السبت، 5 ديسمبر 2020

YAWO A GONAN ZUNUBAI

 ترجمة خطبة المسجد النبوي 

الخطيب الشيخ عبد الباري الثبيتي

المترجم : أمين سعد

اللغة : الهوسا

Hudubar Masallacin Annabi Na shaikh Abdul bari Bin Awad  Assubaiti

19/4/1442AH 4/12/2020Ac

Hudubar Farko

 

Da sunan Allah da godiya a gare shi nake farawa, tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah, Shiyarwar Manzon Allah shi ne mabubbuga na alheri, kuma da haske ne mai fantsama da kuma hasken rayuwa : yana tare da kai har a lokacin zamewa da kuskurewa, Buhari ya rawaito daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : lalle wani bawa ya aikata zunubi ko kuma yace ya yi wani zunubi,sai ya ce : ya Ubangiji na yi laifi ko kuma na aikata laifi, ko na aikata wani to ka gafarta mini, sai Ubangijinsa ya ce : ase bawa na ya san yana da Ubangiji yana gafarta zunubai kuma ya yi damka sabo da shi? na gafarta wa bawa na, sannan ya zauna na wani lokaci da Allah ya so sai ya sake aikata zunubi ko ya yi laifi sai ya ce ya Ubangiji na yi zunubi ko na aikata wani laifi to ka gafarta shi, sai ya ce : bawa na ya san yana da Ubangiji yana gafarta zunubi kuma yana damka da shi? na gafartawa bawa na, sai ya zauna na wani lokaci da Allah ya so sai ya  sake aikata zunubi ko ya yi laifi sai ya ce ya Ubangiji na yi zunubi ko na aikata wani laifi to ka gafarta shi a gare ni. Sai yace :Bawa na ya san yana da Ubangiji da yana gafarta zunubi kuma yana damka da shi? Na gafartawa bawa na har sau uku, to ya aikata abin da ya so,)

Wannan hadisi yana hakaito halin bawa game da zunubi da tsarin musulunci wurin gyara halin masu laifi- dukkan mu masu laifi ne – yana bude kofar fatan alheri da kofa ta alhini kamar yadda ake surantawa kowani mai laifi rahamar Allah da ta yalwaci dukkan komai da kyautarSa ga masoyanSa, da tausayinSa ga bayinSa.

Wannan hadisi na farawa ne da fadinsa (Lalle bawa ya yi zunubi)    musulunci na lura da yanayin rayi irin na mutum, wacce ta ke aukawa cikin zunubai, kuma kafa ta zame da ita bisa mantuwa ko wata shubuha ko sha'awa, a dalilin fizga irin na shaidan da batarwarsa: An karbo daga Abu Said daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, lalle iblis ya ce da Ubangijinsa Mabuwayi da Daukaka, na rantse da buwayarka da daukakarka bazan gushe ba ina batar da bani adama muddin rai na gangan jikinsu, sai UbangijinSa Mabuwayi da daukaka ya ce :Na rantse da buwaya ta da Daukaka ta ba zan gushe ba ina gafarta musu muddin suka nemi gafara ta.). Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : na rantse da wanda raina ke hanun shi, ba don kuna laifi ba da Allah ya tafiyar da ku sai ya zo da wasu mutane suna laifi kuma suna neman gafara sai ya gafarta musu.)

     (lalle wani bawa ya aikata zunubi sai yace ya Ubangiji na yi laifi) mutum ya yi ikirari da zunubinsa wannan wani jarumta ne, da nuna ya san lalle ya yi kuskure wannan kankan da kai ne da rusunawa, wannan shine matakin farko na gyaran zuciya da ladabtar da ita, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (wasu sun yi furuci da laifukansu sun cakuda ayyuka na kwarai da wani mummuna, ana fatan Allah ya yafe musu lalle Allah Mai gafara ne Mai jinkai)

A cikin fadin Manzon Allah ga Aisha Allah ya kara yarda a gare ta (Lalle idan bawa ya yi furuci da zunubansa ya kuma tuba sai Allah ya karbi tubansa)

Musulmi na furuci da zunubansa a duniya ya tabbatar da su a lahira, to idan ya aikata haka sai a gafarta masa zunubansa da izinin Ubangijinsa, An karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara yarda a gare su, yace na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Lalle Allah na kusanto da mumini sai ya dora kariyarSa ya suturce shi. Shin ka san zunubi kaza? Shin ka san zunubi kaza? Sai ya ce : e ya Ubangiji, har zuwa lokacin da ya tabbatar da zunubansa ya fahimci cewa ya halaka, sai Allah ya ce na suturtata a gare ka a duniya to a yau na yafe ma ita, sai a bashi littafin shi na kyawawan ayyukansa).  

furuci da zunubai yana da lokacinsa idan ya wuce to sai ukubar zunubai ta sauka gare shi, Allah Madaukakin Sarki ya ce game da 'yan wuta  wadanda basu yi furuci da gajartawansu ba sai bayan sun dandani azabar wuta: (sai suka yi furuci da zunubansu to nesa ga 'yan wutar sa'ira).

  Musulunci ya nusar da musulmi zuwa ga ikirari da furuci da zunubai sai dai ya yi gargadi game da tonon asiri da yada kuskurensa bayan Allah ya suturce shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Dukkan al'uma ta na samun waraka sai masu bayyana sabo, na daga cikin bayyana sabo mutum ya yi wani aiki da dare bayan Allah ya suturta shi, sai ya ce ya wane na aikata kaza da kaza a halin ya kwanaUbangijinsa na suturta shi, sai ya wayi gari yana yaye suturawar Allah a gare shi.)

    

Na daga cikin falalan Allah a gare mu  suturtawan aibi da kiyaye anbato tsakanin halittu. Wani mutum  yace ga daya daga cikin magabata  : ya ya ka wayi gari? Sai yace : tsakanin ni'imomi biyu, ban sani ba wanne ta fi wani zunubai da Allah Mabuwayi da Daukaka ya suturta ta ba wani da zai iya aiba ta ni da su, da kauna da Allah ya jefa cikin zukatan bayi guri na ba zai iya riska ba, Bawa yana cewa na yi laifi ga raina na disan kunya sabo da ya saka da  kyauta mai kyau bisa sabo mummuna,  zuciyarsa na  fito da radadi sabo da nauyin zunubai da tsananin tsoron Allah, wannan yanayi da

Wannan wani Abu ne Mai ratsa jiki da yanayi na ruhi da ke rayye wanda hakan na karfafan imani kuma ya  kan janyo rahamar Ubangiji Mai rahama.

Komowa zuwa ga Allah bayan zunubi wata kyauta ce  daga Allah kuma raya makunnin shiriya ne bayan duhun sabo, Allah Madaukakin Sarki yace:

: ( Lallai wadanda suka ji tsoron Allah Idan wani yanki NA shaidan ya shafe su sai su tuna sai ga shi suna gani irin na basira).

Sau dayawa wani zunubin kan haifar da rayayyen zuciya ga ma'abocin shi da kankan da kai da rusunawa da kuma fiskantar Allah  da gaggawa wurin aikin alheri , sau dayawa sabo  kan haifar da tuba ga ma'abocinsa ,  tuba irin wanda ke daga matsayinsa  ya gyara halayensa , kuma ya kara imanin sa , kuma ya gyara rayuwarsa .

Ya zo a sunna  ingantacce cewa wani sahabi ya aikata wani zunubi mai girma sannan ya tuba  bayansa ,  tuban da  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce game da ita   (Hakika ya yi tuban da  da za a kasa ta tsakanin al'uma da ta ishe su ).

Ya zo a hadisi (Ya Ubangiji na aikata zunubi ka gafarta mini ), (Wanene ke gafarta zunubi   face Allah ):- shi ne wanda tsarki ya tabbata a gare shi ya ke cewa (Ka labartawa bayina lallai ni dinnan mai gafara ne  mai jin kai ) kuma mai cewa wanda ya aikata wani mummuna ko ya zalunci kansa to, zai samu Allah mai gafara kuma mai rahama) . Ya zo a hadisil kudusi .

 (Ya  ku bayi  na lallai ku kun kasance kuna kusakurai a cikin dare da yini  , kuma ni ina gafarta zunubai gaba daya  to ku nemi gafara na , sai in gafarta mu  ku). Ya zo a cikin hadisi (Ya Ubangiji na  na yi zunubi to ka gafarta mini ). To istigfari tarihi ne na Annabawa,  kuma abin nanatawa ne  a bakin salihai, kuma  shi dinnan magani ne na cututtuka ; yana gyaran rayi , ya tsarkake  ta kuma   ya shigar da kyawawa  , shi ne hasken da yake zuwa ga zunubai  sai ya halaka ta ya zo ga zukata marasa lafiya sai ya ingantata, ya zo ga rayuka masu nauyi sakamakon zunubai sai ya  mikar da shi, ya sanya rayuwa ta zama ado,  rayi kuma ya zamana mai sheki Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Kuma ku nemi gafarar Ubangijin ku kuma ku tuba zuwa gare shi , zai jiyar da ku dadi,  jin dadi mai kyau zuwa wani lokaci abin ambato, kuma ya bawa ko wani ma'aboci falala falalarsa ) Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- (Lallai ni ina  neman gafara  zuwa ga Allah kuma in tuba zuwa gare shi  sama da sau saba'in a wuni  ) ya zo  a hadisi  sai Ubangijin shi ya ce :- ( Ase bawa na ya san yana da Ubangiji mai gafarta zunubai , ? kuma yana damka da shi ? to na gafartawa bawana ) (na gafartawa bawa na) :- Kalmace da take kamar wani magani na yanke  wurin waraka bisa ga zukata masu tsoro , da kwarara natsuwa a cikin zukata  masu tsoro; kalma ce da Allah ke tabbatar da tsarkin jiki  da ita, da  kawar  zuciya   da walwala a rayuwa , kuma ta goge zunubanka  ta yaye zuciya  kuma ta saukake alhaki wanda bayanka  ke dauke da shi .

(Na gafartawa bawana ).Fa'ida ne wanda  ya san Ubangijin shi zai  fiskance shi,   ya ji tsoron mahaliccin shi kuma zubowan hawaye kamar tsani ne zuwa gare shi .

 (Na gafartawa bawa na ) Kalma ce  da ke wasa himma na muminai kuma ta karfafi azamar masu zunubai , ta hanyar gaggawa zuwa ga neman gafara da ribatar dama , da neman mafaka a wurin Allah , to zunubbai , suna da mai rahama kuma mai jin kai  zai goge ta , da Allah mai  tausayi da zai gafarta musu .

Wanda ya gafala daga neman gafara bayan aikata sabo , ko kuma bai haura don nemanta ba to  lallai ya wajaba ya tada idanuwan sa daga gyangyadin da yake yi  kuma ya rinka bibiyan  imaninsa , wannan alamace na mutuwar jin bawa na aikata sabo, Allah Madaukakin sarki ya ce :- (kar ku kasance kamar wadanda  suka manta da Allah sai ya mantar da su kawunansu, wadannan sune fasika).

        Mafi girman zunubai shine bawa ya manta cewa shi  yana cikin mantuwa wannan shi ne tarun bala'i , kuma wannan ita ce asara  mai mummunan karshe  Allah  ya yi gargadi ga wanda ya  zalunci kansa  ya bijirewa istigfari, sai yace :  ( Ase ba za su tuba zuwa ga Allah bakuma su nemi gafararSa lalle Allah Mai gafara ne kuma Mai jinkai)

(Allah yace :Na gafartawa bawana  sau uku ya aikata abin da ya so).fadinSa (ya aikata abin da ya so) ba ya nufin umarni ne da ya aikata sabo ba, sai dai ana nufin tun da ya kasance haka a ko yaushe ya yi zunubi zai tuba to  zunubin ba zai cutar da shi ba bayan  tuba, sabo da tuba na goge abin da ke kafinta, sai dai mutum ya kiyaye daga aikata sabo, sabo da yana da yakini bisa ga sabo amma bai da yakini bisa ga gafara, kuma  zain iya rasa dacen tuba.

Kiyayewa daga  zunubai wajibi ne ,; sau dayawa zunubi kan lalata zuciya  ya fusata Ubangiji , kuma ya bakanta hanya , kuma yakan sa saukar da ukuba a doron kasa, a debe albarkan , a kazanta fidira a rarraba dangi .

Yin ko inkula da sabo dabi'a ne abin zargi,   wofantar da halin mai zunubi abu ne mai yanke kauna da cire tsammani , Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Ka ce  ya ku bayi na  wanda suka yi barna bisa kawunan su kar ku yanke kauna daga rahamar Allah , lallai Allah yana gafarta zunubai gaba daya , lallai shi mai gafara ne mai jin kai).

 

HUDUBA TA BIYU

Na daga cikin hakurin Allah  jinkirtawa mai laifi har ya tuba , idan ya koma kuma ya tuba Allah sai ya karbi tubansa , Allah baya gajiya sai dai ku ku gaji ; ya zo a hadisi , cewa:- Shugaban istigfari  shi ne ; bawa ya ce :- (Ya Allah kai ne Ubangiji na ba abin bautawa da gaskiya sai kai , ka halicce ni kuma ni bawanka ne , kuma ina bisa alkawarinka mai karfi da alkawarinka , iya- iyawa na, ina neman tsarinka bisa ga sharrin abin da na aikata , ina komowa a gare ka da ni'imominKa da ke gare ni , kuma ina komowa gare ka da zunubi na –wato yana furuci da shi to, ka gafarta min lallai ba mai gafarta zunubai  sai kai .  

 

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق