خطبة الشيخ أحمد الطالب
المترجم : أمين سعد
اللغة : الهوسا
التاريخ : 4-5-1442هـ
HUDUBAR
MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH AHMAD –ADDALIB
4-5-1442AH
18-12-2020AD
HUDUBAR
FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimkonSa kuma
muna neman gafararSa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan
ayukanmu duk wanda Allah y shiryar da
shi babu mai batar da shi kuma duk wanda
ya batar da shi babu mai shiryar da shi .
Kuma na
shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai
yake bashi da abokin tarayya , kuma na shiada Annabi Muhammadu bawansa ne kum
ManzonSa ne , kuma zababbenSa ne cikin halittunSa , kuma badadayinSa ne, ya isar da sako kuma ya bada amana ya yi nasiha wa al'uma ya yaye bakin ciki ya yi jahadi don Allah
cancancin jahadi , har mutuwa ta zo mi
shi ,tsira da amincin Allah su tabbata agare shi da iyalan gidansa tsarkaka da kuma matayen sa uwayen muminai da sahabbansa
masu hasken hannaye da kuma wanda
ya bisu da kyautatawa zuwa ranar sakayya .
BAYAN HAKA:
Lallai mafi
gaskiyan zance shi ne littafin Allah , mafi alherin shiriya shi ne shiryarwan
Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , mafi sharrin
al'amura kuma su ne fararrun ta , kuma dukkan fararrun abu bidi'a ne dukkan bidi'a
bata ne, dukkan bata na wuta .
Ya ku
Muminai:
Lallai
Allah ya kira ku ne da suna na imani ,
kuma ya kira ku da ku ji tsoronSa kuma ya umarce ku da ku yiwa kanku
hisabi kafin a yi muku hisabi, dubi zuwa
ga abin da kuka tanada mata kafin komawa
, ya muku gargadi game da manta ta, da kuma
radadin hasarar ta ya sanar da ku
fifikon hali da za a shiga a ranar
komawa gare shi , da girmar
tasirin alkur'ani da an saukar da shi ga duwatsu , ya kuma sanar da ku da
kamalar sunayenSa masu daraja da kaye .
Shi ne Allah wanda zukata
take bauta mi shi bisa kauna da
rusunawa da tsoro, da tsammani da kushu'i , da fata da kuma
firgici .
Shi ne Mai
gaskiya duk abin da ke koma bayan shi
bata ne, kuma mai gushewa, ba abin bautawa da gaskiya sai shi, gani bai iyakance shi,
tunani baya riskan shi, sutura
baya mishi shamaki, sirri baya boyuwa gare shi, da izinin shi ne falaki ya ke
juyawa mai kewayawa, da hukuncinSa da hikimarSa dare kan saba da wuni..
Ma'aboci
rahama mai yalwa mai dorewa, ya daidaita bisa mafi yalwan halittunSa.Da mafi kyaun sunayen sa da mafi yalwan
sifofinSa, (Mai rahama , Ya daidaita a kan Al'arshi. Abin da ya ke a cikin sammai
Nasa ne, da abin da ya ke a cikin kasa da abin da yake a tsakaninsu da abin da ke karkashin turbaya .
Kuma idan ka bayyana da
magana, to, lalle Shi, Yana sanin
asiri da mafi boyuwa . Allah babu
abin bautawa face Shi . Yana da sunaye mafiya
kyau.)
RahamarSa
ta yalwaci halittu wurin samarwa da tattalawa da taimakawa da shiryarwa
da zabarsa ga waliyyanSa, halin shiryarwa da kuma datarwa da tattalawa
har ya kaisu ga matabbatar
rahamarSa da ni'imar aljannarSa, mulki
mai zartuwa na iko a duniya da aikinSa ne da umarninSa , mamallakin sarakuna da
abin da aka mallaka da malakuti da falakoki , yana bada mulki ga wanda ya so ya
kwace ga wanda ya so , ya daukaka wanda
ya so ya kaskantar da wanda ya so, alheri
na hanunSa, kuma shi yana da iko ga dukkan komai.
(UmarninSa, idan Ya yi nufin wani abu , sai Ya ce masa kawai, ''Ka
kasance,'' sai yana kasancewa (kamar yadda Yake nufi).
Ya tsarkaka daga dukkan tawaya sabo da kamala , ya
kubuta daga dukkan aibi sabo da kyau
, ya tsarkake abin da ya so sabo da
albarka da daukakawa, ya amintar da wanda ya so bisa ga wanda ya so sabo da
daukakawa da kaskantarwa.
(makoma), shine
amincin masu tsoro, kuma mafakan masu yankewa don ibada , ba aminci Ya yi imani na da fadinSa cewa shine gaskiya
Mai kasaita, kuma muminai sun yi imani da shi bisa dadin rai a fadi da aiki, saura
halittu kuma suna da'a bisa tilas a karshe ba zaman lafiya sai daga gare shi
kuma zuwa gare shi, rinjayin iko a ilimi
da umarni da shaidawa da karfin
mulki da amfanarwa da cutarwa a sirrace da a bayysane duka na shi ne .
Ya buwaya bisa ga halittunSa wanda tsarki ya tabbata a
gare shi a karfi da kudura da
galaba da hani .
Ya karya garkuwan
halittu bisa umarninSa da haninSa a shari'a da kaddara da karfin mulki , ya karya garkuwan su ta karaya da talauci , da tsanani da cuta
, bisa jin dadi da wadatarwa da gamsarwa
da kuma saukakewa da taimakawa.
Shi ya fi komai girma da daukaka da daraja da
sha'ani da zati da sifa da ayyuka
da iko, to ko wani abu kasa da shi ya ke karami ne abin renarwa ya tsarkaka daga dukkan wani abokin tarayya ,
kuma ya daukaka ba wani abu kwatankwacinSa shi mai ji ne kuma mai gani , ya yi halitta daga babu sai ya bayyana shi ya
halicci iska sai ya sanya mishi wuri ya
suranta a mahaifa sai ya rarrabe , ya kadaita da sunaye , wanda suka kai
kololuwa wurin kyawu a lafazi da ma'ana
, ko wani abu ya yi tasbihi a gare shi
yana mai tsarkake shi da dukkan
harshe .
Allah ya buwaya daga makamanci ko kini, ko kishiya da majibinci da
mataimaki. Ya kyautata halitta a hukunci da hikima, shine Al hakku kuma maganarSa gaskiya ce, hukuncinSa adalci
ne alkalancinSa ne mai rabewa (kat), babu
kusakurai ko zamewa, ba wani abu da zai fita daga iliminSa na aiki ne ko fadi,
Shi Mai hikima ne gwani.(Ya ku wadan da suka yi
imani ku ji tsoron Allah kuma rai ya
dubi abin da ya gabatar domin gobe , kuma ku bi Allah da takawa . Lalle
Allah Mai kididdigewa ne ga abin da
kuke aikatawa.
Kuma kada ku kasance
kamar wadanda suka manta Allah,
Shi kuma Ya mantar da su rayukansu . Wadannan su ne fasikai .
'Yan wuta da 'yan aljanna
basu daidaita , 'yan aljanna su ne masu babban rabo.
Da mun saukar wannan Alkur'ani akan dutse , da
lallai ka ga dutsen yana mai tawali'u mai tsatssagewa sabo da tsoron Allah,
kuma wadancan misalai muna bayyana su ne ga mutane da fatan za su yi tunani .
(Wanda ya saukar da
Alkur'ani) Shi ne Allah wanda babu wani abin bautawa face shi masanin fake da
bayyane , shi ne mai rahama mai jin kai .
Shi ne Allah wanda babu
abin bautawa face shi Mai mulki mai
tsarki , aminci , Mai amintarwa Mai tsarewa Mabuwayi Mai tilastawa Mai kamun kai , tsarki ya tabbata a gare shi
daga abin da suke yi na shirki da shi.
Shi ne Allah mai halitta
mai ginawa Mai surantawa Yana da sunaye
masu kyau , abin da ke a cikin sammai da kasa suna tsarkake shi, kuma shi ne
mabuwayi Mai hikima ).
Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin Alkur'ani mai
girma , ya amfane ni da ku da abin da ke cikin shi na daga ayoyi da ambato mai
hikima, ina fadin wannan maganar tawa
ina neman gafarar Allah wa ni kai na da ku da sauran musulmai daga
dukkan zunubai , kuma ku nemi gafararSa , lallai shi mai gafara ne mai jin kai
.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya isa, tsira da amincin Allah su
tabbata ga Annabi zababbe da iyalansa da
sahabbansan , da wanda suka bi sawunsu .
Bayan haka:
To ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah , lallai mafi
alherin guzuri shi ne tsoron Allah, kuma ku yi riko da igiya mai karfi na
musulunci .
Ku yi salati da aminci…. Ya ku bayin Allah karshe da kuma adu'a.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق