السبت، 19 سبتمبر 2020

FALALAN LIKITA DA LIKITOCI

 

 

ترجمة الخطبة بالمسجد النبوي

اسم المترجم :أمين سعد

اللغة : الهوسا

التاريخ 1-2-1442هـ

Hudubar juma'a  na  masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na Shaikh Salah Albudair 1-2-1442.AH /18-9-2020AD

 

Hudubar farko:

Ya ku musulmai:

Ilimin likitanci na daga cikin ilmuka mafi daukaka da amfani, kuma yafi girma da tasiri, kokari a cikin shi yana cikin dabi'u na masu daukaka, yin kasa da haka kuma wata ukuba ce kamar sauke nauyin abu mai wahala a wurin wahalan haurawa zuwa gare shi, ba gushewa mai neman ilimin likitanci yana mai haurawa zuwa gare shi yana hauhawa daraja bayan daraja har ya isa zuwa ga matsayi madaukaki da martaba mai daraja wanda ba kowa ya ke samunsa ba sai masu kokari  tsayayyu, ba kuma mai riskansa sai wanda ya dace kuma ya lizimci juriya.

 Imamushshafi'i ya ce:'' ilimi iri biyu ne: ilimin fikihu na addinai da kuma ilimin likitanci na jiki ''

Rabi'i ya ce: na ji Shafi'i yana cewa: ban san wani ilimi ba bayan halal da haram da yafi kyau kaman ilimin likitanci .

An ce: kar ka zauna a garin da babu shugaba da zai baka kariya, babu ruwa da zai shayar da kai, babu malami da zai baka fatawa babu likita da zai baka magani.

Musulunci ya kula da harkan likitanci kwarai da gaske dukkan kulawa, ka duba littafi na dibbu (likitanci) a cikin sahihulbukari da kuma babi na magani da rashin lafiya da rukiya a cikin sahihu Muslim da kuma kitabuddibbi a cikin sunanu Abi dauda, da littafi na dibbi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a cikin sunanuttirmizi da kuma littafi na dibb a cikin sunanu kubra na Nasa'i, da kuma littafin Addibb a cikin sunan Ibnu maja.

An rawaito daga Ibnu Masawaihi likita lokacin da ya karanta hadisin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da ya ke cewa (Ba wata jaka da dan Adam zai cika ta zama sharri a gare shi fiye da cikin shi, ya ishi dan Adam 'yan wasu lomomi da za su tsaida mishi kwankwason shi in ya kasance ba makawa to ku kasa shi kashi uku, kashi daya na abincinsa, kashi daya na abin shan sa, kashi daya na numfasawarsa).

Ya ce: da mutane za su yi aiki da wannan kalmomi da sun kubuta daga rashin lafiya da cututtuka, da ma an rasa asibitoci da  shaguna na magani, kemes sun zama ba amfani.

Larabawa suka ce: mafi alherin abin kalace shi ne na sassafe mafi alherin abin cin dare shi ne ………

Likita haziki kwararrae wanda ya ke ya kware suna amfani ne da magunguna wanda suke na boye da suka rufe suka sa yanar ido , allah ya sanya damtsenSa ya zama rahama, mishradansa ya zamana shafaka ciyakanSa ya zamana tsira sadarwanSa ya zamana karba, ribadinSa ya zamana magani, magungunanSa kuma ya zamana waraka.

Larabawa sun ambace shi da mai hikima mai tausayi saboda yana tausayawa ga mara lafiya yana mar muladafa, yana mannashi a jiki, Allah Shi ne wanda ya ke warkarwa kuma ya ke bada lafiya.

Likitoci bas]u da iko koda sun hadu da su koro waraka ga mara lafiya face da izinin Allah saboda Shi kadai ne mai bada waraka, wanda ya ke jarrabawa da cututtuka kuma ya ke bada taimako da magun guna ya kuma rahama da waraka, likita na mun fatan waraka ga idona*** shin akwai wani bayan Allah da ya ke likita?

Yayinda waraka ya zama daga cikin tushe na ni'imomi wanda mara lafiya baya samu sai daga wurin Allah ba wai daga wurin mai magani ba, Ibrahim alaihissalam ya ke cewa: (idan nayi rashi lafiya Shi ya ke bani waraka)

 An karbo daga suhaibu dan sinan arrumi Allah ya kara yarda a gare shi( a kissan wannan yaron wanda ya kasance yana warkarda makaho da kuma mai kuturta kuma yana bada magani da sauran cututtuka da izinin Allah,  sai bafaden sarki ya ji shi bayan kuma da ya makance sai ya zo wurin wannan yaron da wasu kyaututtuka masu yawa sai ya ce: menene wannan? Sai ya ce duka na tattaro naka ne idan ka warkar da ni, sai yaro ya ce: ni bana warkarda wani sai dai Allah ne ya ke warkarwa idan ka yi imani da Allah sai na ma addu'a sai ya baka waraka, sai ya yi imani da Allah shi ke nan sai Allah ya bashi waraka ya maida mishi ganinshi) Muslim ne ya rawaito.

** sai na wayi gari bana rokon likita don ya bani waraka don likitancin shi***

** sai dai ina kiranKa ne ya Mai saukar da ruwa***

Likitoci da nasis sunada falala da zance ba zai iya tattaro su duka  game su ba

** ka sani wadatanka kyautanka ba'a iya sakanyawa ***

Shin ana iya sakanyawa bisa ga abubuwa masu tsada na cikin kogi? ***

To ku kiyaye wa likitoci matsayin su da malaman jinya ku kiyaye musu matsayin su ku gode musu bisa kokarin su da irin bada lokacin su da suke yi, hakika sun tsaya gaba dayan su  wurin bada katanga mai kariya madaukakiya, domin kiyaye mutane daga fadawa ga mutuwa .da dulmuyar korona zuciyar da ba ta kokawa da farfajiya da ba a takawa.

Wasu kamshi na busawa don dadin yabo

                                       Irin nasu a ko ina ana shakansa.

Mun yabe su ba mu riska ba da yabon su

                                      Ba mu bar wata magana ba.

Yabo da rera waka ga irinku akwai dadi

                                     To me zan ce ne bayan ku din ku ne

Kun fifita marasa lafiya a kan yaranku

         Kauna da fifita wani akai ana sanin shi daga gare ku

 

Ya ku Musulmi!

Mustahabbi ne neman magani, idan barinsa zai kai ga halaka to ya zama wajibi.

An karbo daga Usama dan Sharik Allah ya kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(ku nemi magani –ya ku bayin Allah- lalle Allah subhanahu bai sanya wata cuta ba face ya sanya mata magani banda tsufa )  

A wani lafazi (face mutuwa ) ya na nufin mutuwa. Ahmad da Ashabus sunan,

Idan al'amari mukaddari tabbatacce ya sauka lokaci da a ka yanka mishi ya kare magunguna sai su ki aiki dabaru su kare.

Hakika mutane kafin mu sun rabu da masoya

            Maganin mutuwa ya gagari duk wani likita.  

Sau dayawa halaka kan tsallake mara lafiya

          Ya tsira likitan shi ya mutu da itacen magani.

Likita na cewa da kai maganinka na guri na.

                                Idan gwada tafin hanu da zira'i

Da ace likita ya san maganin cuta

                Da zai maida mutuwa bai dandani  cece kuce ba

Mu kan sanya sababi ga magani idan mun yi rashin lafiya

    Shin magani na warkarwa daga mutuwa ne?

Muna zaban likita,ko likita na iya

    Jinkirta abin da aka hukunta

Numfasawarmu ba wani abu bane face a kididdige

  Kai komonmu ba wani abu ba ne face karewa

Ya ku musulmai!

Ya wajaba ga likita ya kwadaitar da mara lafiya ya sa musu tsammanin samun sauki, ya tausasa musu a wajen zance, ya jefa musu farinciki, ya yelwa, da yaye mishi bakinciki da sa mishi annashwa, da lausasa masa da gusar masa da tsoro, da damuwa a kwantar masa da hankali da firgici, da tunatar da shi da sanya mishi natsuwa.

Hakika an ce : Ludufi irin na likita shine rabin magani, dariya a fiskar mara lafiya kan saukake mishi radadin ciwo,yana jefa farinciki a gare shi yana tasiri da bai boyuwa, faruwan shi na ratsa jiki yana da fa'ida mai yawa.

Kuma likita mai tsauri da kaushin hali ya kan gitta wa mara lafiya ne tamkar iska mai kai hari ta tunbuke abin da ke gabanta tana rusa kyakkyawan fata irin ta zuciya, wanda ya tsorata mara lafiya da cuta ta ba zata ba tare da ya  yi wata shimfida ba ko mukaddima ko kankantar wa ba to hakika ya kara bata lamari ne, ya dada illa ne ga cutar.

Ya wajaba ga likita ya zama ya siffantu da hakuri da lura da hakkokin mara lafiya ya karya abin da ya samu mara lafiya ya karfafe shi ya girmama kokawansa.

 Ya ku likitoci ku riki hannayen marasa lafiyanku daga kunci na zafi da radadi zuwa ga yalwa na fatan alheri da taku irin na kunci zuwa ga farfajiya na yaye bakinciki.

Ya wajaba ga likita ya riki mara lafiya tamkar  kan shi sai ya bashi kariya ya mutunta shi ya kiyaye sirrinsa ya boye laifin  shi ya kame daga yada cutar da ya ke tare da ita wanda a cikin yaye ta akwai cutuwa gare shi, Ya wajaba kada ya yaye al'auransa sai idan ya kama na larura na bada magani.

Ya wajaba ga likita ya kirdada sannan kuma ya kiyaye ya kuma jinkiri da kuma yi jinkiri kar ya yi gaggawa wurin binciko cutan da kuma bada maganinta ya tabbatar daga illa na wannan  rashin lafiyan da kuma ya nemi shawara cikin al'amura da suka rikice mishi kada ya yi gaggawa ya bar abkawa ga abu muddin bai kware ba.

Ya haramta mutum ya bada magani wanda baida iliminshi, wanda bayi da kwarewa ko gwanancewa, a duk lokacinda mutum ya kekeren likitanci bisa jahilci ya bawa marasa lafiya magani hakika ya ruudar da mutane kuma ya hujumi da gjahilcinsa bisa ga abin da ya ke na lalata rayuka kuma ya bijiro zuwa ga abin da ya ke wato tahawwuri tare da kuma munanta bada magani zowa ga cutarwa da gan gan to ya wajaba a ladabtar da shi kuma abin da ya ellanta ya biya saboda hadisin Utbatu Umru dan Shu'aibu daga babansa daga kakansa ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce : (duk mutumin da yayi liktanci bisa karya a hali bai san likitanci ba to shi din nan zai biya abin da ya lalata) Abu dauda ne ya fitar da shi da Nisa'I a wurin darakutni kuma akim ya inganta shi (duk wanda ya yi likitanci a kuma shi ba likita ba bai iya likitanci ba sai ya kashe rayi ko kasa da haka to lallai shi zai biya).

Baya halatta ga mai yin likitanci bisa jahilci ko kuma shi likita wanda bai kware ba ya je ya rika yin aikin tiyata ko kuma ya fiskance ta domin iya gudanar da ita hakika ya dauka wa kanshi laifi kuma ya yi zalunci ya yi barna , kuma dole ya biya abin da ya yi kuskure a ciki da abin da aka samu na matsala.

Shi likita wanda ya ke ma'aboci sana'ansa likitanci idan hanunshi ya yi wani laifi ko ya kuskure irin kuskurenda makamantanshi ba sa yin irinshi ko kuma ya yi sakaci ko kuma ya gajarta ko kuma ya ketare gona da iyaka, to shi zai iya biyan asaran da ya biyo.

Kaddabi ya ce: '' ban san wani sabani ba cewa wanda ke bada magani idan ya ketare iyaka ya laata mai rashin lafiya shi ne zai biya abin da ya lalata, haka nan wanda ya ke bada magani a ilmance ko kuma a aikace bai sansu ba to mai ketare iyaka ne , idan ya haifar da wani abu sakamakon wannan abin da ya yi to dole ne ya wajaba ya biya diyya ''

Shi kuma likita jahili wanda zai iya haifar da mutuwa ya shuka abubuwa na tsoro, ya kai ga halaka idan har ciwo ya kara ruruta to zai bayyana a nan irin sakaci irin na likita.

***………………………………***……………………

 

 ya haramta ga likita ya bada magunguna wanda mara lafiya bai bukatanshi , ya haramta ya yiwa mara lafiya kari cikin abin da ba zai sha ba ko ba za a markada ba ko ba za a yi allura ba kafun ya tantance shi na daga wani illa kawai bisa ga zargi ko kuma bisa zato ko kuma kawai ya raya irin maganin da za a bashi , cututtuka ba'a iya magance su da wahami ba abun nufi shi ne gusarda rashin lafiyan ba sai don a gusar da shi ta fiskan amuntacce wanda hakan ba zai haifar da wani cutan ba ko kuma wani illa yafi tsanani ba.

Ya haramta ribatan mara lafiya amishi wasu gwaje -gwaje da aune aune da diban jini wanda ba bukatansu ko kuma ba wata fa'ida cikin tafiyar da su sai kawai kasuwanci ko kuma kwace dukiyan marasa lafiya , tir da irin wannan dukiya din , dukiya ne da bazai amfanu ba ba zai habaka ba sai bisa kasuwanci da radadin mara lafiya da kuma wanda suke cikin halin zazzabi.

Na daga cikin likitoci da kuma masu kemest wanda suke bada magani ga mara lafiya bisa ga wani farashi tare da akwai wani madadin shi wanda yafi dacewa kuma mai sauki a wurin farashi yana yin haka ne domin manufan ya habaka wa kamfani magungunanta ko kuma domin ya samu wasu sashi na garabasan da kamfanin ke gabatarwa saboda maslahansa a fifitata akan maslahan mara lafiya ba zai yi haka ba sai wanda zuciyarsa ba rahama ko yana kusa da ya rasa rahama da kuma rashin tsoron Allah da rashin alkawari da kiyaye amana.

An karbo daga Anas ya cewa: ba sa'annin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke  mana huduba face ya ce: (babu imani ga wanda ba yida amana babu addini ga wanda bayi da alkawari) Baihaki ne ya fito da shi.

Ku kiyaye dajjalai na daga 'yan tsubbu masu bada magani wadanda suke masu da'awan likitanci wadanda suke bude wuraren asibitoci da akwai shubuha a cikin su suna karban marasa lafiya ba tare da wani izini na hukuma ba kuma sunada ikon bada waraka bisa ga wasu cututtuka suna saida kayakin aiki  da suke akwai zamba a ciki ko algus.

Muna gargadan musulmai kar su gaskata wadanda suke ba ma'abota fanni ba a likitanci wadanda suna yada bayanai da siffantawa irin na likita ta hanyan kafafan sada  zumunta suna saida rudu suna wasa da rayuwa na marasa lafiya suna sadar da cutuwa bayyananne wanda ake da yakini a madadin lafiyan mutane da kuma jikinsu.

 

Suna yada abubuwa na mafi hadari kuma suna afkawa gidaje ku kiyaye su kar ku rudu da wadannan azzalumai masu barna a doron kasa mujrimai a hakkin rayi na dan Adam wanda musulunci ya zo domin kiyaye shi ya bashi kariya kuma ya haramta keta alfarman shi.

Ya ku musulmai:

Hakika Allah ya dauke rayin Abatil abubuwa na bata irin na bokaye da hujjoji da Alkur'ani, to ku kiyaye bokaye da kuma dajjalai da kuma masu buga kkasa ko taurari da masu sha'awaza konkulomboto wadanda suna da'awan ilimin gaibi da gano abubuwanda suke na zuciya da sanin abubuwanda suka boyo, to ku kiyaye wadannan dajjalan masu bada magani wadanda sun fita daga magani na shari'a sun kare akai suka shigarda wasu abubuwa na bidi'o'I wanda su ke masu laifi masu fusatawa, ku kiyaye masu yaudara masu rufa ido makaryata wadanda suke da'awan bada magani ga wanda aka ma sihiri da kuma wadanda suke aljani ya shafe su da kuma wadanda suke masu farfadiya ta hanyan shakewa ko ratayewa ko daurewa ko duka ko bada wasu dalasimai , da de wasu kulumboto suna saida wasu layu da kuma wasu abubuwa dunkulallu da kuma tamima ,hatimai da kuma wasu kariya da suke yi domin neman waraka da kuma abubuwa da ake daurewa da wasu rukiya na shirka wanda suna habaka da barna da kurafa suna saida abubuwa da suke na wahami wanda bata zayyanuwa a ganta sai ga ma'abota raunin hankali da akida  An karbo daga Imran da Husan Allah ya kara yarda a gare ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Baya cikin mu duk wanda ya yi shu'umanci haka nan kuma ko wanda aka yima, kuma baya cikin mu wanda ya yi bokanci ko wanda aka mai bokanci ko kuma ya yi sihiri ko yasa aka mishi sihiri, duk wanda ya yi kulle kulle da wanda ya zoma boka ya gaskata shi cikin abin da ya ke fada to ya kafurce abin da aka saukar wa Muhammad) Bazzar ne ya fito da shi.

Duk wanda ya je wurin wadanan dajjalan to shi ma yana tarayya da su wurin alhaki saboda bakinsu da muninsu ya yi yawa kuma suna habaka abin da suke na barnan su to ya wajaba a isar da bangarori na tsaro don duba mataki da za su dauka ga wadannan kazantattu , ya haramta a boye sha'anin su ko a musu shiru .

*** ya fi mana sauki ba kusa ba da jikin mu ya cutu ***

*** mutuncin mu da hankalin mu ya tsira ***

Ina fadin abin da kuka ji kuma ina neman gafaran Allah ni da ku da kuma sauran musulmai daga dukkan zunubbai da kusakurai ku nemi gafaran Shi domin Shi mai gafara ne ga masu komawa gare Shi.

 

Huduba ta biyu:

Ya ku musulmai:

Halittu ana nufansu da jarabawoyi, hakika an ce: muddin kana wannan gida, kar ka yi mamakin faruwan abin da ya ke mai aukuwa  jirkitacce, kar ya kasance cikin wadanda idan wani abu na cuta ya same su sai su firgita su gaza hakuri sai zuciyan su ya dare su yi nesa, yanke kauna daga rahamar Ubangijinsa ya tuna fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (lallai bawa idan yana da wani matsayi a wurin Allah ba zai riske shi ba ta hanyar ayyukan shi sai Allah ya jarrabe shi a jikin shi ko dukiyarsa  ko kuma a dan shi sa'annan sai ya sa shi ya yi hakuri bisa hakan don ya hadu da shi har ya kai shi wani matsayi wanda Allah Ta'ala ya riga ya rubuta shi  a gare shi) Abu dauda ya fitar da shi.

Wani daga cikin magabata ya ke cewa: '' ba don musimun duniya ba da mun zo kiyama muna talakawa''

Kais binu Ubad ya ke cewa:'' awowinda aka yi na wahala suna tafiyar da awowin da aka yi na kusakurai ''

Kada mumini ya yi fatan aukuwan ukuba sai dai ya roki Allah waraka , an karbo daga Anas da Malik Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: (Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ziyarci wani daga cikin musumai ya rame ya zama kaman wani dan tsako, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da shi shin ka kasance kana addu'a da wani abu ne? ko kana rokon Allah da shi? Sai ya ce e, na kasance ina cewa '' ya Allah : muddin zaKa mini ukuba a lahira abin da zaKa min ukuba da shi a lahira to ka sanya min shi a nan duniya sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Subhanallah! Ai Ba zaka iya shi ba inama ka ce: Ya Allah ka bamu kyakkyawa a nan duniya ka bamu kyakkyawa a lahira ma ka kare mu daga azaban wuta? Sai ya roki Allah da ya bashi waraka). Muslim ne ya rawaito.

***Idan ya yi rashin lafiya to hakurin shi ba zai yi rashi lafiya ba ***

*** idan yayi zazzabi to azaman sa ba zai yi zazzabi ba***

***  idan ya mika wuya to ba wai ya rage ba ne sai dai ***

*** na kubuta ni daga alhumam zuwa humam ***

    

Ku yi salati da aminci ga Ahmad alhadi mai ceton dukkan halittu wanda ya yi salati a gare shi guda daya Allah zai mishi salati guda goma.       

 

 

 

 

 

   

                               

 

 

 

 

 

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق