الجمعة، 4 سبتمبر 2020

KA JI TSORON ALLAH A KO INA KA KE

 

اسم المترجم :أمين سعد

اللغة : الهوسا

التاريخ 16/1/1442ه

Hudubar masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na 16/1/1442 na shaihk Husaini Al -Asshaikh

 

Hudubar farko:

An karbo daga Mua'azu dan Jabal Allah ya kara yarda a gare shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(ka ji tsoron Allah a duk inda ka ke, kuma ka bi mummuna da kyakkyawa sai ta goge ta, ka mua'amalanci mutane da kyakkyawar dabia'a) Ahmad ne ya rawaito da Tirmizi kuma ya ce hadisi ne hasan, kuma da yawa daga cikin malamai sun inganta shi lallai hadisi ne mai girma da ya kumshi wasiyya mai girma wanda ya ke masu jumloli masu girma da ka'idoji muhimmai Ibnu hajar alhaisami ya ke cewa: wannan hadisi ne da ya tattaro sauran hukunce hukunce na shari'a wasun su sun ambace shi da uwar sunna ,aiki da shi ya kan kawo walwalan gidan duniya da na lahira da rabauta a cikin su:

Tushe na farko : akwai tabbatar da takawa ga Allah Mabuwayi da daukaka ta hanyan lizimtan umarnoni da da'a da kuma nisatan sabo da laifuka a bayyane da kuma boye .

Lallai wasiyya ce da ta kan sa bawa duk inda ya ke ya lizimci kiyaye dokokin Allah kuma ya yi nesa daga abubuwa na laifi da abubuwa da su ke muharramai , yana mai daidaito a kan tafarki mekakke yana mai kulawa da shi a cikin dukkan sha'ani Allah Madaukakin sarki ya ce :(ku ji tsoron Allah kuma ku sani lallai Allah yana ganin abin da ku ke aikatawa)

Kuma Allah Madaukakin sarki ya ke cewa(ku ji tsoron rananda za ku koma zuwa ga Allah sa'an nan a cikawa ko wace rayi abunda ta kasance ta ke aikatawa ba za ayi zalunce ku ba).

Ibnu Abbas da Sa'id dan Jubair suka ce: wannan wasiyyar Allah ce ga bayinSa a a'aya ta karshe da ta sauka a cikin alkur'ani , kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(ka kiyaye Allah sai ya kiyayeka). Lallai aiki da wannan asali yana hukunta samun rabauta mai girma da kuma lada mai daraja.

Ya zo cikin sahihain wato Bukhari da Muslim cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Mutane bakwai Allah na musu inuwa a cikin inuwarSa ranar da ba wata inuwa sai inuwarSa, kuma ya ambaci a cikinsu da mutumin da mace ma'abociya matsayi da kyawu ta neme shi sai ya ce lallai ni ina tsoron Allah Ubangijin talikai)

Tushe na biyu: biyar da kyakkyawa bayan mummuna, ita kyakkyawa kalma ce da ta tattaro dukkan abin da zai kusantar zuwa ga Allah Mabuwayi Mai daukaka, mafi girman kyawawan abin da su ke tunkude munana shi ne tuba da gaske da kuma neman gafara ta gaskiya da kuma komawa zuwa ga Allah komawa ta gaskiya,

 Imamu Ahmad ya rawaito daga Abu zarri ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (wani ya ce: ya Manzan Allah ka mini wasiyya sai ya ce: idan ka yi aiki mummuna to ka biyo ta da kyakkyawa sai ta goge ta ,sai ya ce: ya Manzan Allah na daga cikin kyawawa (la ilaha illallah)?sai ya ce ita ce mafificiya a cikin kyawawa).

Aikata ayyukan alhairi yana  kankare zunubbai da suka shude Allah Mabuwayi da daukaka ya ce:(kuma ka tsaida sallah a gefe guda biyu na gini da wani yanki na daga dare lallai ne ayyukan kwarai suna kore munanan ayyuka).

Allah Madaukakin sarki ya ce:(idan za ku nesaci manyan zunubai to za Mu kankare muku laifuka (kanana)), yazo a sahihu muslim (salloli guda biyar da kuma juma'a zuwa juma'a da ramadana zuwa ramadan suna masu kankare zunubban da ke tsakaninsu muddin aka nesaci manyan zunubai).

Tushe na uku: mu'amalantar halittu da kyawawan dabi'u da kuma kyawawan halaye da kuma tafarki wanda ya ke mai kyau wannan kuma ta hanyan dadadawa halittu da sake musu fiska da yalwata ayyukan ma'arufi gare su da kuma kamewa daga cutar da su, asali shi ne ka yardarwa dan uwanka abin da ka yarda wa kanka na daga maganganu kyawawa da ayyuka kyawawa da muamala na mutunci,Allah Madaukakin sarki ya fada yana mai yabo ga ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (lallai kana kan wasu dabi'u masu girma)  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (mafi cikan mumini imani shi ne wanda ya fi su kyakkyawan hali) Tirmizi ya rawaito kuma ya ce hadisi ne hasan sahihi,Ibnu hibban da hakim sun inganta shi , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(lallai mumini yana riskan darajan mai azumi da mai tsayuwa ta hanyan kyawawan halayensa) Abu dauda ne ya rawaito kuma Ibnu hibban ya inganta shi.

Ka yi kokari ya kai dan uwana musulmi a rayuwanka ka kasance cikin ma'abota kyawawan hali kuma masu bin abu buwa na yardan Allah wannan shi ne aiki mai girma a wurin Allah kai  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kidanya haka ma cikin da'a  mai sadarwa zuwa ga aljannan alkuld.

An tambayi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi menene biyayya kuma da laifi? Sai ya ke cewa:(Biyayya: ita ce kyakkyawan hali, shi kuma laifi shi ne abin da ya sosa cikin zuciyarka kuma ka kyamaci mutane su tsinkaye shi) Muslim ne ya rawaito.

Hakika an tambaye shi kuma game da yawan abin da ke shigarwa aljanna sai ya ce (tsoron Allah da kyakkyawan hali) Tirmizi ne ya rawaito kuma ya ce hadisi ne hasan sahihi , Ibnu hibban ingantashi

Ku tabbatar - Allah ya muku rahama- wadannan ginshikai masu girma ku lizimce su wadannan ka'idoji masu girma za ku samu rabauta ku samu walwala da nasara a duniya da lahira .

 

Huduba ta biyu:

  

Na daga cikin kyawawa wadanda su ke goge laifuka shi ne akwai kyautata wa mutane ta fiskoki daban daban, Allah Madaukakin sarki ya ce (ku kyautata lallai Allah yana son masu kyautatawa) ,

 An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: wani mutumi ya ce ya Manzon Allah : lallai wance tana yawaita  sallolinta da sadakanta da azuminta sai dai kawai tana cutar da makwabciyarta da harshenta sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (tana wuta) , sai aka ce ya Manzon Allah lallai wance ana ambaton karancin  azuminta da sallan ta kuma tana yin sadaka da  wani yanki na cukui amma bata cutar da makwabtanta , sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (tana cikin gidan aljanna) Ahmad ne da Bazzar suka rawaito da Ibnu hibban a cikin sahihansu da hakim kuma ya ce hadisin sahihi ne isnadinsa da kuma wasu sashi na daga malaman hadisi sun ingantashi.

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق