الجمعة، 23 أكتوبر 2020

WASIYOYIN ALLAH GA ANNABAWA DA SAURAN HALITTU

 

 

 

ترجمة الخطبة

اسم المترجم :أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاريخ : 15-2-1442هـ

 

Hudubar jumma'a na masallacin Annabi na shaik Ahmad Bin Dalib 15-2-1442 Ah / 2-10-2020

 

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonSa da gafararSa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi. Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne. tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da aminci tabbatacce.

(Ya ku wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face kuna musulmai)

(ya ku mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji tsoron Allah da ku ke roko da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance mai tsaro ne a kan ku.)

(ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta mai girma.)

(Ka  ce : '' in karanta  abin da Ubangiji ku  ya haramta .'' wajibi ne akan  ku  kada ku yi shirkin kome da shi.  Kuma ga  mahaifa  biyu  ku (kyautata  mu su) kyautatawa  kuma kada ku kashe diyan ku sabo da talauci , mu ne muke    azurtaku  ku da su kuma kada ku kusanci abubuwan alfasha  abin da ya bayyana  daga gare  ta da abin da ya boyu kada ku kashe rai wanda Allah ya haramta  face  da haki wannan ne (Allah) ya yi muku wasiyya da shi tsammaninku kuna hankalta.

Kada ku kusanci dukiyar maraya  face  da wadda  take ita ce mafi kyau  har ya kai ga karfin  sa  kuma ku cika mudu da sikeli  da adalci  ba mu kallafa wa  rai face  iyawarsa   kuma idan kun fadi magana to ku yi adalci , kuma ko da ya kasance ma'abocin zumunta ne  kuma da alkawarin Allah ku cika , wannan ne ya  mu ku wasiyya da shi  ,  tsammanin ku kuna  tunawa .

Kuma lalle wannan ne  tafarki Na yana madaidaici sai ku bi shi  kuma kada ku bi wasu hanyoyi ,  su rarraba da ku  daga barin hanyaTa , wannan ne Allah ya yi muku wasiyya da shi tsammanin ku kuna yin takawa 

Sa'annan  kuma  mun baiwa Musa littafi yana cikakke  bisa ga wanda ya kyautata (hukuncin Allah ) da rarrabewa  daki –daki  ga ko wani abu , da shiriya da rahama  tsammanin su  suna yin imani da haduwa da Ubangijin su .

Kuma wannan littafi ne  mun saukar da shi mai albarka ne sai ku bi shi  kuma ku yi takawa , tsammanin ku ana jin-kanku .

 Domin kada ku ce abin sani kawai , an saukar da littafi akan kungiya biyu daga gabaninmu , kuma lalle  ne mu mun kasance daga karatun su hakika gafilai .

 Ko kuwa ku ce ''  da dai lalle mu ansaukar da littafi akan mu hakika da mun kasance mafiya shiryuwa daga gare su , to lalle ne ne wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku ta zo mu ku  da shiriya da rahama .

To wane ne mafi zalunci  daga wanda ya karyata game da ayoyin Allah  kuma  ya hinjire daga barin su za mu sakawa wadanda suke hinjirewa daga barin ayoyin mu  da mugunyar azaba saboda  abin da suka kasance suna yi na hinjirewa.

Shin suna jiran (wani abu) face  dai mala'iku  su je mu su , ko kuwa Ubangijinka ya je . A ranar da sashin ayoyin Ubangijinka  ya ke zuwa , imanin rai  wanda bai kasance ya yi imani ba a gabanin ,  ko kuwa  ya yi  tsiwirwirin wani alheri  baya amfanan sa  ka ce :- '' Ku  yi jira lalle  ne mu masu jira ne .

Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bamu labari,  labari na gaskiya yana halin  mai isar da sako kuma yana  mai gaskatawa , (Lalle Allah ya umarci Yahya dan Zakariyya da kalmomi guda  biyar  da ya yi aiki da su kuma da ya umarci banu isra'ila  da  su yi aiki da su, kuma lalle shi dinnan ya kusa da ya jinkirta su  sai ysa ce :- ''Isa  lalle Allah ya umarce  ka da kalmomi guda biyar don ka yi aiki da su  kuma ka  umarci banu Isra'ila da su yi aiki da su  ko dai ka umaarce su ko kuma ni na umarce su  sai yahya ya ce ina tsoron kar ka rigani tashi da su  da sai Allah ya kisfe  ni ko ya  azabtar da ni   sai ya tara banu Isra'ila a Baitul-Makdis, sai masallaci ya cika  suka zauna akan tudu, sai ya ce lalle Allah ya umurce ni da kalmomi guda biyar , da na yi aiki da su kuma na umarce ku kuma ku yi aiki da su : - na farkon su shi ne ku bautawa Allah kada ku hada wani da shi , lalle misalin wanda ya yi shirka da Allah kamar misalin mutum ne da ya sayi bawa daga kudin sa shi kadai na azurfa ko zinari,sai ya ce : wannan gida na ne kuma wannan aiki na ne,to kana yin aiki ka kawo min, to sai ya kasance yana yin aikin kuma yana kaiwa wanin maigidansa, a cikin ku wa zai yarda da bawansa da ya kasance kamar wannan? Kuma lalle Allah ya umarce ku da sallah to idan kuna sallah banda waiwaye, a cin sallah, Allah  na kafa ganinSa ga idon bawansa a cikin sallarsa  muddin bai waiga ba, kuma na umarce ku da azumi, kuma lalle misalin haka shi ne misalin mutumin da ke cikin jama'a tare da shi akwai jaka a ciki akwai turaren almiski, dukkan su yana burge su ko kuma kamshinsa na burge kowannen su,  Warin bakin mai azumi  ya fi kamshi  a wurin Allah fiye da turaren almiski,  kuma na umarce ku da sadaka , lalle misalin haka kamar mutum ne da makiya suka kamashi  suka sa mishi ankwa a hanu zuwa wuyan sa  , suka kuma gabatar da shi don sare wuyan sa , sai ya ce :- '' ni zan fanshe shi daga gare ku  da abu kadan da mai yawa sai ya fanshi kanshi daga gare su ,  kuma na umarce ku da  ku ambaci Allah, misalin haka ; kamar misalin mutum ne da ya fita  makiya suka  bishi a bayan shi da sauri  har sai da ya kai wani katanga mai karfi  sai ya boye kanshi  daga gare su  to haka nan ne bawa wanda baya kare kansa daga shaidan sai da ambaton Allah .)

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- (Nima ina umurtan ku da abubuwa guda biyar Allah ya umurce ni da su  ji  da bi , da  jahadi da hijira  da kuma jama'a  domin duk wanda ya kauracewa jama'a gwargwadon  taki  to hakika ya kwance kulli na  musulunci  daga wuyansa  sai dai idan ya dawo , wanda ya yi da'awa irin da'awan jahiliyya to hakika lalle shi yana cikin makamashi na jahannama   sai wani mutum ya ce ya  Manzon Allah  ko da ya yi salla ya yi azumi? Sai ya ce ''e, ko da ya yi salla ya yi azumi''  ku yi kira da kiran Allah wanda ya ambace ku da musulmai  muminai .)

Ya ku bayin Allah:

Wannan shi ne gaskiyan zance kuma shi ne mafi alherin shiryarwa

(Wadancannin ka su ne wadan da Allah ya shiryar da su , to, ka yi koyi da shiryarwar su , ka ce ba zan tambaye ku wani lada ba   , shi ba wani abu ba ne sai tunatarwa  ga talikai ).

Ku ji tsoron Allah gwargwadon iyawan ku .

Ku yi aiki da abin da aka yi muku wahayi  daga Ubangijin ku  za ku rabauta kuma  ku yi nasara.

Kuma ku nemi  gafaran  Ubangijinku , ku tuba zuwa gare, lalle shi ya kasance ga masu komowa gare shi mai yawan gafara.


 

Huduba ta biyu

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su tabbata ga shugabanmu Muhammadu da iyalansa da sahabbansa baki daya da wanda ya bi su da kyautatawa zuwa ranar sakayya.

(Ya ku wanda suka yi imani ku ji tsoron Ubangijin ku  ku tsoraci wata rana  wanda mahaifi ba zai fanshi dansa ba  , ko da ya fanshi mahaifin sa da wani abu ba , lalle alkawarin Allah  gaskiya ne  kada  rayuwar duniya ta rude ku  kada wani mai  rudi  ya rude ku daga barin Allah ).

Annabi ya bayyana abin da ke kulla kaskanci da abin da ke kawo hasken daukaka  idan kunyi  cinikayya da riba ku ka riki jelan  shanu  kuka yarda da shuki kuka bar jahadi  Allah zai sallada muku  kaskanci , sannan ba zai cire shi ba har sai kun komo addinin ku  .

Bayan haka

Ya ku mutane:

Ku yi salati da aminci  ga wanda ambatonSo ke dadada zukata       

         

      

 


 

 


 

 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق