الجمعة، 23 أكتوبر 2020

ABUBUWAN LURA DAGA SURATUL DUHA

 

ترجمة خطبة الشيخ عبد الباري الثبيتي

  بالمسجد النبوي

اسم المترجم :أمين سعد

اللغة : الهوسا

التاريخ 6-3-1442هـ

Hudubar juma'a  na  masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na Shaikh AbdulBari Bin  Awad Assubaiti 6-3-1442Ah

Hudubar farko:

 

Sura ce da ta sauka a zuciyar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai ta debe masa kewa ta share masa radadin da yake ji ta wanke masa zafin da ya ke ji, ta kuma jefa masa natsuwa a cikin zuciyarsa.

Wahayi ya katse wa Manzon Allah na wani lokaci, sai masu dako na dako da masu shakku na jefa shakku sai Allah ya saukar (Allah na rantsuwa da walaha. Da dare idan duhu ya lullube shi. Ubangijinka bai barka ba kuma bai kaurace ma ba).

   Wannan Sura ta fito da matsayin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da kaunar Allah  da ya ke masa  da kusancin shi da falalar sa ,  sabo da ya kaunaci Allah da gaske  sai Allah  ya  kaunace shi   (Ubangijinka bai barka ba kuma bai kyale ka ba)

 ta yaya Ubangijin shi zai juya mishi baya  zai juyawa zuciyan da ya ke samun nitsuwa da shi  da ganawa da shi yakan ji dadi da ayoyinSa da maganganunsa wallahi ba zai yi nesa ba da bawanda da ya allaka zuciyan shi da shi  sai  ma ya kusanto shi ya manna shi a jiki ya daukaka sha'anin sa ,  ya bashi matsayi

Wannan ayan tana magana ne da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi  kuma tana magana ne da dukkan wani  mumini da mumina   wanda ya yi gaskiya tare  da Allah  ana jefa a cikin zuciya   wani shu'uri na kaunan Allah  da kuma kusancin shi  da kuma ma'iyyarSa  wato kasancewa tare da shi kuma tana kwararo wani abu na  sa'ada da yarda da kuma  jin dadi Allah madaukakin sarki yana cewa:- a cikin hadisin kudusi (BawaNa ba zai gushe ba yana kusanta na  da nafilfilu har sai na kaunace shi  idan na so shi sai in  kasance jin shi da yake ji da shi  da ganin sa da yake gani da shi  da hanunsa da  yake damka da shi da kafan sa  da yake  tafiya da ita  , idan ya roke ni zan bashi  idan ya tambaye ni zan bashi  in kuma ya tambaye ni zan biya mishi bukatanshi.)

(Kuma lallai lahira  ya fi ma alheri akan duniya ), lallai wato karshen al'amari a gare ka shi ya fi ma alheri  akan farkon shi  manzon Allah tsira da  amincin Allah su tabbata a gare shi bai gushe ba yana haurawa darajoji  na daukaka  Allah yana karfafan shi  da addinin sa kuma yana taimakon shi  yana datar da shi a kowani  halayen shi  har zuwa lokacin da ya rasu  a kowani rana da yake shudewa na rayuwarsa  Allah yana kara mishi daukaka  da buwaya  a cikin shi  kuma ya taimake shi da taimako akan taimako  da karfafa akan karfafa  har lokacin da ya ga mutane sun shiga addinin Allah tawaga-tawaga , to hakika ya gaskata  Allah  Allah ya yiawa AnnabinSa gaskiyan Alkawari da ya mi shi  ta inda ya bude masa garin makka  ya yada da'awarsa a gabashin duniya  da yammacin ta  lallai lahira ya fi  duniya , lallai karshe ita tafi  alheri akan farko  a dukkan abin da Allah ya  kaddara  lallai bawa yana mu'amala ne  tare da Ubangiji mai karamci  yana wa bayinSa jarabawa sannan kuma  ya yaye musu bakin ciki  al'amarin ya kare zuwa ga yalwa  dukkan wata hala da ta jinkirta daga cikin yanayin  ka to, lallai  tana da falala bisa ga halin da ya gabta (Kuma lallai lahira  ya fi ma alheri akan duniya )     

  Allah ya san cewa ManzonSa ya sancewa lahira ta fi  duniya a gare shi  Allah madaukakin sarki yana cewa  na tattalawa bayiNa salihai abin da idanuwa basu taba gani ba  kunne ba ta taba ji ba  zuciyan wani dan adam bai taba  hararo shi ba  shi ne kuma ya ke cewa wurin  da ake ajiye bulala a aljanna ya fi alheri akan duniya da abin da ke cikin ta  an bawa Annabi zabi  a rashin lafiyar shi  tsakanin  da  ya rayu a duniya iya yanda zai  rayu, da  kuma abin da ya ke wurin Allah  sai ya zabi abin da ya ke wurin Allah  duk wanda yake da hankali  na shiriya ya  san  cewa  lahira ya fi alheri akan duniya , lallai duniya  mai karewa ne  kuma  dukkan wanda  ya ke doronta kuma zai kare  sai ya rage  fiskan Ubangijin ka kadai  zai wanzu ma'aboci daukaka  da karamci  wannan  ma'ana  na asali  yana tunkuda musulmi  zuwa ga ya kyautata imanin shi ya  ya gyara  ayukan sa  ya tsarkake  rayuwarsa kuma  ya habaka ayukansa a lokutansa (Ubangijinka zai baka har sai ka yarda)  ana karanta wannan aya  a dukkan zamani  da suka shude  ana kuma kawata  kunnuwa da shi  zuciya na raurawa tana hakaito  matsayin da ke lullube  yana kuma hakaito matsayin wanda aka bawa  da kuma matsayin wanda ya ke  bayarwa  wanda akan kanshi yana da ma'ana  da madalulin sa  kyauta ne , madalla da irin wannan  kyauta  daga mai bada kyauta  wanda baya saba alkawari  ba kuma wani falala bayan kyautar sa  ba wani kari  akan ladanSa kuma ba  iyaka bisa ga ni'imarSa,

 Allah ya bashi wani matsayi madaukaki  da sammai madaukaka ya kusantar da shi ga Annabawa gaba daya  ya sanya shi cikamakin Annabawa  ya sanya al'umarsa mafificiyar al'umu ya sanya littafinshi da ya saukar zuwa gare shi shi ne mafi darajan   littatafai  ya sanya shari'arsa kuma shi ne mafi alherin shari'o'i  ya daukaka ma'abotansa ya daraja matayensa  kuma ya bashi na daga falala wanda ba za a iya iyakance shi ba  Allah madaukakin sarki ya ce tsarki ya tabbata  ga wanda in ya ga dama zai sanya maka wanda  ya fi haka alheri  daga gare shi gonakai wanda  koramai na gudana a karkashin sa  kuma ya sanya maka benaye  ya bashi ceto  ga mutanen da suke a maukif  har lokacin da Allah zai yi hukunci a tsakanin su   da ceto kuma ga ma'abota Aljanna  har su samu su shiga .

Yarda da kyautan Allah  ga wanda ya fiskanto  zuwa ga Allah  sai Ubangijinsa ya so shi , wanda Ubangijin shi ya so shi kuma zai kusanto da shi  ya kawo shi kusa  kuma ya yardar da shi ,  ya bashi nitsuwa ta zuci  da kwanciyar hankali,  har zuciya da cikakken natsuwa da  hutu  ya gusar mishi da bakin ciki da bacin rai  amma kuma abin da ya ke lahira  yana cikin rayuwa ne yardajjiya to ki koma zuwa ga Ubangijin ki kina yardajjiya  abin yarda , kina mai yarda kuma abin yarda (ashe Ubangijinka bai same ka maraya ba kuma  ya baka mafaka  ya same ka batacce kuma baka da shiriya kuma ya shiryar da kai , ya same ka kana talaka kuma ya wadata ka)  to kamar yanda ya bashi mafaka yana matsayin  maraya  kuma ya shiryar da shi da wahayi to da wannan kuma ya wadatar da shi da dukkan wani abin da ya sha-gabansa  a dukkan matakai na rayuwarsa   Allah ya wadata shi da tarbiyanSa, tarbiyan Abu –Dalib  ya yin da aka samu  rashin Abu-Dalib  sai Allah ya wadata shi da  dukiyan Khadija , yayin da aka rasa wannan sai Allah ya  wadata shi da dukiyan Abubakar , yayin da aka rasa hakan sai Allah ya  umarce shi da hijira  ya wadata shi da taimakon  mutanen madina .

A cikin wadannan ni'imomi  wanda Allah ya yi baiwada shi ga Annabin sa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  idan mai bakin- ciki  yayi lura  da ita  sai ya gusar mishi da musiba , ko kuma ya samu wasu matsaltsalu a kan hanya da  wasu musibu  to lallai wannan za ta bude mishi kofofi ne  da suke na fatan alheri  da kuma wani gun shiga  abun sha mai  dadi na alhini  kuma ya cika shi da azama da aiki  kuma ya kiraye shi zuwa ga ya yarda duk wani yanke tsammani  ko yanke kauna  ya yada duk wani abin da ke ga zai kawo mishi rashin nasara  ya samu sakankancewa  a dukkan tafiyan sa da rayuwarsa  sabo da gamayyan rahamar Allah  da kuma kyautanSa da bayida iyaka amma shi maraya kada a fi karfin shi  amma kuma matambayi ba a tsawatar mishi  wadannan ayoyi suna isar da ma'ana ne na shiryayyen rayuwa wanda   aka assasa ta akwai daukan nauyi da tausayawa kuma kira ne ga dukkan wanda Allah ya yiwa ni'ima da matsayi bayan da ya kasance ba a sanshi ba , ya  bashi mafaka bayan maraya ne  ya wadata shi bayan talaka ne  ya daga sha'anin sa bayan  ya kaskanta da ya godewa ni'imar Allah .

Kada ka yi rinjaye kada ka fi karfin maraya kada ka walakanta shi ka tsawata  mishi sai dai ka  kyautata mishi ka tausasa mishi  kar ka kasance ga masu rauni kana  mai jabbaranci kada ka yi girman kai kada ka zama mai zafin rai  kana mai maida miskinai  ta hanyar rahama tausasawa da amma ga ni'imar Ubangijinka to ka bada labari .

 

Huduba ta biyu

 rayuwa domin ka ga ni'imomin Allah a gare ka a da can baka kasance komai ba  har  zuwa lokacin da ka wayi gari kana wani abu abin abin ambato ni'imar Allah a ko wani kai komo  da numfasawa ni'imar samarwa da ni'imar shiryarwa da ni'imar lafiya da zaman lafiya da ji da gani da dukiya da zuriya da ni'iman bacci da shiryarwa da fadaka ko farka da ni'imar Allah tun daga kanka har zuwa tafin kafan ka , (A kawunan ku ashe ba za ku yi lura ba) ka yi lura da ni'imomin Allah cikin abin da ya hore maka na daga rana da wata da koramai da koguna da itatuwa da dabbobi da dare da yini ka yi lura  ka yi lura bisa ga ni'imomin Allah ka labarta da su bisa ga hanyoyi na tabbatarwa da rusunawa da yarda  da kuma wafa'I domin wannan ni'ima su dauwama falalan su kuma  ya dauwama , domin ka rika jin wannan ni'ima din tare da kai domin ka rika jin falala na wannan ni'ima , kuma ka san hakkinSa sai halinka ya canza daga gafala zuwa ga mai da'a daga kuma mai gajartawa zuwa ga mai godiya ka godewa Allah a wurin fadi da aiki, a zuciya da gabbai sai Allah ya dada hore maka ni'imomin cikin abinda Allah ya shar'anta maka  .

(Ina rantsuwa da hantsi, da dare a lokacin da ya rufe(da duhunsa)Ubangijin ka bai yi maka bankwana ba kuma bai ki ka ba , kuma   lalle ta karshe ce  mafi alheri a gare ka daga ta farko , kuma lalle ne Ubangijinka zai yi ta baka kyauta har sai ka yarda , ashe bai same ka maraya ba sa'annan ya yi maka makoma , kuma ya same ka ba kada shari'a  sai ya shiryar da kai  kuma ya same ka matalauci sai ya wadata ka  sabo da haka , amma maraya to, kada ka rinjaye shi  , kuma amma mai tambaya kada ka yi masa tsawa , kuma amma ni'imar Ubangijinka sai ka fada (domin godiya )).            

 


 


 

 


 

 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 


 

 

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق