ترجمة الخطبة بالمسجد
النبوي
اسم المترجم :أمين سعد
اللغة : الهوسا
التاريخ 8-2-1442هـ
Hudubar juma'a
na masallacin Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi na Shaikh Abdullah Abuaijan 8-2-1442.AH /25-9-2020AD
Hudubar farko:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode
masa kuma muna neman taimakonSa kuma muna neman gafararSa muna neman tsarin
Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu,duk wanda Allah ya shiryar da
shi to babu mai batar da shi duk wanda ya batar da shi babu mai shiryar da shi,
.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya
wanzuwa na shi ne da yabo kuma gudananar
da al'amura a hanun shi ya ke
da hukunci , yana tafiyar da al'amura zuwa doron kasa
daga sama yana aikata abin da ya so
, ba abin da za ku so sai idan Allah ya
so .
Na shida Annabi Muhammadu bawqnSa ne kuma ManzonSa ne
, ya
isar da sako kuma ya sauke amana ya yi nasiha wa al'uma ya yi jahadi a tafarkin
Allah cancancin jahadi , har mutuwa ta zo mi shi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi da iyalan shi da
sahabbaan shi baki daya .
Bayan haka:
Lallai littafin Allah shi ne zance mafi mikewa , shi
ne kuma dalili mafi shiryarwa
kuma sunnan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi shi ne mafi alherin manhaji , kuma mafi
adalcin tafarki kuma abin koyi
kyakkyawa a wurin bi kuma bata da kauce hanya na cikin kirkiran
bidi'a .
Ya ku bayin Allah
:
Ku ji tsoron Allah a cikin abin da ya yi umarni , ku hanu daga abin da ya hana kuma ya
tsawatar (Ya ku wadan da kuka yi imani ku ji tsoron
allah ku fadi maganan da yake na daidai
zai gyara mu ku ayukan ku kuma ya gafarta mu ku zunuban ku , duk wanda
ya yiwa Allah da Mnzon sa da'a to hakika ya rabauta , rabauta mai girma)
Ya ku jama'ar Musulmi:
Masallatayya
dakuna ne na Allah kuma mafi soyuwan
bigire a gare shi an tanada su ne don bauta da sallah
da ambaton Allah zuwa gare su wanda ya yi imani
da shi kuma ya jibince shi ya ke komawa (Lalle
mai raya masallatan Sa shi ne wanda y a
yi imani da Allah da ranar lahira , ya
tsaida sallah ya bada zakka bai ji tsoron wani ba face Allah , ya wuci wadancan su
kasance cikin shiryayyu .)
Ba bu mai raya su sai muminai na gaskiya , Allah
Madaukakin sarki ya ce :(Mushrikai ba su kasance
da su raya masallatan Allah ba)
:(cikin wasu gidaje da Allah ya yi umarni
da daukaka kuma a ambaci sunanSa cikin su, wasu mazaje suna tasbihi a gare shi
safiya da maraice, kasuwanci bai shagaltar da su ko ciniki daga ambaton Allah
da tsaida sallah da bada zakka suna tsoron wata ranar da zukata da ganai ke
juyawa)
Allah ya yi alkawarin narkon azaba ga wanda ya yi saddu ga tafarkin su ya bata wuraren kiran sallan su da mihraban
su sai ya ce:- (Wa ya fi zalunci sama da
wanda ya hana masallatayyan Allah
da a ambaci sunanSa a cikin
su kuma yayi aiki wurin rusa su wadannan bai kasance ba a gare su da su shige
su face suna halin tsoro , suna da
wulakanci anan duniya a lahira kuma suna da azaba mai girma )
Ya ku bayin Allah :
Masallatai dakunan Allah ne , su ne mafifitan gurare da
bigire, su ne makwancin wanda ke bautawa Ubangijinsa ya yi biyayya.
Daga wuraren kiran sallan su ne ake maimaita shahadan tauhidi ko wace
rana bisa kunnuwa; na shaida ba abin
bautawa da gaskiya sai Allah na shaida
Annabi Muhammadu Manzon Allah ne.
Daga wuraren kiran sallanta ne ake maimaita yekuwa zuwa
ga sallah kinshiki na musulunci ,
na biyu daga cikin rukunan sa masu girma , ku gaggauto
zuwa ga sallah, ku gaggauto zuwa ga sallah , ku gaggauto zuwa ga babban rabo .
Daga mihirabansu
ne da mimbarorin su sako na imani
ya taso , ya bude zukata da kunnuwa , kuma ya goge duhun shirka da gumaka .
Su ne farkon makarantu na tarbiya da ilmantarwa a
musulunci, tawaga irin na sahabbai masu
daraja daga nan su ka fito , sai suka kasance mafi cancantan mutane a ilimi
da aiki.
Su ne farkon
tawagan da aka kafa mimbari na
da'awa , sai suka yada musulunci dukkan
duniya da da'awa da jahadi da halaye .
Ya jama'ar musulmi:
Lallai mafifici kuma mafi daukakan ayuka a wurin Allah
da girman matsayi awurin Allah shi ne
raya masallatayya dakunan Allah (Abin sani kawai wadanda suka yi imani da Allah su ne ke
raya masallatayyan Allah ).
Kuma raya masallatayya na kasancewa ne ta hanyar gina su da bauta a
cikin su da fiskantar su don tsaida sallah
da amsa kiran mai kira idan ya kira a gaggauto zuwa ga sallah .
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare
shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gre shi ya ce :- (Da ace
mutane sun san abin da ke cikin kiran sallah da sahun farko sa'annan ba za su same su ba sai da
kuri'a to da sun yi kuri'a kuma da ace sun san abin da ke cikin diban garji
da sun yi tsere zuwa gare shi da
sun san abin da ke cikin isha'i da asubahi da sun zo mu su ko da da rarrafe ne
) Buhari da Muslim ne suka rawaito
Ya ku bayin Allah:
Na daga cikin abin da ke daga darajoji
ya kankare laifuka akwai yawan taku zuwa masallatayya, An karbo da ga Abu Huraira yace :Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Shin bazan fada maku ba abin da zai kankare maku
zunubanku ba,ya daukaka darajarku ba.sai yace:
"Yawan taku zuwa
masallaci,kyautata alwala alokacin da ake kin taba ruwa, da zama jiran sallah
bayan sallah, wannan shine ribadi wannan shine Ribadi) Muslim ne ya rawaito
An karbo da ga Abu
Huraira yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Duk wanda yayi Sammako ko yayi yammaci zuwa Masallaci,
Allah yayi masa tanadin mazauni a aljanna,duk lokacin da yayi Sammmako ko
yammacin zuwa Masallaci).
Ya ku bayin Allah:
Ya ku mazowa dakunan Allah masu raya masallatan Allah,
barkanku da samun mafi yalwan inuwa. Albishirinku da mafi kyau da cikan haske,
An karbo da ga Abu Huraira yace :Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Mutum bakwai suna cikin inuwar Allah
ranar da ba wata inuwa sai inuwarSa sai ya ambaci da mutumin da zuciyarsa ke ta'allake da
masallaci) Buhari da Muslim
ne suka rawaito.
An
karbo daga Buraida al aslami Allah ya kara yarda a gare shi yace : -Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
yana cewa:
(Ka yiwa
masu yawaita tafiya zuwa Masallaci cikin duhu da wani haske cikakke a ranar alkiyama).
Abu
Dauda da Tirmizi.
Ku
sanya wa gidajen Allah wani kaso na daga lokacin ku , haka nan kuma da ibadojin
ku ku sanya wani kaso na farilla , ku gabatar wa ibadun ku abin da
zai amfane ku kuma Allah ya daukaka ku da shi ranan alkiyama , (kuma abunda ku ka gabatar wa kawunan kuy
na daga alheri za ku same shi wurin Allah mafi girma a lada ku nemi gafarar
Allah , Allah mai gafara ne mai jin kai)
Huduba
ta biyu
Dukkan
yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa datarwarSa godiya a gare \Shi bisa
datarwan Shi da kuma baiwansa na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
Shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya ina mai girmama Sha'anin Shi na shaida
cewa Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma Manzon Sa ne mai kira zuwa ga yardar Sa
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da sahabban sa da aminci
tabbatacce mai yawa.
Ya ku
bayin Allah:
Sauke
garilla cikin jama'a yana cikin manya manyan alamomi na musulunci kuma alamomi
na imani (ku yi
ruku'u tare da masu yin ruku'u), sallan jama'a ya ku bayin Allah yana daga cikin
mafificin ayyuka kuma mafi daukakan da'a kuma mafi tsarkakan ayyukan kusanci
kuma darajoji an karbo daga Abdullahi dan Mas'ud Allah ya kara yarda a gare shi
ya ce (Duk
wanda zai burge shi da ya hadu da Allah gobe yana musulmi to ya kiyaye wadannan
salloli din a yayin da ake kira zuwa gare su domin lallai Allah ya shar'anta wa
Annabin ku tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wasu sunnoni na
shiriya, lallai su din nan duk suna cikin sunnoni na shiriya, da ace za ku yi
sallah a cikin gidajen ku kamar yanda wannan wanda bai samu jam'I ba aka barshi
ya yi sallah a gida to da hakika kun bar sunnan Annabin ku da kuma kun bar
sunnan Annabin ku da kuwa kun bata , ba wani mutumi da zai yi tsarki ya
kyautata alola sa'annan ya nufi zuwa masallaci cikin wadannan masallatan face
Allah ya rubuta mishi a ko wani takawa da zai yi za a rubuta mishi lada a daga
shi daraja da ita a kankare mishi laifi dalilin ta , hakika ba wanda ya ke
barin sallah a cikin mu face munafiki wanda aka san shi da munafinci , hakika
mutum ya kasance ana zuwa da shi ana tagire gire da shi tsakanin mutane biyu
har a zo a tarar da shi cikin sahu) Muslim ne ya rawaito
An
karbo daga Ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi shi da mahaifin shi cewa Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (sallan jama'a yafi sallan mutum daya
da daraja ashirin da bakwai ) Muslim ne ya rawaito.
An
karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(sallan mutum a cikin jam'I tana ribanya sallan sa a
cikin gidan shi haka nan a kasuwan shi da da ribi ashirin da biyarsaboda haka
nema idan mutum ya yi alola ya kyautata
alola sannan ya fita zuwa ga masallaci ba abin da ke fitar da shi sai sallah
to ba zai yi wani taku ba face dawannan takun an daga darajan shi da ita kuma
an kankaare mishi kuskuren shi da ita idan ya yi sallah mala'iku ba za su gushe
ba suna mishi salati muddin yana wurin sallan sa suna cewa : Allah ka yi dadin
tsira a gare shi ya Allah ka mishi rahama, dayan ku ba zai gushe ba yana cikin
sallah muddin ya tsaya jiran sallah) Bukari ne ya rawaito.
Ya ku
bayin Allah:
Hakika
hudubar musiba ta korona ya girmama ga musulmai ya lalata sallan jam'i bakin
ciki da bacin rai sakamakon ta'allukin
zuciya ke yi da masallaci sai
radadin da shaukin da kwadayin ya yawaita ga mutane .
Hakika
Allah ya zo da yaye bakin ciki sai ya sanya mafita ga ko wani kunci da dukkan wani damuwa ya sanya mishi farin
ciki , to ga shi masallatai an bude kofofin su an kimtsa su farfajiyan su an
shirya su, ga dakunan Allah suna jiran
masu raya su da masu ziyartan su an daga sautukan kiran sallan su suna kira ku
gaggauto zuwa ga sallah ku gaggauto zuwa ga sallah ku gaggauto zuwa ga babban
rabo ku gaggauto zuwa ga babban rabo .
Muna
godewa Allah kuma muna kyautata yabo a gare shi muna rokon shi da ya dauke abin
da ya saura na daga wannan annoba kuma ya tunkude shi daga gare mu dukkan wani
bala'i kuma ya cika mana cikakken lafiya da waraka ku
gaggauto ya ku bayin Allah zuwa ga dakunan Allah ku amsa kiran mai kiran Allah
idan ya kiraye ku zuwa ga Allah da Manzon Sa idan ya kiraye ku zuwa ga abin da
zai rayaku kuma ya sa ku cikin walwala ya shiryar da ku, ku tsaida fuskokin ku
a dukkan wuraren masallataiyya, ku kiyaye farilloli ta inda duk lokacin da aka
yi kira zuwa gare su , (abun sani wanda ya ke raya masallatayyan Allah shi ne wanda imani da
Allah da ranan lahira kuma ya tsaida sallah ya bada zakka kuma bai ji tsoron
kowa ba sai Allah ya wuci wadannan su kasan ce cikin wadanda su ke shiryayyu) .
Yak u
bayin Allah Lalle ambaton ni'imar Allah na daga abin da ya yin a ni'ima da shi
ga wannan kasa mai albarka na ni'imar tauhidi da hadin kai da zaman lafiya da
kwanciyar hankali da hidima ga masallatayya biyu masu alfarma da masu zuwa gare
su, da bada kulawa ga batutuwa da suka shafi musulmai, da irin ayyuka na jinkai
a lokuta daban daban, da tabbatar da zaman lafiya na duniya tun lokacin da aka
kafa wannan kasa har zuwa wannan lokaci da muke ciki. Wanda zai sa mu godewa
Allah ga wadannan ni'imomi, da kiyaye amincinta da dukiyanta da tabbatar da
hadin kai irin na addini da dunkulewa irin na kasa daya mubaya'a irin ta sharia
da lizimtar jama'a da jagoranci da ji da bi da adua ga shuwagabannin kasanta ya
datar da su, Allah ya kiyaye kasar mu da sauran kasashen musulmai daga duk wani
abu mummuna da abin ki, lalle Shi mai ji ne mai amsawa.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق