ترجمة الخطبة
اسم المترجم :أمين سعد عبد الله
اللغة : الهوسا
التاريخ : 15-2-1442هـ
Hudubar
jumma'a na masallacin Annabi na shaik Ahmad Bin Dalib 15-2-1442 Ah / 2-10-2020
Hudubar farko
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonSa da
gafararSa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan
ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk
wanda ya batar babu mai shiryar da shi. Na shaida ba abin bautawa da gaskiya
sai Allah, shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi
Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne. tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi da iyalansa da aminci tabbatacce.
(Ya
ku wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu
face kuna musulmai)
(ya
ku mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta
matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji tsoron
Allah da ku ke roko da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance mai
tsaro ne a kan ku.)
(ya
ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara
muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah
biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta mai girma.)
(Ka ce : '' in karanta abin da Ubangiji ku ya haramta .'' wajibi ne akan ku
kada ku yi shirkin kome da shi.
Kuma ga mahaifa biyu
ku (kyautata mu su)
kyautatawa kuma kada ku kashe diyan ku sabo
da talauci , mu ne muke azurtaku ku da su kuma kada ku kusanci abubuwan
alfasha abin da ya bayyana daga gare
ta da abin da ya boyu kada ku kashe rai wanda Allah ya haramta face
da haki wannan ne (Allah) ya yi muku wasiyya da shi tsammaninku kuna
hankalta.
Kada
ku kusanci dukiyar maraya face da wadda
take ita ce mafi kyau har ya kai
ga karfin sa kuma ku cika mudu da sikeli da adalci
ba mu kallafa wa rai face iyawarsa
kuma idan kun fadi magana to ku yi adalci , kuma ko da ya kasance ma'abocin
zumunta ne kuma da alkawarin Allah ku
cika , wannan ne ya mu ku wasiyya da
shi ,
tsammanin ku kuna tunawa .
Kuma
lalle wannan ne tafarki Na yana
madaidaici sai ku bi shi kuma kada ku bi
wasu hanyoyi , su rarraba da ku daga barin hanyaTa , wannan ne Allah ya yi
muku wasiyya da shi tsammanin ku kuna yin takawa
Sa'annan kuma
mun baiwa Musa littafi yana cikakke
bisa ga wanda ya kyautata (hukuncin Allah ) da rarrabewa daki –daki
ga ko wani abu , da shiriya da rahama
tsammanin su suna yin imani da
haduwa da Ubangijin su .
Kuma
wannan littafi ne mun saukar da shi mai
albarka ne sai ku bi shi kuma ku yi
takawa , tsammanin ku ana jin-kanku .
Domin kada ku ce abin sani kawai , an saukar
da littafi akan kungiya biyu daga gabaninmu , kuma lalle ne mu mun kasance daga karatun su hakika
gafilai .
Ko kuwa ku ce '' da dai lalle mu ansaukar da littafi akan mu
hakika da mun kasance mafiya shiryuwa daga gare su , to lalle ne ne wata hujja
bayyananniya daga Ubangijinku ta zo mu ku
da shiriya da rahama .
To
wane ne mafi zalunci daga wanda ya
karyata game da ayoyin Allah kuma ya hinjire daga barin su za mu sakawa wadanda
suke hinjirewa daga barin ayoyin mu da
mugunyar azaba saboda abin da suka
kasance suna yi na hinjirewa.
Shin
suna jiran (wani abu) face dai
mala'iku su je mu su , ko kuwa
Ubangijinka ya je . A ranar da sashin ayoyin Ubangijinka ya ke zuwa , imanin rai wanda bai kasance ya yi imani ba a gabanin
, ko kuwa ya yi
tsiwirwirin wani alheri baya
amfanan sa ka ce :- '' Ku yi jira lalle
ne mu masu jira ne .
Kuma Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bamu labari, labari na gaskiya yana halin mai isar da sako kuma yana mai gaskatawa , (Lalle
Allah ya umarci Yahya dan Zakariyya da kalmomi guda biyar
da ya yi aiki da su kuma da ya umarci banu isra'ila da su
yi aiki da su, kuma lalle shi dinnan ya kusa da ya jinkirta su sai ysa ce :- ''Isa lalle Allah ya umarce ka da kalmomi guda biyar don ka yi aiki da
su kuma ka umarci banu Isra'ila da su yi aiki da su ko dai ka umaarce su ko kuma ni na umarce su sai yahya ya ce ina tsoron kar ka rigani
tashi da su da sai Allah ya kisfe ni ko ya
azabtar da ni sai ya tara banu
Isra'ila a Baitul-Makdis, sai masallaci ya cika
suka zauna akan tudu, sai ya ce lalle Allah ya umurce ni da kalmomi guda
biyar , da na yi aiki da su kuma na umarce ku kuma ku yi aiki da su : - na
farkon su shi ne ku bautawa Allah kada ku hada wani da shi , lalle misalin
wanda ya yi shirka da Allah kamar misalin mutum ne da ya sayi bawa daga kudin
sa shi kadai na azurfa ko zinari,sai ya ce : wannan gida na ne kuma wannan aiki
na ne,to kana yin aiki ka kawo min, to sai ya kasance yana yin aikin kuma yana
kaiwa wanin maigidansa, a cikin ku wa zai yarda da bawansa da ya kasance kamar
wannan? Kuma lalle Allah ya umarce ku da sallah to idan kuna sallah banda
waiwaye, a cin sallah, Allah na kafa
ganinSa ga idon bawansa a cikin sallarsa muddin bai waiga ba, kuma na umarce ku da
azumi, kuma lalle misalin haka shi ne misalin mutumin da ke cikin jama'a tare
da shi akwai jaka a ciki akwai turaren almiski, dukkan su yana burge su ko kuma
kamshinsa na burge kowannen su, Warin
bakin mai azumi ya fi kamshi a wurin Allah fiye da turaren almiski, kuma na umarce ku da sadaka , lalle misalin
haka kamar mutum ne da makiya suka kamashi
suka sa mishi ankwa a hanu zuwa wuyan sa
, suka kuma gabatar da shi don sare wuyan sa , sai ya ce :- '' ni zan
fanshe shi daga gare ku da abu kadan da
mai yawa sai ya fanshi kanshi daga gare su ,
kuma na umarce ku da ku ambaci
Allah, misalin haka ; kamar misalin mutum ne da ya fita makiya suka
bishi a bayan shi da sauri har
sai da ya kai wani katanga mai karfi sai
ya boye kanshi daga gare su to haka nan ne bawa wanda baya kare kansa
daga shaidan sai da ambaton Allah .)
Annabi tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:-
(Nima ina umurtan ku da abubuwa guda biyar Allah ya umurce ni da su ji da
bi , da jahadi da hijira da kuma jama'a domin duk wanda ya kauracewa jama'a
gwargwadon taki to hakika ya kwance kulli na musulunci
daga wuyansa sai dai idan ya dawo
, wanda ya yi da'awa irin da'awan jahiliyya to hakika lalle shi yana cikin
makamashi na jahannama sai wani mutum
ya ce ya Manzon Allah ko da ya yi salla ya yi azumi? Sai ya ce ''e,
ko da ya yi salla ya yi azumi'' ku yi
kira da kiran Allah wanda ya ambace ku da musulmai muminai .)
Ya ku bayin
Allah:
Wannan shi ne
gaskiyan zance kuma shi ne mafi alherin shiryarwa
(Wadancannin
ka su ne wadan da Allah ya shiryar da su , to, ka yi koyi da shiryarwar su , ka
ce ba zan tambaye ku wani lada ba , shi
ba wani abu ba ne sai tunatarwa ga
talikai ).
Ku ji tsoron
Allah gwargwadon iyawan ku .
Ku yi aiki da
abin da aka yi muku wahayi daga
Ubangijin ku za ku rabauta kuma ku yi nasara.
Kuma ku
nemi gafaran Ubangijinku , ku tuba zuwa gare, lalle shi ya
kasance ga masu komowa gare shi mai yawan gafara.
Huduba ta
biyu
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su
tabbata ga shugabanmu Muhammadu da iyalansa da sahabbansa baki daya da wanda ya
bi su da kyautatawa zuwa ranar sakayya.
(Ya
ku wanda suka yi imani ku ji tsoron Ubangijin ku ku tsoraci wata rana wanda mahaifi ba zai fanshi dansa ba , ko da ya fanshi mahaifin sa da wani abu ba
, lalle alkawarin Allah gaskiya ne kada
rayuwar duniya ta rude ku kada wani
mai rudi
ya rude ku daga barin Allah ).
Annabi ya
bayyana abin da ke kulla kaskanci da abin da ke kawo hasken daukaka idan kunyi
cinikayya da riba ku ka riki jelan
shanu kuka yarda da shuki kuka
bar jahadi Allah zai sallada muku kaskanci , sannan ba zai cire shi ba har sai
kun komo addinin ku .
Bayan
haka
Ya ku
mutane:
Ku yi
salati da aminci ga wanda ambatonSo ke
dadada zukata
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق