الأربعاء، 20 مايو 2020

LOKUTA MASU DARAJA A KAN YAWAITA AYYUKAN ALHERI A CIKINSU

Hudubar masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na 22/9/1441 na shaihk Ali dan Abdurrahman Alhuzaifi.

Da sunan Allah mai rahama mai jin kai.

 

Huduban farko :

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin kasa da sammai a hanun shi ne alheru su ke , shi ne kuma wanda ya ke gafarta zunubai yana tunkude mummuna da abinda aka ki ina kyautata yabo ga ubangijina kuma ina gode mishi bisa ni'mominSa masu yawa wanda ba mai iya  kididdige su sai shi wanda muka sani daga cikinsu da wanda ba mu sani ba shi ne ma'aboci falala da kuma kyawawa ,na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya mai amsa addu'o'i , na shaida cewa Annabin mu kuma shugaban mu muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne mai kira zuwa ga  Aljanna masu yawa wanda aka karfafe shi da mu'jizozi, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci bisa albarka ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalanSa da sahabbanSa wadanda suka tsere zuwa ga ayyuka na kwarai.

Bayan haka:

Ku ji tsoron Allah ta hanyan kusantazuwa gare shi da ayyukan yardanSa da kuma nesatan fushinSa da azabansa ta hanyan barin abubuwan da ya haramta.

Ya ku musulmai :

Hakika Allah ya kwarara muku a wan nan wata albarkoki daga cikin albarkatu  da alherori Allah ya yi baiwa a cikin shi da nau'uka na biyayya masu yawa Allah kuma ya kiyaye ku daga abubuwan da suke muharramai da kuma abinda aka ki da abinda Allah ya boye muku na daga lada bayan mutuwa shi ne abunda zai faranta wa mumini rai kuma duk wani mai musabaka a cikin alheri zai yi musabaka zuwa gare shi , Allah madaukakin sarki ya ce (ka ce da falalan Allah da rahamarSa saboda haka su yi farin ciki shi ne ya fi akan abin da su ke tattarawa) sai suka bi kyawawa da kyawawa to ku bi ayyuka na kyawawa da kyawawa ku kasance a kjarshen watan ku kun dada tsananta kokari kun fa girmama neman daidai ku yi kuma nesa daga zunubai da sabo wanda suke bata ayyuka na kwarai ko suke rage ladansu, Allah madaukakin sarki ya ce: (ya ku wadanda suka yi imani ku yi da'a wa Allah ku yi da'a wa ManzonSa kada ku bata ayyukanku) a'aya ubangijin mu mai rahama mai jin kai ya shar'anta mana wasu kofofi na falaloli da ayyuka na kwarai domin mu yawaita alheri dama da muka samu na rayuwa baka san wani aiki ne Allah zai karba ba ya tsiratar da kai daga azaba da shi , Allah Madaukakin sarki ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani ku yi ruku'u ku yi sujjada ku bauta wa ubangijinku ku aikata alheri ko za ku samu rabauta)

An karbo daga Abi zarrin Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Mazon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(kar ka rena aikin alheri komin kankantan shi ko da ma a ce ka hadu da dan uwanka ne da sakekken fiska) Muslim ne ya rawaito , duk wanda ya nemi rabauta da tsira da kuma rayuwa na dindin din cikin ni'ma dawwamammiya to ya yi aiki na kwarai a cikin wadan nan ranaku masu falala da dararraki masu albarka domin lallai abinda ya shude ba zai dawoba na daga lokaci masu daraja su ne lokaci na ayyuka kuma da tabbatar da alherori na daga burace burace , an karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:( ku gaggauta da ayyuka abubuwa guda bakwai ,shin akwai abinda ku ke jira facetalauci abin mantawa ? ko wadata abin ………? Ko kuma rashin lafiya ? ko kuma tsufa ? ko kuma mutuwa shiryayyiya ? ko kuma dajjal to sharrin abinda ya ke boye da ake jira ? ko kuma tashin alkiyama domin tashin alkiyama shi ya fi zafi shi ya fi bala'I kuma shi ya fi daci )Tirmizi ne ya rawaito kuma ya ce: hadisi ne hasan ku din nan ya jama'ar musulmai kuna goman karshe na ayyukan albarkatoci da kuma  ayyuka ku sani abin la'akari shi ne karshen su kuma lailatul kadri na kaura a cikin wan nan goman ne duk wanda aka datar da shi ya yi tsayuwan darenta to za a gafarta mishi abinda ya gabata na daga zunuban shi , An karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (duk wanda ya yi tsayuwan daren lailatul kadri yana mai imani kuma da neman lada za a gafarta mishi abinda ya gabata na daga zunubban shi) Bukari da Muslim ne suka rawaito , alherin ta da albarkatun ta ko wani musulmi na iya riska bauta a cikinta shi ne abinda ya fi na daga ibadan watanni dubu wanda ba a cikin daren lailatulkadri ba Allah ya kebance wan nan al'umma da ita wan nan kuma falalan Allah ne da ya ke bawa wanda ya so Allah ma'abocin falala ne mai girma,ya ku musulmai : ku ku yawaita na daga adu'a da adauke bakin ciki daga al'umma hakika Allah ya muku alkawarin amsa addu'a a wannan wata mai girma kuma ku yi tawakkali zuwa ga Allah da ayyukan ku na kwarai domin lallai hakan na daga cikin sabuba na amsa adu'a ku tsanannta wurin adu'a a wurin rokon Allah ubangiji mai jin kai wurin dauke wan nan annoba  daga kasashe musamman ga kasashen musulmai , kuma ya dauke daga bayin Allah domin Allah ubangijin dukkan komai ne amma dan adam sunada rauni suna da gajiyawa ba su mallaki wani abu ba wa kansu na amfani ko na cutarwa Allah Madaukakin sarki ya ce (Allah ya halicci mutum cikin rauni) haka kuma Allah subhanahu wa ta'ala ya ce:(ku kirayi  Ubangijinku kuna masu kankan da kai da kuma a boye, lalle ne shi ba ya son masu wuce iyaka. Kuma kada ku yi barna a cikin kasa a bayan gyaranta, kuma ku kiraye shi saboda tsoro da kuma tsammani lalle ne rahamar Allah Makusanciya ce ga masu kyautatawa).

Allah ya sa min albarka ni da ku a cikin Alkur'ani mai girma.

 

Huduba ta biyu         

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mai rahama Mai jinkai Mabuwayi Mai hikima, ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode masa bisa abin da ya kwarara a gare mu na daga ni'imomi, da kuma tunkude musibu a gare mu da azaba na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya Ma'aboci daukaka da girma, kuma na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, ma'aboci dabiu na karamci, to ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga bawanka kuma ManzonKa Muhammad daiyalansa da sahabbansa wadanda suka taimakawa wannan addini mikakke.

Bayan haka ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa, ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.

Ya ku musulmai hakika Ubangijinku ya kirayeku da fadinSa (Ya ku wadanda suka yi imani ku tuba zuwa ga Allah tuba ta gaskiya, mai yiwuwa Ubangijinku ya kankare muku miyagun ayyukanku, kuma ya shigar da ku gidajen Aljanna koramu na gudana a karkashin su, a ranar da Allah bai kunyatar da Annabi da wadanda suka yi imani tare da shi, haskensu yana tafiya gaba gare su da jihohin damansu). Kuma Allah Madaukaki ya ce : ( ku tuba zuwa ga Allah gabadayanku ya ku wadanda suka yi imani ko zaku samu rabauta)

 Hakika Allah ya muku baiwa na tuba a wannan tsanani, lalle kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (lalle Allah ya fi farinciki da tubar bawanSa sama da mutumin da abar hawansa ta bace a cikin jeji ya neme ta har ya gaji sai ya kama barci a karkashin wata bishiya yana farkawa sai ga dabbar tsaye a kan shi, sai ya riki linzaminta ya ce : Ya Allah kai ne bawa na nine Ubangijinka ya yi kuskure sabo da tsaban farinciki.) muslim ne ya rawaito daga hadisin Anas Allah ya kara yarda a gare shi.

Kada ku warware tubanku da abin da ke kishiyantar ta, ku yawaita tilawan Alkur'ani a watan Alkur'ani, domin shi ne kalacen ruhi, zuciya na amfana da shi sama da komai a wannan wata, domin shine anbato mai hikima kuma mai shiryarwa ga tafarki mikakke, shi ne mai hukunci na gaskiya cikin abin da mutane suka saba a cikinsa.

Ya ku bayin Allah! Lalle Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce mai yawa.

 

  

 


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق