الجمعة، 23 أكتوبر 2020

DUNIYA HIKIMOMI DA HUKUNCE HUKUNCE

 

ترجمة الخطبة بالمسجد النبوي

اسم المترجم :أمين سعد

اللغة : الهوسا

التاريخ 22-2-1442هـ

Hudubar juma'a  na  masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na Shaikh Aliyu Bin Abdurrahman Alhuzaifi 22-2-1442Ah

Hudubar farko:

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin kasa da sammai,mai daga darajoji,ya yi umarni da biyayya sabo da abin da ke ciki na alheri da albarka, ya yi hani daga abubuwan da aka haramta, sabo da abin da ke cikin su na shu'umci da sharri da halaka.

          Ina kyautata yabo ga Ubamgiji na kuma ina gode mishi bisa ni'imominSa da ba mai iyakance su sai Shi, wadanda muka sani da wadanda bamu sani ba, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ya dayanta da sunaye kyawawa da sifofi mafi kamala, na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, mafi alherin halittu wanda aka karfafe shi da mu'ujizozi Ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalansa da sahabbansa masu tsere zuwa ga alheri, Bayan haka.    

To ku ji tsoron Allah ta hanyan kusantan shi, ku kusanta zuwa gare shi da abinda zai yardar da shi da kauracewa abinda zai fusata shi ,kuma ya cutar da shi, abin mamaki da kyakkyawan karshe irin na masu tsoron Allah, abun mamaki da munin karshe na masu sabawa Allah mabarnata, to ku kasance daga cikin wadanda suka bi tafarkin tsira kar ku kasance daga cikin wadanda suka bi hanyoyi na masu sabo, Allah madaukakin sarki ya ce (duk wanda yayiwa Allah da'a da Manzon Sa to wadannan suna tare da wadanda Allah ya yi ni'ima a gare su na daga annabawa da siddikai da shuhada'ada salihan bayi madalla da abokan zama irin wadannan) (wannan falala ne daga Allah kuma Allah ya isa masani) kuma Allah Madaukakin sarki ya ce:( Duk wanda ya ke sabawa Allah da manzonSa to lallai yanada wutan jahannama yana dawwama a ciki har abada)

Ya ku musulmai:

Lallai Allah ya halicci wannan duniya kuma ya sanya abubuwan da duk mukallafi ke bukata a ciki na daga arziki ne da jin dadi ne da kawa da dukiya ne da dabbobi  da waninsu , kuma ya saukake wannan  duniya ga halittu ya horar da su duka gaba daya domin maslahohin halittu da amfanin su da kuma tashi tsayuwan rayuwansu zuwa ga lokaci abin ambato a wurin Allah wanda ba mai iya tsallake shi, Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ke cewa (shi ne wanda ya sanya muku doron kasa a kaskance to ku yi tafiya a yankin ta ku ci daaga arzikin Sa kuma zuwa gare shi za a tashe ku), Allah Madaukakin sarki ya ce (ba mu halicci sammai da kasa ba da abunda ke tsakanin su face da gaskiya kuma da wani ajali a ambato wadanda suka kafurce suna masu kauda kai daga abunda aka musu gargadi) Allah Subhanahu wa ta'ala ya ke cewa:(dabbobin gida ya halicce su ne don ku a ciki akwai dif'un da kuma abun amfani daga ciki kuke ci kuma kunada kawa a ciki lokacinda kuke yammaci da kuma lokacin da kuke safiya) (kuma tsana daukan abubuwanku masu nauyi zuwa ga wasu garurruwa wanda baza ku iya ba sai da wahalan rayi, lallai ubangijin ku mai tausayi ne mai jin kai) (dawakai kuma da alfadura da jakuna don ku hausu kuma da ado , yana halittan abinda baku sani ba)  Allah Subhanahu wa ta'ala ya ke cewa (kuma ya horar a gare ku abunda ke cikin sammai da abunda ke cikin kasa domin gaba daya daga gare shi , lallai a cikin haka akwai a'ayoyi ga mutane da su ke tinani), Allah Mai tsarki ya ke cewa (Allah ya sanya a gare ku daga kawunan ku mataye, ya sanya muku kuma daga matayen ku 'ya'ya da kuma jikoki, kuma ya azurta ku daga dadada, shin da bata za su yi imani kuma su kafurcewa ni'imomin Allah?).

Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ke cewa:(in za ku kidanya ni'imomin Allah ba za ku iya iyakance su ba), Allah ya halicci wannan duniyan cikin kamalarSa da kyansa da kuma cikansa sosai da abubuwa da suke na tsaida rayuwa dukkanin su yayi ne ga wanda suke doron kasa da kuma yawan abubuwan amfaninsa da kuma nau'ukan su da kuma horewan shi da sabuba na wanzuwan rayuwa da kuma habakan ta ,Ubangijinmu ya bamu labari Mabuwayi da daukaka cewa bai halicci wannan duniyan ba don wasa, kuma bai barsu haka ba kuma bai yishi haka banza ba, Allah mai tsarki ya ke cewa:(ban halicci sama da kasa ba da abunda ke tsakanin su da sunan wasa) (da a ce mun so mu rike shi wasa da mun rike shi daga gare mu in mun kasance masu yin hakan ne , sai dai muna hurga gaskiya akan bata domin ya rusa shi sai gashi ya gushe , kuna da bone na daga abinda kuke siffantawa), Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ke cewa (hakika mun halicci a saman kutara'ika guda bakwai , bamu kasance bisa ga halittan mu gafalallu ba) Mai tsarki ya ce (ba mu halicci sama da kasa ba da abinda ke tsakanin su haka kawai da sunan bata a banza ba sai dai wannan zaton wadanda suke kafurai ne to bone ya tabbata ga wadanda suka kafurce na daga wuta) Allah subhanahu ya ke cewa (shin ko kun zaci mun halicce ku wasa na kuma ba za ku koma zuwa gare mu ba? To Allah ya daukaka daga wannan mai mulki na gaskiya, ba abun bautawa da gaskiya sai shi ubangijin al'arshi mai girma) Allah Madaukakin sarki ya ce (Allah shi ne wanda ya daga sammai ba tare da gofwanni ba , sannan ya daidaita bisa al'arshi kuma ya horar da rana da wata duk suna gudu zuwa ga wani ajali abun ambato, yana tafiyar da al'amura yana rarrabe a'ayoyi , ko zaku sakankance game da haduwa da uban gijin ku) .

Allah Subhanahu wa ta'ala ya ce:(ba wani abu a doron kasa na daga dabba face Allah ne mai azurtata kuma ya san matabbatan ta kuma da inda ta ke a'adanan ta dukkan haka yana cikin littafin bayyananne)

Allah madaukakin sarki ya ce:(masani ne na gaibu kuma baya kwace masa ko da na kwayan zarra abunda ke sama ne ko a kasa ko mafi kankanta akan haka ko mafi girma face yana littafi bayyananne) Allah Madaukaki ya ce (rayi bata kasance da ta mutu ba face da izinin Allah abu ne rubutacce mai lokaci ) Allah bai wakilta halitta ba zuwa ga wanin Sa sai dai ya halicci duniya ne wanda ake gani da gaskiya shi ne tauhidi da kuma da'a duka , dukkanin su da gyara da gyaruwa ga doron kasa , Allah Madaukakin sarki ya ce:(ya ku mutane, ku bautawa ubangijin ku wanda ya halicce ku da wadanda suke kafin ku ko zaku ji tsoron Allah wanda y sanya muku doron kasa mai shinfida sama kuma gini. Ya saukar da ruwa daga sama sai ya fitar da 'ya'yan itace da shi arziki a gare ku,to kada ku sanya wa Allah kishiya a halin kuna sane. )

Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ban halicci aljanu da mutane ba face don su bauta min, ba na bukatar arziki daga gare su, kuma ba na bukatar da su ciyar da ni lalle Allah Shine Mai azurtawa Ma'aboci karfi)

Hakika Allah ya turo manzanni, na karshen su shine shugabanmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, don ya yi gyara a doron kasa na daga da'a  da tsarkake ta daga shirka da abubuwa masu halakarwa,(  Hakika mun turo ga kowace al'uma Manzo da a bautawa Allah kuma a nesaci dagutu ) kuma ya ce Allah Subhanahu wa ta''ala ya ce: (kada ku yi barna a doron kasa bayan manzanni sun gyarata da littatafan da aka saukar):(hakika mun turo cikin ko wace al'umma manzo da su bautawa Allah kuma su nisan ci dagutu) Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ce:(kada ku yi barna a doron kasa bayan an gyarata) bayan manzanni sun gyarata da litttatafai wadanda aka saukar

Hakika  Allah ya umarni manzanni amincin Allah su tabbata a gare su  da su ji dadi da abinda ya halatta musu na rayuwan duniya daga tsarkaka  kuma su dimanci da'a wa Allah wanda kasa ata gyaruwa sai da ita .

Allah Madaukakin sarki ya ce: (ya ku manzanni ku ci na daga tsarkaka (dadada) kuma ku yi aiki na kwarai lallai ni din nan bisa ga abinda ku ke aikatawa ina sane), mabiya manzanni su ne muminai wadanda aka yiwa umarni suyi koyi da shi a fadin sa (ya ku wadanda suka yi imani ku ci daga tsarkaka din da muka azurta ku da shi kuma ku godewa Allah in kun kasance shi kadai ku ke bautawa) Allah Subhanahu wa ta'ala ya ce (ka ce wa ya haramta kawa na Allah? Wanda ya fitar ga bayin sa da kuma tsarkaka na daga arziki? Ka ce: su din nan ga wadanda suka yi imani ne a rayuwan duniya kuma ya kebanta ranar alkiyama gare su)   manzanni amincin Allah su tabbata a gare su da mabiyan su muminai sun sanya wannan duniyan gaba daya wuri ne da kuma lokaci ne na ayyukan da'a da kuma gyara sun sanya shi wato kamar wurin tsallakawa ne da ayyukan alheri da kuma neman aljanna da kuma ayyuka na kwarai amfanin su duka gaba daya yana komawa ne zuwa ga mutum, amfanar da halittu ta hanyan tashi da rukunnan musulunci da sauran ayyuka na da'a yana bin wannan rukunnan ne, ya kai musulmi kada ka raina ayyukan da'a komin kankantan su na daga wani abu, baka sani ba a ciki wani aikin ne zai shigar da kai  aljanna kuma ya tsiratar da kai daga wuta.

An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (kar ka rena wani abu na daga aikin alheri lallai daga cikin abubuwa na ma'arufi ka hadu da dan uwanka fiska a sake) Bukari bda Muslim ne suka rawaito.

An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce(wani mutumi yana tafiya a wani  hanya sai ya samu wani reshi na kaya akan hanya sai ya dauke shi ya ja shi baya sai Allah ya gode mishi kuma ya gafarta mishi)

Bukari da Muslim ne suka rawaito.

 An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa : (wata mace mazinaciya taga kare a wata rana yana shawagi a wurin rijiya yana lallage da harshen sa saboda tsananinkishi sai ta cire huffin ta ta cika shi da ruwa ta bashi ta bashi ya sha sai aka gafarta mata) Bukari da Muslim ne suka rawaito, Allah Madaukakin sarki ya ce:(lallai Allah baya zalunta ko na kwatankwacin kwayan zarra in har ta kasance kyakkyawa ce zai ribanya ta ne kuma ya bada daga gare shi lada mai yawa).

Muminai sun riki wannan duniya wani zamani ne kuma wuri ne domin ayyukan da'a, amma wadanda basu yi imani da Allah ba da ranar lahira suka kafirce to sun riki wannan duniya ne wani lokaci ne da kuma wani wuri ne na su na bin soye soyen rayuka na daga abubuwan da aka haramta da bin kyalakyalai masu gushewa da kuma aikata ayyukan sabo mafi girman laifi shi ne shirka da Allah, wato bawa ya riki wani abu da ya ke halittacce yana kira shi yana rokon shi yana fata daga gare shi kuma ya dogara gare shi kuma yana neman taimakonsa kuma yana neman a'agajinsa ya daga mishi bukatun shi da abubuwan da ya ke nema, kuma yana ragaba zuwa gare shi wurin arziki ko kuma nasara ko kuma ya rika daga murya da shi wurin neman yaye tsanani da bakin ciki wannan shi ne shirkan da Allah ba ya gafartawa, tsarki su tabbata a gare shi sai dai ta hanyar tuba, Allah Subhanahu wa Ta'ala ya ce:(lallai Allah baya gafarta da ahada shi da wani amma yana gafarta abinda ke kma bayan haka ga wanda ya so duk wanda ya hada Allah da wani to hakika ya bata batya wanda ya ke nesa), Allah Madaukakin sarki ya ce: (lallai sha'anin shi duk wanda ya ke shirka da Allah to Allah ya haramta a gare shi aljanna kuma makoman sa wuta ne kuma azzalumai basu da mataimaka), wanda zasu biyo bayan wannan su ne manyan zunubbai suna cikin girman laifuka ne masu girma bayan shirka gwargwadon barna zunubi da kuma gwargwadon sabawa, bawa ke zaluntan ransa tsakanin shi da kuma Allah ya tuba kuma daga gare su Allah sai ya gafarta mishi amma abubuwa da su ke na abinda aka zalunci  bayi to Allah baya gafartawa har sai utun ya maidawa wanda aka zalunta hakkin sa kafun ranarda babu dirhami ko dinari sai dai kawai kyawawa ne da za a bawa wanda aka zalunta na daga kyawawantun wanda ya yi zaluncin  idan har kyawawan sa sun kare sai a dauka daga laifukan wancan wanda aka zalunta a jefa mishi shi wanda ya yi zaluncin sannan a hurga shi a cikin wuta, an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(duk wanda ya kasance yanada wani abu da ya zalunci wanin shi na daga dan uwan shi na daga mutuncin shi ne ko wani abu nashi to ya warware tun kafun wannan ranan ya zo, ranan da zai kasance babu dinari ko dirhami, idan mutum ya kAsance yanada ayyuka na kwarai sai a dauka daga gare shi gwargwadon wanda ya zalunta, in kuma ya kasance yanada kyawawa sai a dauki daga kyawawan sa in ya kasance baida kyawawa sai a dauka daga munanan sahibin nasa sai a dora mishi) Muslim ne ya rawaito da Tirmizi.

An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (lallai ku bada hakkoki zuwa ga ma'abotan su tun kafun ranan alkiyama, ranan da za a yi kisasi daga akuya mara kaho daga akuya mai kaho wanda ta soketa da shi) Muslim ne ya rawaito.

Da mutum zai kubuta daga nauyin hakkoki a wurin abubuwa na zalunci to da muminai sun kubuta masu biyayya daga neman hakkoki na zalunci a tsakanin su , an karbo daga Abu Sa'id Alah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (za a kubutar da muminai daga wuta bayan sun tsallake siradi sai a kange su a wani wuri da ake cewa kandara tsakanin wuta da aljanna sai a musu kisasi sashin su a yiwa sashi kisasi daga abunda wani ya zalunci wani wanda ya kasance tsakanin su a duniya har zuwa lokacin da aka tsarkake aka tsabtace su sai a musu izini da  su shiga aljanna na rantse da wanda raina ke wurin Sa zan same su sun fi shiryuwa zuwa ga matsayi a aljanna da matsayin da na kasance a gare shi a duniya) Bukari ne ya rawaito.

Ya kai musulmi: na horeka da zunubbai ko da a idonka kanana ne, domin lallai a wurin Allah abu ne mai girma, an karbo daga Abdullahi dan  Umar Allah ya kara yarda a gare su daga Annabi tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi ya ce: (wata mace ta shiga wuta a sakamakon kyanwa wanda ta daure ta bata sake ta ba ta ci daga ciyayin kasa) Bukari da Muslim n suka rawaito.

Manzon Allah tasira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (na horeku daga abubuwa na raina zunubbai domin su din nan su suke taruwa ga bawa Har su halaka shi), Allah Madaukakin sarki ya ce: (ya ku bayiNa wadanda suka yi barna wa kawunan su kada ku yanke tsammani daga kawunan ku daga rahamar Allah lallai Allah na gafarta zunubbai gaba daya lallai shi din nan mai gafara ne kuma mai jin kai)(kuma ku koma zuwa ga ubangijin ku ku mika mishi wuya tun kafun azaba ya zo sannan baza ku yi nasara ba) (ku bi daga abunda ya fi kyau cikin abunda aka saukar muku na daga ubangijin ku tun kafin azaba ya zo bagatatan a halin ba ku sani ba)

Allah ya sa min albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma

 

Huduba ta biyu:

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin talikai majibincin masu takawa mawadaci daga halittunSa da'an masu da'a baya amfanar da shi haka nan kuma sabon masu sabo baya cutar da shi ina kyautata yabo ga ubangijina kuma ina gode mishi bisa ga ni'imomin Shi da waninshi ba ya iya kidinye su wanda muka sani da wanda ba mu sani ba, na shaida ba abun bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarauyya , mulki nashi ne wanda ya ke ma'aboci gaskiya kuma bayyananne na shaida Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad bawanSa ne kuma Manzon Sa ne amuntacce ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanKa kuma manzonKa Muhammad da 'yalan shi da sahabban shi baki daya .

Bayan haka:

Ku ji tsoron Allah cancancin takawa ku yi riko da igiya mai arfi na musulunci .

Ya ku musulmai:

Lallai na daga cikin abinda ke kankare zunubai kuma ya ke kara kyawawa kuma ya ke tsarkake ayyuka shi ne ayyuka na kwarai kuma ya ke goge da ke cikin ayyuka na kusanci abinda ke koran shaidanu kuma shi ne ambaton Allah Mabuwayi da daukaka daga dukkan hali.

Allah Madaukakin sarki ya ce: (ya ku wadanda suka yi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa kuma ku yi tasbihi a gare shi safiya da maraice), an karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: wani ya zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai ya ce: ya Manzon Allah: shari'o'i  na musulunci sun min yawa to da wanne zan yi riko dunkulalle? Sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa: (kada harshen ka ya gushe yana danye daga ambaton Allah)Ahmad ne ya rawaito da Tirmizi.

Ya ku bayin Allah lallai Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce.

  

 

 

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق