الجمعة، 11 سبتمبر 2020

TARIHIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI

 

ترجمة خطبة المسجد النبوي

اللغة : الهوسا

المترجم : أمين سعد

التاريخ :23-1-1442هـ

Hudubar Masallacin Annabi Tare da shaikh Abdullah bin Abdurrahman Albuaijan 23-1-1442AH 11-9-2020Ad

Hudubar farko:

Dukkan yabo  da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya cikamake manzancin sama da shari'armu ya kuma cikamake annabawa da manzanni da Annabimmu ya sanya al'umar mu tsaka-tsakiya, mafi alherin al'umar da aka fitarwa mutane

 

Na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai bashi da abokin tarayya, yana halittan abin da yaso kuma yayi zabi, na shaidah cewa Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzosa ne, mustafa kuma zababbe cikin zababbun zababbu.

 

Ya isar da sako kuma ya sauke amana kuma yayi nasiha wa al'umah kuma yayi jihadi a tafarkin Allah cancancin jihadi har yakini yazo mishi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi da wanda ya bisu da kyautatawa har zuwa ranan sakayyah.

 

 bayan haka:

 

lallai mafi gaskiayan zance shine littafin Allah, mafi kyan shiryarwa shine shiriyar Muhammad dan abdullahi, sharrin al'amura kuma sune fararrunta, dukkan wata fararriyar abu bidi'a ce, dukkan bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta.

 

Yaku wadanda sukai imani kuji tsoron Allah cancancin tsoronshi kuma kada ku mutu face kuna musulmai

 

Ya jama'ar musulmi, mutum yana tare da wanda yake kauna, kaunar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sharadi ne a imani, kuma mafificin hanya don kaunar Annabi sallallahu alaihi wa sallam, shine sanin rayuwarsa da halayensa da dabi'unsa, to ku san Annabinku domin ku san kimansa da matsayinsa, sai a samu kaunarsa ta samu da kuma da'a gare shi ba dayanku da zai yi imani har sai ya kasance Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance mafi soyuwa a gare shi akan kansa da dansa da mahaifinsa da ma dukiyarsa da mutane baki daya.

Ya ku bayin Allah:

Allah yana zaban manzanni cikin malaiuku da kuma a cikin mutane ma hakika Allah ya zabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, daga mafi tsadar ma'adinai da mafi tsada da kyau, Allah ya karrama shi kuma ya fifitashi akan sauran mutane, Allah Madaukakin sarki yace: (Hakika Manzo yazo muku daga cikinku yana mishi nauyi abin da ya wahalar da ku, mai fata ne ga muminai kuma mai jin kai mai tausayi).

 

Ya sanya shiryarwarsa ma'auni ne domin wurin falala da kamala, (Hakika ya kasance a gareku ga Manzon Allah abin koyi ga wanda ya kasance yana fatan Allah da kuma ranar lahira.)

Allah ya tsarkake shiryarwarSa da halittanSa da kuma iliminSa da hankalinSa da fadinSa da aikinSa ,Allah ya tsarkake shi tsarkakewa cikakkiya a zahiri da badini ya tsarkake shi a hankalinsa sai ya ce (sahibinku bai bata ba kuma bai kauce hanya ba) ya tsarkake shi a ganinshi sai ya ce:(gani bai kauce ba kuma bai wuce gona da iri ba) ya kuma tsarkake shi a kirjinsa(zuciyarsa) sai ya ce (ase ba Mu fadada maka zuciyanka ba?) ya tsarkake shi a ambatonsa sai ya ce:(sai Mu ka daga ambatonka gareka) ya tsarkake shi a tsarkinsa sai ya ce:(Muka dauke maka laifinka) ya tsarkake shi a gaskiyansa sai ya ce: (baya furuci bisa son rai) ya tsarkak shi a iliminsa sai ya ce :(ma'abociai tsananin karfi ne ya koyar da shi) , ya tsarkake shi a hakurinsa sai ya ke cewa: (mai tausayi ne da jin kai ga muminai) ya tsarkake shi a halitansa na gaba daya sai ya ce:(lallai kana kan dabi'u masu daraja).

Ya ku bayin Allah:

Lallai Allah Ta'ala ya halicci bayinSa suna masu karkata zuwa ga addinin Annabi Ibrahim gaba dayan su hakika sai shaidanu suka zo musu sai suka yi awon gaba da su daga addinin su suka haramta musu abunda Allah ya halatta musu suka umarce su da su yi shirka da Allah kuma cikin abin da Allah bai saukar da wani hujja ba lallai Allah ya yi dubi zuwa ga doron kasa sai ya fusata da su ,larabawansu da ajamawansu  sai saura daga cikin mutanen ahlil kitabi sai ya zabi a tsakaninsu mafi tsadan ma'adinai ma'abota izza da daukaka mabubbuga na alheri da falala , ya karramasu ya tsarkake su mafi karramansu da tsarkakansu shi ne Muhammad dan Abdullahi dan Abdulmuttalib balarabe bakuraishe kuma bahashime uwarsa Aminatu 'yar wahab bakuraishiya .

Ya zaba mishi mafificin wuri sai aka haife shi kuma ya taso aka turo shi a Makka uwar alkaryu , kuma masaukan wahayi ya kasance haifuwarsa a Rabi'ul'auwal ne shekaran giwaye, bayan haka da kwatankwacin shekaru dari shida da talatin da biyu daga haihuwar almasihu Isa alaihissalam dan Maryam aka haifi Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , ya turo shi zuwa ga Makka a shekarunshi ya dumfari arba'in ya mutu kuma yana sittin da uku na daga shekaru .

Ya jama'ar musulmai:

Manzon Allah ya rayu ya dandani daci irin na maraici mahaifin shi ya rasu a halin shi yana cikin mahaifiyarsa, mahaifiyar shi ta rasu yana kwatankwacin shekara shida na daga rayuwansa, sai kakansa Abdulmuttalib ya dauke shi shekaru biyu har zuwa ya rasu sai baffan shi Abu dalib ya jingina shi sai ya zama yana kewaye da shi yana kiyaye shi yana bashi kariya har zuwa lokacinda ya rasu yana dan shekara goma daga turowa manzanci .

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance shi kadai ne a wurin mahaifansa , bashi da wani dan uwa ko dan uwa hakika Allah ya tattaro mishi siffofi na alheri da falaloli da ta'adodi da dabi'u kyawawa yayi harkan kasuwanci ya fita zuwa sham ba so daya ba ya fita tare da baffanshi a kasuwanci haka nan kuma ya fita kasuwancin Khadija matarsa 'yar Kuwailid kamar yanda ya yi kiwon dabbobi bisa ga wasu silalla ga mutanen garin Makka .

Ya auri Khadija 'yar kuwailid shekarunshi na ashirin da biyar , ita kuma ta kasance mafificiyar me taimakawa da kuma bada gudumawa , ta haifa mishi dukkan 'yayanda ya ke da su maza banda Ibrahim shi uwarsa Mariya ce alkibdiyya .

Yayin da ya kai shekaru arba'in Allah ya zabe shi kuma ya turo shi kuma ya cikamake Annabawa da Manzanni da shi sai ya fara da'awan shi zuwa ga tauhidi da kuma yin nesa da shirka ya kuma kwadaita zuwa ga kyawawan dabi'u na alheri da umarni da kyakkyawa da hani da mummuna da zalunci da barna, yana Makka na tsawon shekaru goma sha uku yana kira a boye da kuma a bayyane dare da wuni sai suka rinka sanya hannayen su a kunnuwansu suna makirci makirci mai girma suka rufa tufafinsu kuma suka doge suka yi girman kai girman kai suka ketare iyaka suka yi musu suka karyata suka cutar kuma suka yi izgili suka tuhume shi da sihiri da kuma kahana (bokanci) da kuma hauka , Allah ya girmama bala'I ga mabiyansa da kuma masu taimakonsa sai mutanen Makka suka yita azabtar da su suka kokkore su basu musu ukuba ba face sai don sun yi imani da Allah Mabuwayi abun godiya .

Ya ku bayin Allah:

Allah ya yi izini ga AnnabinSa da yayi hijira zuwa ga Daibatuddaiba (Madina) inda zama ke yin dadi kuma gida na imani ta inda ya ke shi ne masulala na imani ta inda rundunan Allah Ansarawa suke, wadanda suka mallaki gida kuma da imani kafun su suna son wandanda suka yi hijira zuwa gare su kuma ba'a samun wani abu a cikin zukatan su na bukata cikin abunda suka bada kuma suna fifitawa a kan kansu koda sun kasance sunada haja duk wanda aka kare shi daga rowan kanshi to hakika yana cikin wadanda suka rabauta.

Daulan musulunci ta fara tana habaka tana tasowa a garin Madina aka assasata a dan lokaci kankani , hukunce hukunce suka sauka sa'an nan sai ta rika tattaro mutane ana jihadi a tafarkin Allah ana yakan duk wanda ya yaki Allah da ManzanSa , aka kulla kulleleniya da alkawura da yarjejeniya da mawasik.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya cigaba da zama a ciki shekara goma har zuwa lokacin da wasu abubuwa suka faru masu yawa da kuma shari'o'i da kuma yake yake a doron kasa tunda Allah ya shinfidata kuma ya kafa ta tarihi bai san wani farawanta ba har zuwa yau wasu alumma da suka fi gaskiya da a'adalci akan tsayuwa akan tafarki mikakke kuma fi soyuwa zuwa ga Allah game da wancan fatra da wancan jama'a .

Ina neman tsarin Allah daga sharrin shedan abin jefewa, Shi ne wanda ya turo cikin ummiyai Manzo cikinsu yana karanta a'ayoyinSa kuma yana tsarkake shi kuma yana karantar da shi littafi da hikima ko da da sun kasance kafin haka suna cikin bata mabayyane .

 

Huduba ta biyu:

     Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah mai bayyana gaskiya mai daukakata mai kaskantar da karya kuma mai tunkude ta ya tura ManzonSa da shiriya kuma da addini na gaskiya domin ya bayyana shi akan addinai gaba daya ko da mushrikai sun ki.

 ya ku bayin Allah :

a tsakanin shekaru goma na lokacin zaman Madina Allah ya cika addininShi , mutane suka shiga addinin Allah tawaga tawaga musulunci ya shiga ko wani bangare na yankin kasashen larabawa, mutanenta suka rusunawa musulunci suka mika wuya a gare shi, wadannan watanni akwai abubuwa da suka faru a wannan lokaci

A shekaran farko: na hijira Annabi tsira da am incin Allah su tabbata a gare shi ya gina masallacinSa da kuma gidansa , ya hada 'yan uwantaka tsakanin muhajirun da ansar ya shar'anta kiran salla.

A shekara ta biyu: ya maida alkibla zuwa Ka'aba kuma aka farlanta azumin ramadana a ciki ne kuma aka farlanta sadakatulfidr zakkan fidda kai .

A ciki ne kuma aka yi yakin badar kuma a ciki ne Rukayyatu 'yar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ta rasu a ciki ne kuma Annabi Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya shiga da A'aisha , a ciki ne kuma aliyyu Allah ya kara yarda a gare shi ya auri fadima 'yar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi .

A shekara ta uku : an yi yake yake daga ciki akwai yakin uhud akwai kuma yakin banunnadir an haramta giya bayanta sannan kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya auri Hafsa 'yar Umar dan kaddabi , Usman kuma ya auri Ummu kulsum 'yar Manzon  Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , kuma aka haifi Hasan dan aliyyu ga Fadima

A shekara ta hudu: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya auri ummu salama , aka kuma shar'anta taimama , aka ce kuma a wannan shekaran ne aka yi yakin kandak da kuma zatu rika'a a ciki , haka nan kuma sallan tsoro .

A shekara ta biyar: aka yi yakin daumatuljandal da kuma kuraiza , aka shar'anta kuma hijabi.

A shekara ta shida :aka yi sulhul hudaibiya da kuma bai'atul ridwan da kuma yakin banil mustalak, Rana kuma ta kisfe aka saukar da hukuncin zihari.

A shekara na bakwai : ne aka yi yakin kaibar kuma umra na kada'a Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi aure da Habiba da Maimuna da Safiyya da Mariyal kibdiyya , kuma Abu huraira ya musulunta.

A shekara na takwas: ne aka yi yakin mu'ta da zatussalasil , aka bude Makka a Ramadana, aka haifi Ibrahim kuma Zainab 'yar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ta rasu , a ciki ne kuma aka yi yakin Hunain.

A shekara ta tara: a ciki ne aka yi yakin tabuka Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi hajji da mutane , kuma Ummu kulsum 'yar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ta rasu , Najashi ma ya rasu kuma runduna runduna na zuwa suka yawaita.

A shekara ta goma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi hajjin ban kwana, kuma Ibrahin dansa ya rasu,Allah ya saukar da (idan nasara ya zo daga Allah da kuma budi)(ka ga mutane na shiga addinin Allah kungiya kungiya)(to ka yi tasbihi da godiya ga Ubangijinka kana mai neman gafararSa, lallai Shi ya kasance mai yawan karban tuba ne).

Ya ku bayin Allah:

(Dukkan rai zai dandani mutuwa,) (dukkan wanda ke doron kasa kuwa zai kare) .

Ya ce

shi  mutuwa kan da ke sara baya kaucewa ya yi ha'inci ***

Tabki ne mai dafi duk wanda  ya rayu zai sha shi**

A cikin Rabi'ul auwal ne a shekara na sha daya bayan hijira kuma hajjin ban kwana Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ji wani irin ciwo, na bada fansa da mahaifina da kuma mahaifiyata a gare shi , Allah ya bashi zabi sai ya zabi haduwa da Ubangijinsa ,

Ya Allah Arrafikul A'ala, ya Allah Arrafikul A'ala , lokacin rabuwa ya yi sai aka yi wasiyya kuma ya yi  ban kwana, duniya ta yi duhu sakamakon rabuwa da shi sai ga shi an shiga matsananci bakin ciki.

Wayyo Allah , abin mamaki da irin girman wannan bala'in da tsananin wannan musiban kai ba abin da ya kai wannan wahala ba wani lokaci da aka wuce shi mai nauyi irin wannan , hakika  wahayi ya yanke daga kasa sakamakon rasuwan Annabi Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , duniya ta yi duhu .

(Muhammadu ba wani ba ne face Manzo hakika Manzanni kafin shi sun shude).

 

    

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق