ترجمة
خطبة المسجد النبوي للشيخ حسين آل الشيخ
اللغة : الهوسا
المترجم : أمين سعد
التاريخ : 26/4/1442هـ
HUDUBAR
MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH HUSAIN AL-ASSHAIKH 26-4-1442AH 11-12-2021AD
HUDUBAR
FARKO
Cutar da halittu
da sabbaba hakan ba tare da hakki
ba na daga cikin hanya mafi hadari ga mutum.
Wannan ita ce hanya irin ta shaidanu tana tasowa daga sabani da gaba da rikici na kashe juna, tare da rasa ginshiki na
rahama da hali irin na tausayi, da
jinkai.
Lalle cutar
da bayi dabia ce mara kyau abin zargi ne da ta tattaro sifofi daban daban na laifi da abubuwa masu halakarwa.
Lalle sake
linzami ga rai ya cutar da wasu da
harshe ne ko a aikace bai fitowa sai
daga masu raunin imani da biye ma son rai, wanda bata da rai mai yawan umarni
da mummuna da alfahasha.
To ka kare
kanka daga cutar da wani - ya kai musulmi - ka yi wa kanka gargadi daga halaka zaka
kubuta ka rabauta a duniya da lahira Allah Madaukakin Sarki yace : (Wadannan da suke cutar da muminai maza da mata ba da
abin da suka aikata ba suke jifansu hakika sun lafta karya da zunubi mabayyani
ga kansu)
Allah
subhanahu yana cewa : ( Wanda ya aikata kuskure
karami ko babba sannan ya dorawa wanin sa to hakika ya girba karya da zunubi
mabayyani)
Kuma
Manzonmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bayana littafin
Ubangijinsa ya fassara shi yayi bayanin
wadannan ayoyi daki – daki, ta hanya
mutawatiri da aka karbo daga gare shi yana mai gargadi mai tsanani da jan
hankali mai karfi bisa cutar da wani da
zaluntar su da musu shisshigi da wuce iyaka wajen cutar da su, Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Musulmi
dan uwan musulmi ne ba zai zalunce shi ba ba zai rena shi ba ba zai tabar da shi ba) Muslim ne ya rawaito.
Kuma ya
fitar a hadisin hana zama a kan hanya Annabi ya bayyana cewa
(Na daga cikin hakkin hanya kamewa daga cutarwa)
ya kai musulmi
ka kiyaye
kyawawanka ka kare addininka, ka kame daga cutar da waninka, ka kasance kamar
yadda Fudail Bin Iyad yace :(Ba ya halatta a
gare ka ka cutar da kare ko alade ba tare da hakki ba, to ina ga halitta mafi
daukaka )
Matsanancin
hani ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
Game da
cutar da musulmi sai ya ce : (ya tawagan wadanda
suka yi imani da harshensu a halin imani bai fantsama cikin zuciyarsu ba, to
kar ku cutar da musulmai kar ku aibata
su kada ku bibiyi al'aurarsu, to lallai
wanda ya bibiyi al'aurar dan'uwansa musulmi to Allah zai bibiyi al'aurarsa,
kuma duk wanda Allah ya bibiyi al'aurarsa to zai kunyata shi ko da kuwa a
tsakiyar gidansa ne ) Tirmizi ne ya rawaito.
Katada yace
:(Na hore ku da ku nesaci cutar da mumini domin
Allah na kewaye da shi kuma yana iya yin fushi dominsa.)
Ya
kai bawan Allah!
Ka
kubutar da kanka daga cutarwa , ka hana kanka daga zalunci da ketare iyaka zaka
kubuta daga walakanta da halaka.
Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Musulmi
shine wanda musulmai suka kubuta daga sharrin harshensa da hanunsa) Buhari ne
ya rawaito.
Kuma
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Duk wanda
ya yi imani da Allah da ranar lahira to kada ya cutar da makwabcinsa) Buhari ne
ya rawaito. A gun muslim kuma (Ba zai shiga aljanna ba duk wanda makwabcinsa
bai aminta da sharrinsa ba) wato
sharinsa da mugayen halinsa.
Ya 'yan uwa musulmi
A
duniyar yau akwai abin da ake cewa
kafofin sadarwa ta sada zumunta,wanda wasu ke amfani da shi wajen cutar da
musulmai da suka ga mahukuntansu da malamansu da daidaikunsu. Da
al'umominsu da maganganu na fajirci da
yada jita –jita marasa kan gado. To masu yin wannan lalle su tuna cewa : Allah
na dakon su a madakata, kuma lalle mizani ya hada da kyawawa da munana to su kiyaye kada su je ga Ubangijinsu suna
halin Muflisai wadanda suka shiga cikin rudani sun yanke tsammani, - muna
rokon Allah afuwa da waraka-.
Lalle
haramcin cutar da musulmi bai tsaya ga cutar da daidaiku ba, sai dai ya game da
cutar da musulmai cikin maslahohinsu da ya shafi kowa da kowa.da abubuwan
amfaninsu da ake tarayya kamar kayakin
al'uma mallakin gwamnati, na daga tushe na musulunci akwai (Ba cuta
ba cutarwa).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi yana cewa: (ku tsoraci abubuwa biyu masu janyo tsinuwa : wanda ke bahaya a hanyar mutane ko inuwar su).Muslim ne ya
rawaito.
Dabarani ya fitar da
sanadi hasan daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
yace ; wanda ya cutar da musulmai a kan hanyar su to tsinuwa ta tabbata a gare
shi).
Huduba
ta biyu
Ya dan uwa
musulmi !
Ka sabarwa
kanka da kubuta daga cutar da halittu, ka tsarkake ta daga zaluntar wasu a
zahiri da badini, ka sani kubutar da rai
daga shirka da bidiah , da kullin zuci
da hasada da kyashi da muzanta musulmai da zaluntansu na daga cikin sabuba na
kubuta. Kuma sifa ce daga cikin sifofi na 'yan aljanna . Allah Madaukakin sarki
ya ce game da khalilin sa Ibrahim in da ya roki Ubangijinsa game da abin da ya
roki Ubangijinsa da shi,( kada ka kunyatar dani ranar da ake tashin mutane) kuma Allah ya ce (Mun
fitar da abin da yake cikin kirzansu na daga keta, halin kasancewarsu "yan uwa, suna kan gadaje suna kallon
juna ).
Hakika hadisai da
yawa sun inganta wurin bayyana falalan lafiyan zuciya
ga musulmai daga gaba da kiyayya
da nufin muzantawa, na daga ciki akwai mutumin na da ya zo daga cikin
Ansarawa wanda Annabi ya yi mar shaida
da cewa dan aljanna ne, Abdullahi dan Amru Dan As ya bibiyi wannan mutumin har
ya taho ya yi kwanaki uku a gidan mutumin, amma bai ga wani abu na daga
kyawawan ayyukan shi ba irin su tsayuwan dare ba, face in ya tashi cikin dare
daga makwancinsa sai ya ambaci Allah
yayi kabbara har zuwa ya tashi don sallar Asubahi, bai fadi wani abu ba
face alheri, sannan Abdullahi ya bashi labarin abin da Annabi ya fada game da
kissarsa, sai mutumin yace da shi game da ayyukansa shi bai yin wani abu face
abin da ka gani sai dai ni ba na rike wani musulmi a cikin zuciya ta kuma bana
hasada ga wani bisa wani alhairin da Allah ya bashi saiAbdullahi ya ki cewa lale wanan itace
wanda ta kai ka wanan matsayin da ba zamu iya ba.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق