ترجمة الخطبة بالمسجد النبوي
اسم المترجم :أمين سعد
اللغة : الهوسا
التاريخ 22-2-1442هـ
Hudubar
juma'a na masallacin Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi na Shaikh Aliyu Bin Abdurrahman Alhuzaifi 22-2-1442Ah
Hudubar
farko:
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin kasa da sammai,mai daga darajoji,ya yi
umarni da biyayya sabo da abin da ke ciki na alheri da albarka, ya yi hani daga
abubuwan da aka haramta, sabo da abin da ke cikin su na shu'umci da sharri da
halaka.
Ina kyautata yabo ga Ubamgiji na kuma
ina gode mishi bisa ni'imominSa da ba mai iyakance su sai Shi, wadanda muka
sani da wadanda bamu sani ba, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi
kadai yake ba shi da abokin tarayya, ya dayanta da sunaye kyawawa da sifofi
mafi kamala, na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma
ManzonSa ne, mafi alherin halittu wanda aka karfafe shi da mu'ujizozi Ya Allah
ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad
da iyalansa da sahabbansa masu tsere zuwa ga alheri, Bayan haka.
To ku ji
tsoron Allah ta hanyan kusantan shi, ku kusanta zuwa gare shi da abinda zai yardar
da shi da kauracewa abinda zai fusata shi ,kuma ya cutar da shi, abin mamaki da
kyakkyawan karshe irin na masu tsoron Allah, abun mamaki da munin karshe na
masu sabawa Allah mabarnata, to ku kasance daga cikin wadanda suka bi tafarkin
tsira kar ku kasance daga cikin wadanda suka bi hanyoyi na masu sabo, Allah
madaukakin sarki ya ce (duk wanda yayiwa Allah da'a
da Manzon Sa to wadannan suna tare da wadanda Allah ya yi ni'ima a gare su na
daga annabawa da siddikai da shuhada'ada salihan bayi madalla da abokan zama irin
wadannan) (wannan falala ne daga Allah
kuma Allah ya isa masani) kuma Allah Madaukakin sarki ya ce:( Duk wanda ya
ke sabawa Allah da manzonSa to lallai yanada wutan jahannama yana dawwama a
ciki har abada)
Ya ku
musulmai:
Lallai
Allah ya halicci wannan duniya kuma ya sanya abubuwan da duk mukallafi ke
bukata a ciki na daga arziki ne da jin dadi ne da kawa da dukiya ne da
dabbobi da waninsu , kuma ya saukake
wannan duniya ga halittu ya horar da su
duka gaba daya domin maslahohin halittu da amfanin su da kuma tashi tsayuwan
rayuwansu zuwa ga lokaci abin ambato a wurin Allah wanda ba mai iya tsallake
shi, Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ke cewa (shi ne
wanda ya sanya muku doron kasa a kaskance to ku yi tafiya a yankin ta ku ci
daaga arzikin Sa kuma zuwa gare shi za a tashe ku), Allah Madaukakin
sarki ya ce (ba mu halicci sammai da kasa ba da
abunda ke tsakanin su face da gaskiya kuma da wani ajali a ambato wadanda suka
kafurce suna masu kauda kai daga abunda aka musu gargadi) Allah
Subhanahu wa ta'ala ya ke cewa:(dabbobin gida ya
halicce su ne don ku a ciki akwai dif'un da kuma abun amfani daga ciki kuke ci
kuma kunada kawa a ciki lokacinda kuke yammaci da kuma lokacin da kuke safiya)
(kuma tsana daukan abubuwanku masu nauyi zuwa ga
wasu garurruwa wanda baza ku iya ba sai da wahalan rayi, lallai ubangijin ku
mai tausayi ne mai jin kai) (dawakai kuma
da alfadura da jakuna don ku hausu kuma da ado , yana halittan abinda baku sani
ba) Allah Subhanahu wa ta'ala
ya ke cewa (kuma ya horar a gare ku abunda ke cikin
sammai da abunda ke cikin kasa domin gaba daya daga gare shi , lallai a cikin
haka akwai a'ayoyi ga mutane da su ke tinani), Allah Mai tsarki ya
ke cewa (Allah ya sanya a gare ku daga kawunan ku
mataye, ya sanya muku kuma daga matayen ku 'ya'ya da kuma jikoki, kuma ya
azurta ku daga dadada, shin da bata za su yi imani kuma su kafurcewa ni'imomin
Allah?).
Allah
Subhanahu wa Ta'ala ya ke cewa:(in za ku kidanya
ni'imomin Allah ba za ku iya iyakance su ba), Allah ya halicci wannan
duniyan cikin kamalarSa da kyansa da kuma cikansa sosai da abubuwa da suke na
tsaida rayuwa dukkanin su yayi ne ga wanda suke doron kasa da kuma yawan
abubuwan amfaninsa da kuma nau'ukan su da kuma horewan shi da sabuba na
wanzuwan rayuwa da kuma habakan ta ,Ubangijinmu ya bamu labari Mabuwayi da
daukaka cewa bai halicci wannan duniyan ba don wasa, kuma bai barsu haka ba
kuma bai yishi haka banza ba, Allah mai tsarki ya ke cewa:(ban halicci sama da kasa ba da abunda ke tsakanin su da sunan
wasa) (da a ce mun so mu rike shi wasa da
mun rike shi daga gare mu in mun kasance masu yin hakan ne , sai dai muna hurga
gaskiya akan bata domin ya rusa shi sai gashi ya gushe , kuna da bone na daga
abinda kuke siffantawa), Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ke cewa (hakika mun halicci a saman kutara'ika guda bakwai , bamu
kasance bisa ga halittan mu gafalallu ba) Mai tsarki ya ce (ba mu halicci sama da kasa ba da abinda ke tsakanin su haka
kawai da sunan bata a banza ba sai dai wannan zaton wadanda suke kafurai ne to
bone ya tabbata ga wadanda suka kafurce na daga wuta) Allah
subhanahu ya ke cewa (shin ko kun zaci mun halicce
ku wasa na kuma ba za ku koma zuwa gare mu ba? To Allah ya daukaka daga wannan
mai mulki na gaskiya, ba abun bautawa da gaskiya sai shi ubangijin al'arshi mai
girma) Allah Madaukakin sarki ya ce (Allah
shi ne wanda ya daga sammai ba tare da gofwanni ba , sannan ya daidaita bisa
al'arshi kuma ya horar da rana da wata duk suna gudu zuwa ga wani ajali abun
ambato, yana tafiyar da al'amura yana rarrabe a'ayoyi , ko zaku sakankance game
da haduwa da uban gijin ku) .
Allah
Subhanahu wa ta'ala ya ce:(ba wani abu a doron kasa
na daga dabba face Allah ne mai azurtata kuma ya san matabbatan ta kuma da inda
ta ke a'adanan ta dukkan haka yana cikin littafin bayyananne)
Allah
madaukakin sarki ya ce:(masani ne na gaibu kuma baya
kwace masa ko da na kwayan zarra abunda ke sama ne ko a kasa ko mafi kankanta
akan haka ko mafi girma face yana littafi bayyananne) Allah
Madaukaki ya ce (rayi bata kasance da ta mutu ba
face da izinin Allah abu ne rubutacce mai lokaci ) Allah bai wakilta
halitta ba zuwa ga wanin Sa sai dai ya halicci duniya ne wanda ake gani da
gaskiya shi ne tauhidi da kuma da'a duka , dukkanin su da gyara da gyaruwa ga
doron kasa , Allah Madaukakin sarki ya ce:(ya ku
mutane, ku bautawa ubangijin ku wanda ya halicce ku da wadanda suke kafin ku ko
zaku ji tsoron Allah wanda y sanya muku doron kasa mai shinfida sama kuma gini.
Ya saukar da ruwa daga sama sai ya fitar da 'ya'yan itace da shi arziki a gare
ku,to kada ku sanya wa Allah kishiya a halin kuna sane. )
Allah
Madaukakin sarki ya ce : (Ban halicci aljanu da
mutane ba face don su bauta min, ba na bukatar arziki daga gare su, kuma ba na
bukatar da su ciyar da ni lalle Allah Shine Mai azurtawa Ma'aboci karfi)
Hakika
Allah ya turo manzanni, na karshen su shine shugabanmu Muhammad tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi, don ya yi gyara a doron kasa na daga
da'a da tsarkake ta daga shirka da
abubuwa masu halakarwa,( Hakika mun turo ga kowace al'uma Manzo da a bautawa Allah
kuma a nesaci dagutu ) kuma ya ce Allah Subhanahu wa ta''ala ya ce:
(kada ku yi barna a doron kasa bayan manzanni sun
gyarata da littatafan da aka saukar):(hakika
mun turo cikin ko wace al'umma manzo da su bautawa Allah kuma su nisan ci dagutu)
Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ce:(kada ku yi barna a
doron kasa bayan an gyarata) bayan manzanni sun gyarata da
litttatafai wadanda aka saukar
Hakika Allah ya umarni manzanni amincin Allah su
tabbata a gare su da su ji dadi da
abinda ya halatta musu na rayuwan duniya daga tsarkaka kuma su dimanci da'a wa Allah wanda kasa ata
gyaruwa sai da ita .
Allah
Madaukakin sarki ya ce: (ya ku manzanni ku ci na
daga tsarkaka (dadada) kuma ku yi aiki na kwarai lallai ni din nan bisa ga
abinda ku ke aikatawa ina sane), mabiya manzanni su ne muminai
wadanda aka yiwa umarni suyi koyi da shi a fadin sa (ya ku wadanda suka yi imani ku ci daga tsarkaka din da muka azurta ku da
shi kuma ku godewa Allah in kun kasance shi kadai ku ke bautawa)
Allah Subhanahu wa ta'ala ya ce (ka ce wa ya haramta
kawa na Allah? Wanda ya fitar ga bayin sa da kuma tsarkaka na daga arziki? Ka
ce: su din nan ga wadanda suka yi imani ne a rayuwan duniya kuma ya kebanta
ranar alkiyama gare su)
manzanni amincin Allah su tabbata a gare su da mabiyan su muminai sun
sanya wannan duniyan gaba daya wuri ne da kuma lokaci ne na ayyukan da'a da
kuma gyara sun sanya shi wato kamar wurin tsallakawa ne da ayyukan alheri da
kuma neman aljanna da kuma ayyuka na kwarai amfanin su duka gaba daya yana
komawa ne zuwa ga mutum, amfanar da halittu ta hanyan tashi da rukunnan
musulunci da sauran ayyuka na da'a yana bin wannan rukunnan ne, ya kai musulmi
kada ka raina ayyukan da'a komin kankantan su na daga wani abu, baka sani ba a
ciki wani aikin ne zai shigar da kai
aljanna kuma ya tsiratar da kai daga wuta.
An karbo
daga Jabir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: daga Annabi tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce: (kar ka rena
wani abu na daga aikin alheri lallai daga cikin abubuwa na ma'arufi ka hadu da
dan uwanka fiska a sake) Bukari bda Muslim ne suka rawaito.
An karbo
daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce(wani mutumi
yana tafiya a wani hanya sai ya samu
wani reshi na kaya akan hanya sai ya dauke shi ya ja shi baya sai Allah ya gode
mishi kuma ya gafarta mishi)
Bukari da
Muslim ne suka rawaito.
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda
a gare shi ya ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa : (wata mace mazinaciya taga kare a wata rana yana shawagi a
wurin rijiya yana lallage da harshen sa saboda tsananinkishi sai ta cire huffin
ta ta cika shi da ruwa ta bashi ta bashi ya sha sai aka gafarta mata)
Bukari da Muslim ne suka rawaito, Allah Madaukakin sarki ya ce:(lallai Allah baya zalunta ko na kwatankwacin kwayan zarra in
har ta kasance kyakkyawa ce zai ribanya ta ne kuma ya bada daga gare shi lada
mai yawa).
Muminai sun
riki wannan duniya wani zamani ne kuma wuri ne domin ayyukan da'a, amma wadanda
basu yi imani da Allah ba da ranar lahira suka kafirce to sun riki wannan
duniya ne wani lokaci ne da kuma wani wuri ne na su na bin soye soyen rayuka na
daga abubuwan da aka haramta da bin kyalakyalai masu gushewa da kuma aikata
ayyukan sabo mafi girman laifi shi ne shirka da Allah, wato bawa ya riki wani
abu da ya ke halittacce yana kira shi yana rokon shi yana fata daga gare shi
kuma ya dogara gare shi kuma yana neman taimakonsa kuma yana neman a'agajinsa
ya daga mishi bukatun shi da abubuwan da ya ke nema, kuma yana ragaba zuwa gare
shi wurin arziki ko kuma nasara ko kuma ya rika daga murya da shi wurin neman
yaye tsanani da bakin ciki wannan shi ne shirkan da Allah ba ya gafartawa,
tsarki su tabbata a gare shi sai dai ta hanyar tuba, Allah Subhanahu wa Ta'ala
ya ce:(lallai Allah baya gafarta da ahada shi da
wani amma yana gafarta abinda ke kma bayan haka ga wanda ya so duk wanda ya hada Allah da wani to hakika ya bata batya wanda
ya ke nesa), Allah Madaukakin sarki ya ce: (lallai sha'anin shi duk
wanda ya ke shirka da Allah to Allah ya haramta a gare shi aljanna kuma makoman
sa wuta ne kuma azzalumai basu da mataimaka), wanda zasu biyo bayan
wannan su ne manyan zunubbai suna cikin girman laifuka ne masu girma bayan
shirka gwargwadon barna zunubi da kuma gwargwadon sabawa, bawa ke zaluntan
ransa tsakanin shi da kuma Allah ya tuba kuma daga gare su Allah sai ya gafarta
mishi amma abubuwa da su ke na abinda aka zalunci bayi to Allah baya gafartawa har sai utun ya
maidawa wanda aka zalunta hakkin sa kafun ranarda babu dirhami ko dinari sai
dai kawai kyawawa ne da za a bawa wanda aka zalunta na daga kyawawantun wanda
ya yi zaluncin idan har kyawawan sa sun
kare sai a dauka daga laifukan wancan wanda aka zalunta a jefa mishi shi wanda
ya yi zaluncin sannan a hurga shi a cikin wuta, an karbo daga Abu Huraira Allah
ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce:(duk wanda ya kasance yanada wani
abu da ya zalunci wanin shi na daga dan uwan shi na daga mutuncin shi ne ko
wani abu nashi to ya warware tun kafun wannan ranan ya zo, ranan da zai kasance
babu dinari ko dirhami, idan mutum ya kAsance yanada ayyuka na kwarai sai a
dauka daga gare shi gwargwadon wanda ya zalunta, in kuma ya kasance yanada
kyawawa sai a dauki daga kyawawan sa in ya kasance baida kyawawa sai a dauka
daga munanan sahibin nasa sai a dora mishi) Muslim ne ya rawaito da
Tirmizi.
An karbo
daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Annabi tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce: (lallai ku
bada hakkoki zuwa ga ma'abotan su tun kafun ranan alkiyama, ranan da za a yi
kisasi daga akuya mara kaho daga akuya mai kaho wanda ta soketa da shi)
Muslim ne ya rawaito.
Da mutum
zai kubuta daga nauyin hakkoki a wurin abubuwa na zalunci to da muminai sun
kubuta masu biyayya daga neman hakkoki na zalunci a tsakanin su , an karbo daga
Abu Sa'id Alah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce: (za a kubutar da
muminai daga wuta bayan sun tsallake siradi sai a kange su a wani wuri da ake
cewa kandara tsakanin wuta da aljanna sai a musu kisasi sashin su a yiwa sashi
kisasi daga abunda wani ya zalunci wani wanda ya kasance tsakanin su a duniya
har zuwa lokacin da aka tsarkake aka tsabtace su sai a musu izini da su shiga aljanna na rantse da wanda raina ke
wurin Sa zan same su sun fi shiryuwa zuwa ga matsayi a aljanna da matsayin da
na kasance a gare shi a duniya) Bukari ne ya rawaito.
Ya kai
musulmi: na horeka da zunubbai ko da a idonka kanana ne, domin lallai a wurin
Allah abu ne mai girma, an karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara yarda a gare su daga
Annabi tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi ya ce: (wata mace ta shiga wuta a sakamakon kyanwa wanda ta daure
ta bata sake ta ba ta ci daga ciyayin kasa) Bukari da Muslim n suka
rawaito.
Manzon
Allah tasira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (na horeku daga abubuwa na raina zunubbai domin su din nan
su suke taruwa ga bawa Har su halaka shi), Allah Madaukakin
sarki ya ce: (ya ku bayiNa wadanda suka yi barna wa
kawunan su kada ku yanke tsammani daga kawunan ku daga rahamar Allah lallai
Allah na gafarta zunubbai gaba daya lallai shi din nan mai gafara ne kuma mai
jin kai)(kuma ku koma zuwa ga ubangijin
ku ku mika mishi wuya tun kafun azaba ya zo sannan baza ku yi nasara ba)
(ku bi daga abunda ya fi kyau cikin abunda aka
saukar muku na daga ubangijin ku tun kafin azaba ya zo bagatatan a halin ba ku
sani ba)
Allah ya sa
min albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma
Huduba ta
biyu:
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin talikai majibincin masu takawa
mawadaci daga halittunSa da'an masu da'a baya amfanar da shi haka nan kuma
sabon masu sabo baya cutar da shi ina kyautata yabo ga ubangijina kuma ina gode
mishi bisa ga ni'imomin Shi da waninshi ba ya iya kidinye su wanda muka sani da
wanda ba mu sani ba, na shaida ba abun bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai
ya ke ba shi da abokin tarauyya , mulki nashi ne wanda ya ke ma'aboci gaskiya
kuma bayyananne na shaida Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad bawanSa ne kuma
Manzon Sa ne amuntacce ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga
bawanKa kuma manzonKa Muhammad da 'yalan shi da sahabban shi baki daya .
Bayan haka:
Ku ji
tsoron Allah cancancin takawa ku yi riko da igiya mai arfi na musulunci .
Ya ku
musulmai:
Lallai na
daga cikin abinda ke kankare zunubai kuma ya ke kara kyawawa kuma ya ke
tsarkake ayyuka shi ne ayyuka na kwarai kuma ya ke goge da ke cikin ayyuka na
kusanci abinda ke koran shaidanu kuma shi ne ambaton Allah Mabuwayi da daukaka
daga dukkan hali.
Allah
Madaukakin sarki ya ce: (ya ku wadanda suka yi imani
ku ambaci Allah ambato mai yawa kuma ku yi tasbihi a gare shi safiya da maraice),
an karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: wani ya
zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai ya ce: ya
Manzon Allah: shari'o'i na musulunci sun
min yawa to da wanne zan yi riko dunkulalle? Sai Annabi tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ke cewa: (kada harshen
ka ya gushe yana danye daga ambaton Allah)Ahmad ne ya rawaito da
Tirmizi.
Ya ku bayin
Allah lallai Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku wadanda suka yi
imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق