Hudubar Juma'a a
Masllacin Annabi tare da sheikh Aliyu dan
Abdurrahman Alhuzaifi 7/12/1437
Hudubar Farko:
Yabo da godiya sun tabbata ga Allah, (Dukkan Godiya da yabo sun tabbata ga Allah wanda ya halicci sammai da
kasa ya kuma sanya duffai da haske)
An'ami 1,
kuma ya shar'anta shario'i, rahama ga bayi
domin lada ya yawaita ga talikai kuma ya tunkude musu ukuba da dukkan sharri,
ina yabo ga ubangiji na kuma ina gode mishi kuma ina tuba gareshi, kuma ina
neman gafaran shi, kuma na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi
kadai ne bashi da abokin tarayya masani ga abin da ke cikin zukata, kuma na shaida
Annabin mu kuma shugabanmu Muhammad
(Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)
bawansa ne kuma Manzonsa ne, mai kira zuwa ga dukkan aiki na biyayya. ya
Allah kayi salati da sallama da albarka
wa bawanka kuma manzonka muhammad da
iyalansa da sahabbansa wadanda suka taimaki addinin Allah Madaukaki, har dukkan
mushrikai masu yawan kafurci su ka
rusuna masa.
Bayan haka : ku ji soron Allah madaukaki, da gaggawa zuwa ga
ayyukan Alheri, da nisantan haramtattun abubuwa, don shi Ubangiji madaukaki ya
cancanci a kiyaye dokokin shi a ji
tsoron shi, ba wadanda zasu rabauta sai masu tsoron Allah, ba hasararru sai
wadanda suka juya baya su ka sa shakku a addinin Allah.
Ya ku musulmai!
Lalle
kuna cikin ranaku masu albarka da falala, sauran kwanakin nan goma da
Allah ke ribanya ladan ayyuka na kwarai, yana kyale tuntube da aka yi a cikin
su, kuma yana karban uzuri daga wanda ya bada uzuri, kuma Allah na karbar tuban
wadanda suka tuba, ya yafe zunuban masu neman gafara.
An karbo daga Abdullahi
dan Abbas Allah kara musu yarda,yce ; Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce; (Ba wasu
ranaku da ayyukan alheri ya fi soyuwa a gurin Allah kamar wadannan ranaku goma) sai su ka ce
har da jihadi? Sai yace : har da jahadi, sai dai mutumin da ya fita da ransa da
dukiyansa bai dawo da komai ba.) Buhari ne ya rawaito.
An karbo daga Abu
Huraira Allah kara yarda a gare shi yace :
daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (
Ba wasu ranaku da ya fi soyuwa ga Allah da a yi bauta a cikin su kamar goman
farko na zulhajji, azumin kowani rana na daidai da azumin shekara, tsayuwan
kowani dare na daidai da tsayuwan daren lailatul kadri,) Tirmizi da Ibnu maja
da Baihaki,
A cikin wannan goman akwai ranar arafa, wanda Allah ya yalwata alheri a
cikinta, falala da albarka na sauka a cikinta, da rahama ga wanda ya halarce
ta, kyautayin Allah da karamcinsa na
kwarara ga dukkan musulmai a doron kasa,
a wannan wunin,
An karbo daga Abu
katada Allah kara yarda a gare shi, daga Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi: (an tambaye shi game da azumin ranar Arafa sai yace : yana
kankare zunuban shekaran da ta gabata da mai zuwa,) Muslim ne da Abu Dawud suka rawaito.
An karbo daga Aisha
Allah kara yarda a gare ta, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce: (Babu wata rana da Allah ya ke yawaita 'yanta bayi daga wuta
kamar ranar arfa, lalle Allah na kusantowa ya bayyana, sannan ya yi tinkaho da
su a gaban mala'iku, sai ya ce: me wadannan ke bukata?) Muslim ne ya rawaito da
Nasai.
Daga Abdullahi dan
Umar Allah ya kara yarda a gare su, daga Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi yace: ( Idan yammacin Arafa ya yi ba wanda zai rage cikin
wadanda akwai kwayan zarra na imani a zuciyarsa face Allah ya gafarta masa, sai na ce ya
manzon Allah ya kebanci mutanen Arafa ne kadai? Yace : a 'a , ga dukkan
musulmai! ) Dabarani ya rawaito a Al- Kabir.
An karbo daga ubada
dan samit Allah ya kara yarda a
gareshi kan lallai manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a greshi ya ce
: (Annabi ya ce a ranan arfa :ya ku mutane ! lallai Allah ya muku falala
a wannan rana ya gafarta muku, sai dai nauyin wani da ke kan wani a tsakaaninku (Hakkoki) kuma yayi kyautan( ceton) masu musgunawanku ga
masu kyautatawanku, ya bawa mai kyautatawanku abin da ya roka, to ku tunkude, idan
ya kasance a muzdalifa sai ya ce :lalle Allah ya gafartawa na kwarai a cikin ku
, kuma na kwaranku zasu yi shafa'a ga na
banzanku, rahama na sauka gare ku ta game su, sai a raba gafara a doron kasa
sai ta sauka kan duk wanda ya tuba cikin
wanda ya kiyaye harcensa, da hannunsa,kuma iblis da rundunarsa na kan dutsen Arafa, suna
sauraron abin da Allah zai yi , idan an saukar da gafara sai ya yi yekuwa shi
da rundunarsa suna ( wayyo azaba ta da Halaka, na kasance ina ingiza su wani
lokaci, sannan gafara ta zo ta lullube su, sai su rarraba suna wayyo Allah mun
boni mun lalace.) Dabarani ne ya rawaito a Al kabir. Tsayuwan Arfa shi ne rukuni mafi girma a hajji,
Ayyukan hajji da aduo'in alhazai na game
dukkan musulmai a doron kasa. kai ai
manyan Ibadoji da alamomi na hajji suna amfanar da kasa baki daya. Sai Allah ya
tunkude azaba da ita ko ya sasssauta zunubansa. Allah madaukakin sarki ya ce:(
Allah ya sanya ka'aba daki mai alfarma rayuwa ga mutane al'amarin addininsu na
hajji yake mikewa sabo da shi,) Ma'ida 97.
Al Bagawi Allah ya
jikan sa ya ce: Ai abin da zai mikar musu da addininsu da duniyarsu.
Allah madaukakin sarki
ya ce : ( Kuma ba domin tunkudewar Allah ga mutane sashinsu da sashe ba lalle ne da kasa ta baci, kuma
amma Allah maabocin falala ne a kan talikai) Bakara 251
Al- Bagawi ya ce a
tafsirinsa: ba don tunkudewar Allah ga
muminai masu biyayya ba daga kafurai da fajirai ba da kasa ta halaka da wanda
ke cikinta, sai dai Allah na tunkudewa kafiri a dalilin muminai haka yana
tunkudewa fasiki a dalilin salihin bawa.) ya tike.
Bayan Arafat akwai
ranar babbar sallla da ranakun tashrik sune mafi alherin ranaku a gun Allah
madaukaki, ya shar'anta ayyuka na kwarai da Allah ke ribanya lada da su, da
kuma irin abin da Allah zai tseratar na daga azaba, A ranar babbar sallah Allah
ya hada mafiya yawan ayyukan hajji a cikinsa, sune jifa da yanka da aski da
dawaful ifada, kuma bisa wannan tsari ya fi, amma in da zaa fara gabatar da
wani kafin wani, to ba laifi sai dai an bar abin da ya fi. sabo da manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a ranar babbar sallah baa tambaye
shi ba game da wani abu da aka kaddamar ko aka jinkirta ba face ya ce ku yi ba
laifi.
Kuma Allah ya ambaci
ranar babbar sallah da Ranar babban Hajji.kuma yana cikin mafi alherin ranaku a
gurin Allah madaukaki. Ranar sha daya ga wata ke bi masa, shi ake cewa ranar ALKAR, da ranaku biyu da ke bi
masa shine cikaton ranakun Attashrik , ya shar'anta sauran ayyukan hajji
kamar yadda aka shar'anta yawan ambaton Allah ga alhaji da waninsa.
Daga Abdullah dan kurad
Allah ya kara yarda a gare shi, daga Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Mafi alherin ranaku a gun Allah shi ne ranar
suka, sai ranar Karr) Tabarani da Ibn
Hibban suka rawaito.
Ku godewa Allah bisa abin da ya yalwata muku na ni'ima, da abin da ya
shar'anta muku na sabuban rahama. Ku girmama albishirin da Allah ya yi mana, ku
karbe ta da farin ciki da yakini, Alkawarin Allah mai kasancewa ne ba sabawa, Allah madaukakin sarki yace : (saannan kuma
abin bautawar ku Abin bautawa ne guda, sai ku sallama masa kuma ka yi bushara
ga masu kankantar da kai. Wadanda su ke idan an ambaci Allah sai zukatansu su
firgita da masu hakuri akan abin da ya same su da masu tsayar da sallah, kuma
suna ciyarwa daga abinda mu ka azurta su ). Hajj 34-35.
Allah madaukakin
sarki ya ce: kuma ku gabatar da alheri sabo da
kan ku, ku ji tsoron Allah kuma ku sani cewa lalle ne ku masu haduwa da shi ne,
kuma ka yi albishir ga muminai)
Ku gaggauta ayyuka na
kwarai kafin zuwan ajali, da katsewar ayyuka, domin duniya gida ne na rudi,
matattara nena musibu da sharri, ku dubi
yanda ta yi da masu kwadayinta, da kuma yadda ta shelanta rabuwa da su, ba gida
ne na dawwama ba, ko ni'ima na dindindin ba, gidan mumini ita ce gidan aminci
gidan ni'ima da zama wanda bai sauyawa
ko gushewa, ku yi aiki don ita game da abin da Allah ya kira ku zuwa gare shi
ku yi nesa da abin da Allah ya gargade ku ga me da shi, kamar ga ku da ranaku
sun juya baya, ga lokacin mutuwa ya yi, to a wannan lokacin ne kowa zai yi da
na shina, Me kyautatawa zai yi fatan ace ya kara aikin alheri, mai sabo zai yi
kaito da nadama sakamakon tafiyarsa da ba guzuri, ya ku musulmi a wadannan
ranaku, duk wanda Allah bai nufe shi da hajji ba, to Allah ya shar'anta mishi
kofofi na da'a da ayyukan kwarai masu yawa
da zai riski wanda ya sha gaban shi, ko ya cin ma wanda ya yi mar
fintinkau, da izinin Allah madaukaki, wanda aka datar da shi da yin hajji to ya
godewa Allah madaukaki, ya kuma kyautata wa kansa ta hanyar aikata daa da barin
abin da aka ki, ya zuba alheri nsa ya kame daga sharrinsa ya kiyaye dokoki na
wannan farilla, kuma ya godewa Allah bisa abin da ya saukake masa na sabuba, da
kuma irin baiwa da Allah ya yi wa Alhazai na daga aminci da imani, da saukin
arziki, da saukake abubuwa masu wahala, to godiya ta tabbbata ga Allah bisa
ni'imarsa na bayyane da na boye. Godiya tana gare shi a cikin duniya da lahira,
Allah madaukakin sarki ya ce : ( sabo da haka Kuma ku ambace ni na ambace ku
kuma ku yi godiya gare ni kuma kada ku butulce mini) Bakara 152
Allah ya saka wa wannan
kasa mafi alherin sakayya, bisa abin da
ta ke tashi da shi na hana kansu barci don Alhazai su samu hutu, haka ma masu
umra da ziyara. Da kuma kulawa da take ba su ta bangaren lafiya. Da saukake
musu duk wata hidima da kawo zaman lafiya, da abin da ake gani a kowace shekara na daga tsare tsare da ta cin ma, na
ban mamaki wanda ya bawa duniya mamaki,cikin ayyukan hajji don neman lada,
muminai na farin ciki da haka,
Allah Madaukakin sarki
ya ce : ( Ku yi gaggawa zuwa ga
gafara daga Ubangijinku da Aljanna da fadinta (daidai) da sammai da kasa ne, an
yi tattalinta domin masu takawa. Wadan da suke ciyarwa a cikin sauki da
tsanani, kuma suke masu hadiyewar fushi, kuma masu yafewa mutane laifi kuma
Allah ya na son masu kyautatawa.) Al Imran 133-134.
Allah sa min albarka ni
da ku cikin Alkur'ani mai girma.kuma ya amfanar da ni da ku da abin da ke ciki
na ayoyi da ambato mai hikima, kuma ya amfanar da mu da shiryarwar shugaban
Manzanni, da fadinsa mikakke, abin da na fadi kenan ina nemawa kai na da ku
gafara daga dukkan zunubai. Da sauran musulmai daga dukkan zunubai, to ku nemi
gafararsa don shi mai gafara ne mai jinkai.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga maaboci buwaya da daukaka, maabocin girmame girmame, mai girma
madaukaki, ina yabon Ubangiji na ina gode masa ina tuba zuwa gare shi, kuma ina
neman gafararsa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke
ba shi da abokin tarayya,mai tsananin hila, na shaida Annabin mu muhammad tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi wanda Allah ya tsamar da dan Adam ta hanyarsa daga bata.
Ya Allah ka yi dadin
tsira da aminci da albarka ga bawanka kuma Manzonka Muhammad da Sahabbai da
Iyalai, bayan haka! Ku ji tsoron Allah madaukaki yadda ya dace a ji tsoronsa,
duk wanda ya ji tsoronsa zai kare shi daga abubuwa masu halakarwa, a duniyarsa
da lahirarsa,
Ya ku bayin Allah ! ku
tuna abin da Allah ya muku na niima cikin farillai na hajji, na daga 'yan
uwantaka na musulunci, da madauri na imani, da hadin kai na mafiskanta da ke
kawo hadin kai na zuciya, da hadin kai na sahu
da ke haifar da yada rarrabuwa da sabani, Allah madaukakin sarki ya ce :(
kuma ku kankame igiyar
Allah gaba daya kuma kada ku
Rarraba) Al imran
103.
Allah madaukakin
sarki ya ce: (su muminai 'yan uwan junane a cikin addini) Hujurat 10.
Allah madaukakin sarki
ya ce: (ya ku mutane hakika mun halicceku daga namiji da mace kuma muka
sanyaku dangogi da kabiloli domin ku san juna lalle mafificinku daraja a wurin
Allah shi ne wanda yake mafificinku a
takawa) Hujurat 13
. Kuma ku tuna wasiyoyin
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shida hudubarsa a hajjin ban
kwana : na daga cikin abin da aka kiyaye daga gare shi a wannan hajji tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi fadinsa : Ku bauta wa ubangijin ku, ku yi
sallolinku biyar, ku azumci watanku, ku yi biyayya ga mai jagorantar ku za ku
shiga aljannar ubangijinku ) Ahmad ya rawaito daga hadisin Abu Umama Allah
kara yarda a gare shi.
Ya ku bayin Allah !
( lalle Allah da
malaikunsa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a
gare shi da aminci tabbatacce.
Ku yi salati da sallama
ga shugaban mutanen farko da na karshe, kuma shugaban manzanni.
Ya Allah ka yi salati
ga Annabi Muhammad da iyalan muhammmad kamar yadda ka yi salati ga Ibrahi
da iyalan Ibrahim, Lalle kai mai godiya
ne kuma abin girmamawa.
Ka yi dadin tsira mai
yawa.
Ya Allah ka yarda da sahabbai baki daya. Da tabian da
wadanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar hisabi,
Ya Allah ka yarda da mu
tare da su da baiwanka da karamcinka da rahamarka ya mai tausayin masu jin kai.
Ya Allah ka gafarta
mana abin da muka gabatar da abin da muka jinkirtar da abin da muka boye da
abin da muka bayyana da abin da kai ka fi mu sanin shi a kanmu, kai ne mai
gabatarwa kuma kai ne mai jinkirtarwa ba
abin bautawa da gaskiya sai kai.
Ya Allah ka gafartawa
matattun mu da matattu cikin musulmai,
Ya Allah ka gafartawa
matattun mu da matattu cikin musulmai, da rahamarka ya mafi rahamar masu
rahama.
Ya Allah muna rokonka maaboci
daukaka da girmamawa,
Ya Allah muna rokon ka
da ka dushe wutar fitina mai batarwa
tsakanin musulmai ya ubangijin talikai.
Ya Allah muna rokon ka
da ka dushe wutar fitina mai batarwa
tsakanin musulmai ya ubangijin talikai.
Ya Allah ka hada
zukatar musulmai ka gyara tsakaninsu.
Ya Allah ka azurta mu
da musulmai fahimtar addini, Ya Allah ka azurta mu da musulmai fahimtar addini,
da rahamarka ya mafi tausayin masu tausayi.
Ya Allah ka kyautata
karshenmu a dukkan al'amura, ka kare mu daga walakancin duniya da azabar
lahira, ya maabocin girma da karramawa.
Ya Allah muna neman
tsari daga mummunar abin da aka kaddara, da kuma dariyan makiya, da kuma fadawa
ramin tsiya, da matsanincin bala'I,
Ya Allah ka yaye bakincikin
muminai daga cikin musulmai, Allah ka
biya bashi ga wadanda ake bin bashi cikin musulmai,
Ya Allah ka bada lafiya
ga marasa lafiyan da marasa lafiyan musulmai, Ya Allah ka bada lafiya ga marasa
lafiyanmu, ka taimake mu kan wadanda suka riki gaba da mu, da rahamarka ya mafi
jinkan masu jinkai,
Ya Allah ka kare mu da
zuriyarmu daga iblis da zuriyarsa da shaidanunsa,da rundunarsa da masoyansa, ya
Ubangijin talikai, Ya Allah ka kiyaye mu daga sharrin kawunanmu, da munanan
ayyukanmu, Ya Allah ka kiyaye musulmai da zuriyarsu daga Iblis da zuriyarsa, ya
Ubangijin talikai, da rahamarka ya mafi jinkan masu jinkai,
Ya Allah ka kiyaye
sojojinmu, Ya Allah ka kiyaye sojojinmu, kuma ka datar da su, Ya Allah ka
kiyaye iyakokinmu, Ya Allah ka kiyaye kasarmu daga azzalumai masu ketare iyaka,
da rahamarka ya mafi jinkan masu jinkai, ka kashe fitintinu masu batarwa, ga musulmai ya Ma'abocin daukaka da
karramawa,
Ya Allah ka kiyaye
musulmai daga sharrin makiya musulunci, ya Ubangijin talikai, Ya Allah ka
lalata shirin makiya musulunci, da suke kullawa musulunci da musulmai, ya
maaboci girma da daukaka,
Ya Allah ka kame
sharrin munafukai, domin lalle kana da iko ga dukkan komai,
Ya Allah muna neman
tsarinka daga rarrabuwa da munafunci da munanan dabi'u,
Ya Allah ka jefa tsoron
Allah a zukatanmu, ka tsarkake su kai ne mafi alherin wanda zai tsarkake su,
Ya Allah muna rokon ka
aljanna da abin da zai kusantar da mu gare ta na fadi ko aiki,
Kuma muna neman
tsarinka daga wuta da abin da zai kusantar da mu gare ta na fadi ko aiki,
Ya Allah ka datar da Kadimul
haramaini(shugaban kasar saudiya) cikin abin da ka ke so kuma ka yarda da
shi, Ya Allah ka shiryar da shi zuwa ga shiriyarka, ka sanya aikin shi cikin
yardardarka ya Ubangijin talikai, ya Allah ka taimake shi akan dukkan alheri,
ka datar da shi ra'ayoyinsa ya Ubangijin talikai,
Ya Allah ka datar da
mataimakansa guda biyu cikin abin da akwai alheri da daukaka ga musulunci da
musulmai, ya Ubangijin talikai,
Ya Allah ka karbawa
alhazai ayyukansu kuma ya Allah ka kiyaye su,ya Ubangijin talikai,
Ya Allah ka maida su
garuruwansu cikin aminci da nasara suna halin ka gafarta musu zunubansu, ya
Ubangijin talikai, kuma ka saukake musu al'amuransu.
Ya Allah muna rokonka
ya ma'aboci daraja da daukaka, ka isarwa musulmai sharrin masharrata da
makircin munafukai da mutanen banza, Ya ma'aboci daraja da daukaka.
Ya ku bayin Allah!
(Lalle Allah na yin
umarni da adalci da kyautatawa, da baiwa ma'abocin zumunta, kuma yana hani da
alfahasha da abin da aka ki da zalunci, yana muku wa'azi don ku wa'azantu.)
Nahl 90.
Ku ambaci Allah mai
girma da daukaka
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق