ترجمة خطبة الشيخ حسين آل الشيخ
بالمسجد النبوي
اسم المترجم :أمين سعد
اللغة : الهوسا
التاريخ 29-2-1442هـ
Hudubar
juma'a na masallacin Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi na Shaikh Husain Bin Abdul'Aziz Al - Asshaikh 29-2-1442Ah
Hudubar
farko:
Allah wanda
tsarki ya tabbata a gare shi yana tunatar da mu sunnar rayuwa da yadda yake
tafiyar da ita a cikin al'umomi, sai wanda shaninSa ya buwaya yace :( Ba mu tura wani manzo ba cikin wata alkariya face mun riki
mutanenta da tsanani da cuta ko za su kankan da kai)
ABA'SA: shine tsanani da kunci
irin na rayuwa,
ADDARRA:Dukkan cuta da mawuyacin hali cikin sabuba na duniya.
Sai Allah
ya bayyana hikimar faruwan hakan da sabubansa, don bayi su komo ga Ubangijinsu
su rusunawa Mahaliccinsu, su dawo zuwa ga Allah abin bautansu su bar abin da
zai fusata shi Allah Mabuwayi da daukaka ta hanyar tuba ta gaskiya zuwa gare
shi, da lizimtar da'a gare shi, da rusunawa umarninSa da tafiya bisa tafarkin
sharia.
Na daga
cikin hikimomi na jarabawa da ma duk wani abu da ke samun mutum a rayuwa na
tsanani da wahala, da abin da ke faruwa a gare shi na cuta a jikinsa da cututtuka.
Na daga
cikin hikimar haka halittu su koma ga Ubangijinsu, su mika-wuya zuwa ga
umarninSa tsarki ya tabbata a gare shi su
kama hanya zuwa ga shiriyarsu su gargadu daga bata da musu, ko sandararrun
zukata za su lausasa, su waazantu su gyaru su shiryu su riki shiriya su kama
hanya ta daidai,
Allah
Madaukakin sarki ya ce : ( kuma hakika mun tura zuwa ga al'umomi da suke gabaninka sai
muka rike su da tsanani da cuta ko za su
kankan da kai).
Ya wajaba
ga bayi su yiwa kansu hisabi a halin suna ganin jarabawowi daya – bayan daya su
koma da gaskiya zuwa ga addinin Allah, su sabunta tuba ta gaskiya kuma su nemi
gafarar Allah da gaske, su sake sabunta alkawari na tafiya bisa tafarki
mikakke. Na daga cikin mafi girman musibu
jarabawowi su zo su wuce zukata basu tausasa ba, gabbai ba su koma ga
Ubangijinsu ba. Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ina
ma da lokacin da tsananinmu ya je musu sun kankan da kai sai da zukatansu ta
kekashe kuma shaidan ya kawata musu abin da suka kasance suna aikatawa)
Mafi girman
musibu kuma mafi munin sifa ta shakawa, a samu jarabawowi amma masu gafala suna
dogewa cikin gafalarsu, masu demuwa suna baccinsu da wasanninsu da ayyukan sabo,
mabarnata sun bace cikin barnansu da laifukansu.
Nu'man Bin
Bashir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :(
Lalle Halaka dukkan halaka shine ka yi sabo a lokacin jarrabawa ) Ibnu Abi
Shaiba ne ya rawaito
Allah
Subhanahu wa Ta'ala yana mai gargadi game da sha'anin kafurai masu musu, (Hakika mun rike su da azaba ba su kaskantar da kawunan su ba
gaUbangijin su ba su kasance suna rusunawa ba) ai mun jarrabe su da
musibu daban daban da tsanani ba su rusuna ba ba su yi kushu'i ba ba su kwantar
da kai ba zahiri da badini sai dai ma sun doge cikin batan su da barnan su.
Ya ku bayin
Allah:
Lallai
akwai laruran tuba mai tsanani da bukatuwa zuwa ga yiwa kai hisabi mai karfi,
Allah Madaukakin sarki ya ce (mai Allah zai yi da
azabtar da ku idan kuka gode ku ka yi imani? Allah ya kasance mai godiya kuma
masani)
Musibu ba
za su iya su koma ni'ima ba , tsanani da cuta su koma yalwa da yayewan bakin
ciki sai ta hanyar tuban bayi zuwa ga Ubangijin
su da komawa zuwa ga mahaliccin su da haka ne Allah Mabuwayi zai jikan su ya yi
ni'ima a gare su ya dauke bala'i da suke cikin da abin da ya faru da su , lallai Allah yana
jarabta bayin sa da tsanani da musibu da laifuka domin ya kwadaitar da su zuwa
ga yin da'a gare shi kuma su dawo zuwa ga bangaren shi .
Allah
Madaukakin sarki ya ce:(barna ta bayyana a doron
kasa da kuma kogi sakamakon abinda hannayen mutane suka haifar don ya dandana
musu wani sashi na abunda suka aikata ko za su komo).
Allah
Subhanahu wa Ta'ala ya ce:(za mu dandana musu na
daga azaba na kusa banda azaba mai girma ko za su juyo).
Allah Subhanahu
wa ta'ala ya na cewa (muka jarrabe su da kyawawa da
kuma munana ko za su juyo) , Malaman tarihi sun ambata cewa: a
shekara ta dari bakwai da arba'in da tara wata annoba ta auku a Misra da Siriya
(sham) wanda a dalilin ta mutane da yawa suka rasa rayukansu sai mutane suka
hadu a masallatayya suka kankan da kai ga Ubangijinsu suka tuba daga zunubansu
suka fuskanci Allah da nau'uka na sadakoki har zuwa lokacin gushewan bala'in
cikin gaggawa,
Duk wanda
Allah ya nufe shi da alheri kuma ya datar da shi sai su riki fadawa cikin
musibu kamar wani abu ne na gargadi da wa'azi da kuma tunatarwa , Allah
Madaukakin sarki ya ce (Hakika mun riki fir'auna da
jama'an sa da tsanani da fari da tawaya na daga 'ya'yan itace ko za su wa'azan
tu su tuna) ko su wa'azantu domin tsanani na ratsa zukata kuma tana
kwadaitar da ita cikin abin da ke wurin Allah Mabuwayi da kuma komawa zuwa gare
shi.
Ya ku bayi
Allah
Babu samun
abunda ake kwadayi rayi ta ke sha'awa babu tsira daga abunda ake tsoro zuciya
ta ke kin shi sai ta hanyan tuba na gaskiya zuwa ga Allah Mabuwayi da daukaka,
Allah madaukakin sarki ya ce:(ku tuba zuwa ga Allah
gaba daya ya ku musulmai ko za ku rabauta)
Rahamar
Allah ga halittunSa wanda ita ta ke yaye bakin ciki kuma ta gusar da wahalhalu
ba ta tabbatuwa sai ta hanyan da'a ga Allah kuma da tsoron shi da bin
shari'arSa da tafiya akan sunnan manzon Sa tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi, Allah Madaukakin sarki ya ce: (ku tsaida
sallah ku bada zakka ku yi da'a wa manzo ko za ku samu rahama ko za aji kan ku),
Allah Madaukakin sarki ya ke cewa:(duk wanda ya ji
tsoron Allah to Allah zai sama masa mafita)
Allah
Mabuwayi da daukaka ya ke cewa (duk wanda ya ji
tsoron Allah zai saukake mishi daga cikin al'amuransa)
To ku koma
zuwa ga Allah Subhanahu wa Ta'ala ku gyara fadin ku da ayyukan ku ku lizimci
abubuwa da su ke na hani da umarni za ku samu shiriya kuma ku rabauta, Allah
Madaukakin sarki ya ce:(duk wanda ya aikata aiki na
kwarai na miji ne ko mace a halin yana mumini to za mu raya shi rayuwa daddada
mu sakanya mishi da ladan shi mafi kyan abinda ya ke aikatawa).
Huduba ta biyu:
A duk
lokacinda al'umma suka tabbatar da imani tabbatarwa ta gaskiya ta zahiri da ta
badini a kuma duk lokacinda suka kasance akan manhaji tafarki na Allah a dukkan
al'amuran su da sha'anonin su da kai -komon su a rayuwan su to Allah zai bude
musu albarkatu su rayu cikin yalwa da rayuwa daddada da kuma jin dadi wanda ba
wani gurbata ko bakin ciki da zai cakudu da shi
Allah
Madaukakin sarki ya ce:(da ace mutanen alkarya sun
yi imani sun ji tsoro da mun bude musu albarkatoci daga sama da kasa sai dai
sun karyata sai muka rike su da abinda suka kasance suna aikatawa).
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق