareshi shine makkah,Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce: ( Wallahi lalle ke ce mafi  alherin kasar Allah kuma mafi soyuwar kasa a gun Allah madaukakin sarki kuma ba don an fitar da ni daga cikinki ba da ban fita ba) Ahmad ne ya rawaito shi ,
ita ce uwar alkaryu kuma waninta  na  biye mata ne, Allah ya rantse da ita, don  nuni ne zuwa ga girmanta sai yace :(Ubangiji na rantsuwa da wannan gari (Makka), tare da rantsuwa  ya kira shi da gari amintacce, sai ya ce; ( Da wannan gari amintacce).
Masallacin makka ne mafi daukaka cikin masallatayya, shi ne dakin farko mai albarka da aka sanya a doron kasa don shiryar da mutane, : ( kuma lalle ne daki na farko da aka aza domin mutane hakika shi ne wanda ke Bakka mai albarka kuma shiriya ga talikai) Ali Imran 95
Abu Zarri Allah kara yarda a gare shi yace:( ya manzon Allah: wani masalllaci ne aka  fara  aza shi  a doron kasa? Sai yace :( Masallacin ka'aba), sai nace  saannan sai wanne? Sai yace (masalllacin Aksa) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
Allah ya shiryar da Annai  Ibrahim zuwa ga gina  dakin kaba,  a cikinta, Allah madaukakin sarki ya ce (Kuma a lokacin da muka iyakance wa Ibrahim wurin dakin ) Hajj 26
Sai ya daga shi da dansa Annabi Isma'ila, kuma khalilin Allah ya roki a jefa son Makka a  zukatan mutane da farin ciki lokacin zuwa gare shi sai ya ce (sai ka sanya zukata daga mutane ta dinga karkata izuwa garesu) ibrahim '37.
 Allah ya zabe ta domin mafi karamcin manzanninsa, a cikinta ne aka haifi Annabi muhmmad tsira da amincin Alla su tabbta a gare shi kuma acikinta ya taso kuma acikin ta aka turo shi, kuma a cikinta aka fara sauko da wahayi da alkur'ani, Manzon Allah ya  rayu a cikinta sama da shekaru hamsin, daga nan kira na musulunci ta taso, kuma a nan ne mafi alherin mutane bayan Annabawa wato sahabbai suka taso, daga nan ne aka yi tafiyan dare da shi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi zuwa ga masallacin Aksa.
Manzon Allah ya so shi so mai yawa, an kuma fitar da shi daga garin makkan a halin tilasci, yayin da  ya sauka madina ya kasance  yana adu'a (ya Allah ka jefa mana son madina kamar yadda ka sanya mana son makka ko sama da haka). Buhari da Muslim,ne suka rawaito shi . Gari ne mai aminci Annabi  Ibrahim yayi mar addua na neman aminci sai ya ce :  (ya ubangiji na ka sanya wannan gari amintacce ) Bakara 126
 Allah yayi ma garin baiwa  inda yake cewa, (Asai  basu ganin mun sanya harami amintacce kuma ana kaiwa mutane hari  a kewayenshi )Ankabut 67.
 Malam kurdubi Allah ya masa rahama yake cewa : " lalle makka bata gushe ba cikin aminci  kuma cikin alhurma daga masu dagun kai da girgizan kasa da kuma sauran abubuwa na fitintinu da ke sauka a kasa.
Duk wanda ya shiga Masallacinta zai samu aminci irin nata Allah (Mai tsarki da daukaka )yake cewa : ( Duk wanda ya shige shi  zai kasance  amintacce) Ali Imran 97.
 Allah ya sanya mata alhurma tun lokacinda ya halicci sammai da kasa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce: (lallai Allah ya sanya ahurma wa makka tun randa ya halicci sammai da kasa, sai ta kasance tsararriya ce  da alhurman Allah har zuwa ranan Alkiyama) buhari ne ya rawaito.
  Annabi ibrahim shi ya bayyana wa halittu  alfarmarta kamar yadda manzon Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,yake cewa: (lalle  Ibrahim  ya haramta garin makka) Bukhari da muslim suka rawaito.
Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana girmamata, a ranan hudaibiyya yake cewa :( na rantse da wanda raina ke hanunshi baza su tambayeni wata kudda ba wanda suke girmama Alhurman Allah  a cikinta sai  na basu ita ) Bukhari ne ya rawaito
Na daga cikin Alhurmanta akwai cewa : Zubar da jini a cikinta ba tare da hakki ba ya fi muni da alfarma akan watan ta.
Manzon Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce : (Baya halatta ga mutumin da yayi imani da Allah da ranan lahira da ya zubar da jini a cikinta) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
Ba a tsorata mutanenta ta hanyan rike makami a cikinta manzon Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce : ( Ba ya halatta ga dayanku ya riki makami a makka )muslim ne ya rawaito.
Haka dabbobi ma amintattu ne da amincin Allah a farfajiya ko fili, su kuma tsuntsaye suna masu tafiya ne cikin jeji )  kuma itatuwanta na kadawa da aminci ba a sare ta,  kuma baa tsintuwan batattun dukiya a  a cikinta kamar sauran garurruka  manzon Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce :  (ba a tsinke danyen itaciyarta haka nan kuma ba a yanke bishiyarta sa'annan kuma ba a kora abin farawtarta haka nan kuma ba a tsintuwan abin tsintuwan cikinta sai ga wanda zai nemi me shi)Bukhari da muslim ne suka rawaito.
  Manzon Allah ya kamanta alhurman dukiyoyi da mutunci da kuma jini  saboda girman hurumcinta Allah Madaukakin sarki ya ce :  (lallai jininku da dukiyoyinku  da mutuncinku haramtacce ne a gareku kamar haramcin wannan rana naku a wannan gari naku kuma da wannan wata naku ) Buhari da muslim ne suka rawaito.
  wanda yayi niyyan aikata mummuna a cikinta Allah zai  azabtar da shi  Allah  Madaukakin sarki ya ce : (wanda yayi nufin aikata aikin  ilhadi  a cikinsa da  zalunci zamu dandana masa daga wata azaba mai radadi  ) Hajji 25

Dan masud  -Allah kara masa yarda – " ya ce : Da wani mutum zai yi nufin  ilhadi kuma yana garin Adan  Da Allah ya dandana masa azaba mai radadi ".  
kuma mai zalunci a cikinta shi ne wanda Allah yafi ki a cikin mutane,  Manzon Allah  (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya ce : (wanda Allah ya fi ki a cikin   mutane   shi ne mai ilhadi  a harami ) Buhari ne ya rawaito.
Saboda girman alhurmanta mushriki baya taka kasanta,  sai  Allah ya ce : (lallai mushrikai masu najasa ne kar su kusanto masallacin harami)Tauba 28.
  kuma dujjal shine ya kafurce wa Allah yana fitinan mutane a addininsu,   sai Allah  ya hana shi  shiga makka da madina,Manzon Allah  (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi )  ya ce (Babu wani gari da dajjal baya takawa sai Makka da Madina )Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
  Allah ya kiyaye makka kuma zata cigaba da zama cikin kiyayewar  Allah, duk wanda ya nufe ta da mummuna  Allah zai  halaka shi, mutanen giwaye sun  nufe ta da sharri, sai  Alla ya kangesu kuma ya sanya su suka zama aya da darasi har zuwa ranar sakayya,
  wasu mutane zasu yaki garin ka'aba har sai idan sun kasance a wata sahara  sai  Allah ya kisfe na farkonsu har zuwa  na karshensu)  Bukhari ne ya rawaito. 
Kamar yadda Allah ya sanya aminci a cikinta, ya yi falala ga mutanenta da alhkairu da 'ya'yan itace, duk da cewa tana kwari ne a tsakanin duwatsu biyu wanda ba  shuki, duwatsu ne ke kewaye da ita ta kowani gefe, kasar da gu ne da zaa tsammaci yunwa, sai Ibrahim ya yi adua ga mutanenta da a azurta su da 'ya'yan itace, kamar yadda Allah ya azurta garuruwa masu ruwa, da shuki, sai yace :
(kuma ka azurta mutanenta da yayan itace )Bakara 126.
 sai Allah ya amsa da cewa ( shin bamu tabbatar musu da mallakr hurumi ba ya zama amintacce ana jawowa zuwa gare shi  'ya'yan itace  kowani irin bisa ga azurtawa daga garemu?)Kasas 57.
A'a ai Annabi  Ibrahim ya mata adduan albarka a cikin kwanon awunta da mudunta, wato cikin abin shanta da abincin ta,
Na daga cikin Adduar  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce (ya Allah ka sanya a madina ribin Abinda ka sanya a makka na Albarka )Buhari da muslim ne suka rawaito.
Ya shayar da mutanen ta ruwan da ba irin shi a doron kasa, wanda mutane na fatan samun ko dan kadan ne daga gare shi. Ruwan zamzam ruwa ne mai albarka kuma abin ci ne Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : :( lallai ruwa ne mai albarka kuma abin sha ne mai dadano ) muslim ne ya rawaito  har ila yau waraka ne daga dukkan cuta manzon Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce(zam zam abinci ne kuma abin sha ne waraka ne kuma ga cuta )  Muslim ne ya rawaito.
Malaika ya tsaga kirjin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya wanke shi da ruwan zamzam.) Bukhari ne ya rawaito
Samuwar arziki da kuma aminci  a cikinta abubuwa ne da za su sa a bauta wa Allah shi kadai,  Allah Madaukakin sarki ya ce: ( su bautawa ubangijin wannan gida (kaba)* wanda ya ciyar da su (ya hanasu daga yunwa kuma ya amintar da su daga wani tsoro )) kuraish 3-4
 Allah zai tunkude sharri daga mutanenta a dalilin girmama daki da suke yi a cikinta da kuma kadaita Allah,  Allah Madaukakin sarki ya ce : (Allah ya sanya ka'aba daki me alfarma rayuwa ga mutane ) Ma'ida 97.
Ibnu kasir ya ce : wato ze dauke musu mummuna sakamakon girmama fiskantanta,
 Makka gari ne mai albarka alherinta gamamme ne,  da na daga cikin Albarkanta ribanya sallah a cikinta don (sallar mutum a masallacin ka'aba ya fi sallah dubu dari a waninsa ) Ahmad ne ya rawaito,  yin dawafi a dakin ka'aba ibada ne kuma ba za a hana wani ba  daga cikin mutane  cikin dare ne ko wuni  Allah ya ce (kuma suyi dawafi a daki dadedde ) Hajj 29
wuraren nata alamomin  addini  ne  kuma wurarene na bauta ga musulmai, Allah ya wajabta  musu fiskantanta  kuma ya sanyata daya daga cikin rukunnan musulunci ,
matafiyi zuwa Masallacinta na samun lada,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi ya ce : (ba a nika gari zuwa ga kowani masallaci sai  guda uku masallacin ka'aba da masallacin Manzon Allah da Masallacin aksa) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
  Babu wani wuri a doron kasa da ake kewaya shi da sunan ibada sai dakin ka'aba haka kuma ba wani wuri a duniya da aka shar'anta sumbatan shi, sai  Hajarul – Aswad, da ke ka'aba,  rukunul  yamani na ka'aba  ake shafa wa.
 Allah ya sanya ka'aba wurin neman lada, da kuma wurin komawa  kuma da aminci  gare ta ne mutane ke cacarindo  shekara bayan shekara daga kowani sako mai zurfi,  rayuka na begensa kuma zuciya na kwadayin zuwa gare shi a duk lokacin da suka ziyarce ta sai begensu ya karu zuwa gareta.  Annabawa sun nufe shi , Annabi Musa da  Annabi  Yunus da Annabi Muhammad  sun yi hajji, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce; (kamar gani ina ganin Musa (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) yana sauka daga tsakanin duwatsu ya na mai kakan da kai zuwa ga Allah da talbiya, kamar ina dubi zuwa ga yunusa dan matta Amincin Allah ya tabbata agare shi ya na kan jar taguwa a halin  yana mai talbiya) Muslim ne ya rawaito.        
Allah ya daukaka wannan daki ya jingina shi zuwa gare shi, kuma ya sanya shi wurin daukaka tauhidi da haskaka shi, ya yi umarni da a tsarka ke shi daga dukkan wani abu da zai kishiyanci hakan na daga gumaka da bauta musu, sai ya ce (ka tsarkake dakina don masu dawafi da masu tsayuwa da masu yawan ruku'u da sujada) Hajj 26
Ya sanya zuwa gare shi ya zama kankara ne ga zunubai da kusakurai da suka shude, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce : (wanda yayi hajji a wannan dakin kuma bai yi jimai ba, kuma bai yi  fasikanci ba  zai dawo kamar yadda mahaifiyarsa ta haife shi ) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
  Allah bai  yarda  da wani lada  ga wanda ya ziyarci ka'aba ba koma bayan Aljanna ba,  Annabi Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce :( Daga umra zuwa wata umra kankara ne ga zunubai, aikin hajjin da aka yi da'a bai da sakamako sai aljanna ) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
   kuma shi ne alkibila  na mutanen doron kasa baki daya,kuma dukkan musulmi na fiskantan shi sau da dama a kowani rana   Allah Madaukakin sarki ya ce : ( sai ka juya fiskarka wajen masallaci tsararre kuma inda duk kuka kasance to ku juyar da fuskokinku jiharsa)Bakara 144.
Wanda ya mutu cikin musulmai za'a fiskantar da kabarinsa zuwa gare shi.
 Ubangiji mai tsarki ya sanya masa alhurma   ba a fiskantan jihar shi yayin fitsari ko kuma ba haya,  Manzon Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce : (kada ku fiskanci alkibila da bahaya ko bawali sai dai ku fiskanci gabas ko kuma yamma )Bukhari da Muslim ne suka  rawaito.
  zuwa gareshi ne ake kora  hadaya da kuma abin da za a nemi kusanci zuwa ga ubangiji  Allah Madaukakin sarki yake cewa : (sa'annan kuma wurin halatta ta zuwa ga dakin yantacce ne ) Hajj 33
A dakin kaba akwai ayoyi bayyanannu, lallai yana daga cikin ginin Ibrahim, akwai  Makama ibrahima, Amincin Allah ya tabbata a gare shi, Allah ya ya umarce mu da mu mu rike shi gurin sallah, a dakin Allah mai girma akwai Hajarul Aswad (ya sauko  daga Aljanna a halin ya fi nono fari,sai kusakuran bani adam ya bakanta shi) Ahmad ne ya rawaito shi.
shi dutse ne da baya amfanarwa ko kuma  cutarwa, kawai dai ana sumbatan shi domin bin sunna na  Annabi Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sayyidina Umar Allah ya kara masa yarda ya ce : (lallai ni na san kai dutse nebaka cutarwa kuma baka amfanarwa ba don na ga Annabin  Allah yana sumbattanka ba da ba zan sumbanceka ba ) Bukhari da Muslim suka rawaito.
A Masallacin ka'aba akwai Safa da Marwa,   suna daga cikin manyan alamomi na  ibada  wajibi ne a girmamasu a kai komo a tsakaninsu.
 A dakin Allah akwai zamzam,abin lura ne kuma aya ne cikin yawansa da albarkansa da amfaninsa.
Kuma Bayan Ya ku Musulmai:
Dakin Allah an gina shi ne don bautawa Allah shi kadan shi bashi da abokin tarayya,  yana daga cikin wuraren da ake karban tuba, kuma ake komawa zuwa ga Allah,
 ga  duk bawa ya nufi wannan masallaci na ka'aban yana mai kankan da kai da rusunawa ga Allah yana mai neman kusanci zuwa ga mai tsarki Madaukakin sarki don neman a yafe masa zunuban shi. Wajibi ne akan bayi su girmama dakin Allah, don  girmama abin da Allah ya girmama na daga cikin tsoron Allah, a cikin hakan akwai   gyaruwan  Musulmai a cikin addininsu da duniyansu.
Duk wanda yayi  hidima wa Masallatai biyu masu alfarma, da alhazai da masu umrah da masu ziyara, to sakayyansa fa yana wurin Allah ne mai girma,   dukkan Masallatan biyu Annabi ne ya gina su, kuma suna cikin guraren ibada a gurin Allah,
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan abin jefewa.
(Kace) An umarce ni in bautawa Ubangijin wannan gari, wanda ya mayar da shi Hurumi, kuma yana da dukkan kome. Kuma an umarce ni da na kasance cikin masu mika wuya.) Namli 91.
Allah mini albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma, kuma ya amfanar da ni da ku da abin da ke cikin shi na ayoyi da ambato mai hikima, Ina fadin wannan bayanan nawa kuma ina neman gafarar Allah wa ni da ku da dukkan musulmai daga dukkan zunubai, ku nemi gafararsa don lalle shi mai gafara ne mai jinkai.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo sun tabbata ga Allah  bisa kyautatawarsa, da kuma godiya bisa ga datarwan shi da baiwarsa, Na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai bashi da abokin tarayya muna masu girmama sha'aninsa kuma na shaida lalle Annabinmu  Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi da iyalansa da sahabbansa kuma da tsira tabbatacciya mai yawa.
 ya ku musulmai:
A wannan gari mai albarka amintacce musulmai suna sauke hajjinsu suna masu tsiraituwa daga dukkan wasu abubuwa na duniya da kwadaye kwadayenta, suna mika kawunansu ga Allah kuma suna masu bauta mishi kuma suna neman a 'yanta su, tawhidi ya hadasu kuma kuma Imani ya tausasa zukatansu ya hada  su, suna masu bayyana da'a ga Allah madaukakin sarki  suna masu kankan da kai kuma suna jayuwa a tafarkin Allah, suna masu nuna talaucinsu ga Allah suna neman bukata a wurin shi kuma suna rokon Allah, kuma suna masu yawan ambaton Allah halin zaman gida ko tafiya.
A wurare na ayyukan ibada na aikin hajji akwai abin lura da kuma wa'azuzuka, dukkan mutane a wurin Allah daya suke,ma' aunin  shi ne tsoron Allah, haka nan kuma a wurin ihrami da kuma tattaruwan mutane akwai  tunatar da su, game tattaruwan da zasu yi a matattara wato ranar alkiyama, wanda za'a karbi nashi shine wanda ayyukansa ya kasance yayishi da ikhlasi don Allah bai cakuda shi da shirka ba, ko  riya ko rashin  bin sunnar Annabi, lokutan hajji na da tsada, kuma wanda ya samu dace shi ne wanda ya ribaci wannan lokutan ta hanyan yawaita ambaton Allah da kuma Ayyuka na kwarai.
Sa'annan ku sani lallai Allah ya umarce ku da salati da aminci ga Annabinsa , sai yace cikin
Alkur'ani : ( Lalle Allah da Mala'ikunsa suna salati ga Annabi, ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama tabbatacciya.) Ahzab 56.
Ya Allah ka yi salati da aminci da albarka bisa ga Annabinmu Muhammad, Ya Allah ka yarda da khalifofinsa shiryayyu, wadanda suka yi shude akan gaskiya kuma da ita suke hukunci: Abubakr, Umar, Usman, Ali, da sauran sahabbai baki daya, ka hada mu da su cikin kyautar ka da karamcinka ya mafi karamcin masu karamci.
Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai, ka kaskantar da shirka da mushrikai, ka ruguza makiya addini, ka sanya wannan gari cikin aminci da kwanciyar hankali da  yalwa da suran garuruwan musulmai.
Ya Allah duk wanda ya nufe mu ko ya nufi gidajenmu ko ya nufi musulmai da mummunar manufa to ka shagaltar da shi da kansa, ka sanya kaidinsa a makasansa, ka jefa tsoro cikin zuciyarsa ya mai karfi ya mabuwayi.
Ya Allah ka amintar da Alhazai da masu Umra, ya Allah ka sanya Hajjinsu karbabbe, aikinsu abin godiya, da aikinsu  karbabbe, ya maabocin daraja da karramawa, ya Allah ka gyara musu niyoyinsu da zuriyarsu, ka saukar musu da kwanciyar hankali da natsuwa, da khushu'I da kankan da kai gare ka ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka gyara halin musulmai a ko ina, ya Allah ka amintar da iyakokinmu, ya Allah ka karfafi zukatan sojojinmu, ya Allah ka datar da  jifansu, Ya Allah ka basu nasara mai karfi, ya ma'abocin daraja da daukaka.
Ya Allah ka datar da jagoranmu zuwa ga shiryarwarka, ka sanya aikinsa cikin yardarka.
Ya Allah ka datar da masu hidima ga Masallatayya biyu masu alfarma, ka daga ladansu, ka sanya su cikin masoyan bayinka, ya ma'abocin daraja da daukaka.
(Ya Ubangiji ka bamu kyakyawa a nan duniya da kyakkyawa a lahira kuma ka kare mu daga azaba na wuta.) Bakara 201
Ya ku bayin Allah: (Lalle Allah na yin umarni da adalci da kyautatawa da bai wa ma'abocin zumunta. Kuma yana hani ga alfahasha da abin da aka ki da zalunci, yana muku gargadi ko zaku waazantu). Nahl 90
Ku ambaci Allah mai girma da daukaka zai ambace ku, ku gode mishi bisa ni'imominsa zai kara muku, kuma ambaton Allah ya fi girma Allah ya san abin da ku ke aikatawa.

     


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق