Hudubar masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
na 29/9/1441
Hudubar farko:
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah tsira da amincin Allah su tabbata ga manzonSa
Bayan haka
:
watan
ramadana ya kare , wanda Allah ya bamu labari cewa wasu 'yan kwanaki ne
kididdigaggu sai gashi ya wuce kaman kyabtawan ido, ya wuce kaman hasken
walkiya, hakika zukata sun kasance sun yi shaukin zuwan shi, ga shi a yau kuma
yana shelanta tafiya kuma yana juyawa yana mai ban kwana, ba abin mamaki ba ne
a samu zuciya ta samu nau'uka daban daban na abin da ta ke ji na daga cikin
labaran zuciya, muna jin falalan Allah a gare mu da ya shiryar da mu zuwa ga
musulunci kuma ya sanar da mu alkur'ani, kuma ya riskar da mu ramadana ya
taimake mu zuwa ga azumi da kuma tsayuwa, shi ne mai ni'imtarwa mai yawan
kyauta, Allah Madaukakin sarki ya ke cewa:(suna
goranta maka don sun musulunta ka ce kar ku min gori bisa musuluncin ku sai dai
Allah Shi ne zai goranta muku saboda ya shiryar da ku zuwa ga imani)
wan nan shi ne halin masu tafiya zuwa ga Allah suna shelantawa da dukkan ladabi
mai girma da daukaka da rusunawa da jingina ni'ma zuwa ga ma'bocinta (sai ya ce wannan falala ne na Ubangijina) wan nan
shi ne abin da ya dace duk wasu ayyukan kwarai a rufe da su, a fiskanci ayyukan
girmamawa da su (Dukkan godiya a gare shi ta ke a
duniya da kuma lahira hukunci ma naShi
ne kuma gare shi za ku koma) lallai Shi Madaukaki mai falala na
hakika da dukkan wani abu mai kyau ga halittunSa ,
An karbo
daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ba wani
ni'ma da Allah zai yiwa bawa sai bawan ya ce godiya ta tabbata ga Allah face
sai abin da aka bashi zai fi abin da ya rika) wan nan shi ne yanayin
halin 'yan aljanna a lokacin da suka kai kololuwa gurin buri da samun yardan
Allah sannan suka shiga aljanna harsunan su na daga murya da godiyan Allah Madaukaki
suna cikamake adu'arsu da shi da ayyuka na kwarai , Allah Madaukakin sarki ya
ke cewa (sai suka ce dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah da ya tafiyar mana da bakin ciki lallai Ubangijin mu mai yawan
gafara ne kuma mai yawan godiya)(wanda ya
bamu masauki a gidan dawwama daga cikin falalanSa , ba wani gajiya ko wahala da
zai shafe mu)
Gaggautawa
zuwa ga godiyan Allah da kyautata yabo bisa ga ni'mominsa a yayin kammala
wannan watan falala shi ne manhaji na musulunci da kuma taujihin alkura'ani ,
Allah Madaukakin sarki ya ce: (Domin ku cike adadin
kuma ku girmama Allah bisa ga abin da ya shiryar da ku ko za ku gode)
ya zo a hadisi wanda Bukari da Muslim suka rawaito shi daga Abu huraira Allah
ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce :(Mai azumi nada farin ciki guda biyu ,
farin ciki guda yayin shan ruwansa farin ciki guda kuma yayin haduwa da Ubangijinsa
)
Tabbatar da ma'ana ta yabo da godiya ta watan
ramadana alama ce ta kyautata zaton bawa ga Allah da kuma fatansa cewa Allah ya
karba mishi abin da ya yi na da'a kuma ya kankare mishi tawaya da aka samu a
aiki da kuma gafala na daga halaka da kuma jahilci , yayin sauke nauyi , hakika
ya zo a hadisul kudusi (Ni ina inda bawa na ya
zaceNi) idan bawa ya kyautata zato ga Ubangijin shi to ya lizimta a
gare shi da ya yawaita addu'a don Allah ya karba mishi da'an shi yana mai
ladabi tare da Allah da neman tabbatar da zaton shi da gaskiyan fatan shi.
Hakikanin
godiya a karshen watan ramadan shi ne gyaruwan aikin bawa da lazimtan shi ga
da'a ga Ubangijin shi da gaggautawa zuwa ga wurin samun yardar Allah , Allah
Mabuwayi da daukaka ya ke cewa(ku yi aikin
godiya ya ku mutanen Dauda , kadan ne daga cikin bayi Na su ke masu godiya)
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kan yi tsayuwan
dare har kafafuwarsa su kumbura sai a ce da shi kai da Allah ya gafarta maka abin
da ya gabata na daga zunubanka da abin da ya jinkirta? Sai ya ce : (Ashe ba zan zama bawa mai yawan godiya ba ?).
Musulmi wanda
Allah ya haskaka zuciyarsa a cikin watan ramadana ya kara fadada da imani ya
sha daga mabubbuganSa, ya koshi daga tabkinSa, ya yi tsayuwan daren Sa , ya
azumci wuninSa , to ba zai gushe ba yana tsere zuwa ga ayyuka na da'a har bayan
watan ramadana, ba zai yi sakaci ba wurin neman ayyuka na ganima wanda ya ci
daga dadinta a cikin azumin shi da kuma sallarsa da biyayyarsa, duk wanda ya
dandani dadin ganawa da Allah ya kuma dandani dadin imani a ramadana natsuwa da
kwanciyar hankali ya kwararo a cikin zuciyarsa to ba zai yi sakaci ba wurin barin wannan sa'ada din ya
tsere mishi, zai zame ne zuciyarsa na
ta'allake da Ubangijin shi kuma zai zame yana ta debe kewa da Ubangijin shi,
kuma tare da Allah kuma zuwa ga Allah, idan lokacin ramadana ya kare lallai
lokuta na alheri na bibiyan juna falaloli na Mai rahama ba a'a iya iyakance su
lokuta na da fifiko wurin kima da kuma lada a duk lokacin da aka samu nunfasawa
na wani lokaci da dama ta samu to mai
hankali zai yi gaggawa ne ya tashi zuwa gare ta, mai komawa zuwa ga Ubangijin
shi zai ribace ta, Allah Madaukakin sarki ya ce: (ka
yi sujada ka kusanto)
A dukkan
safiya da gari zai waye fage ne na yin hailala da kuma godiya da kabarbari da
kuma istigfari.
A dukka yammaci in ya sake duhun shi to lokaci ne na ganima wanda zai farauce shi, wanda ya san kimanta shi ne masu
yawan ibada a cikin dare wanda sassan su ke nesatan makwanci suna rokon Ubangijinsu
suna bisa halin tsoro da kuma tsammani.
Wadanda suka san hakikanin rayuwa da kuma kimanta
suna da iko lokutan su su zama duka lokuta ne na ayyukan alheri, za su kuma
rika kai komo cikin nau'uka na mubadara
ta hanyan ayyuka na kwarai da, yada ilimi da taimaka wa mabukaci da girmama
bako da kuma shafa kan maraya da kuma gyara da gina masallaci da kuma yalwata
nasiha da karfafan tsangayoyi na
alkur'ani da tarayya wurin gidauniya na alheri da kuma aiki bisa habaka kasa da
kuma daga al'uma, Allah Madaukakin sarki ya ce: (Duk
wanda ya ke son lahira kuma ya yi aiki don ita irin aikinta a halin yana mumini
to wadan nan ayyukan su za su zama abin godiya).
Musulmi ya
kan hadu da wani nau'i na bala'i ko annoba a zuciyansa ko iyalansa idan ya godewa
Allah kuma ya nemi ladan musiban a wurin Allah ya yi imani da abin da Allah ya
hukunta ya kaddara to Allah sai ya girmama mishi ladan shi, ya maida mishi da
mafi alheri kuma ya rubuta masa rahama da gafara da shiriya Allah Madaukakin
sarki ya ce:( lallai za mu jarabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da
tawaya na daga dukiya da rayuka da 'ya'yan itace, ka yi albishir ga masu hakuri
wadanda idan musiba ta same su sai su ce : ga Allah muke kuma gare shi za mu
koma, wadan nan suna da wani kyakkyawan ambato daga Ubangijinsu da kuma rahama
kuma lallai wadan nan su ne shiryayyu)
Haka na
zuwa ne a wani yanayi na annoba wanda ya sanya abu mai motsi ya zama ya natsu
ya mosta kuma abin da ya ke zaune gu daya, ya yi yawo a doron kasa ya sanya
zukata cikin tsoro da idanuwa kuru kuru
na daga abin da jiki ke kwanta dama, da abubuwa da ke faruwa na kamuwa da
cututtuka daya bayan daya da ake gani a wan nan yanayi na kunci mai tsanani
akan fiskanci ludufin Allah boyayye rahamomin Allah su kewaye mu sai Allah ya
kiyaye bayi daga wan nan annoba mai ragargazawa ya katange kasa daga rashin
lafiya mai halakarwa ya dauke bakin ciki daga al'uma tasirin shi a doron kasa
ya zamana dan kadan ne san nan ya tunkude shi da falalanSa ga Ubangiji wani abu
ne da ba mai wahala ba.
wannan shi
ne yaye bakin ciki mai girma, zai sanya idin mu ya zama zai zo gare mu nan kusa
cikin mafi kyan idi kuma wanda ya fi farin ciki da kuma jin dadi domin tufafin
da za mu sa sabo a cikin idi shi ne na tsoron Allah da kuma lafiya, abin hawa mai
laushi da za mu hau shi ne na aminci da zaman lafiya shakatawa da walwala shi
ne mu shaki tacecciyar iska wacce ta kubuta daga wan nan annoba da kuma farin
ciki na haduwan iyalai da 'yan uwa da makusanta da kuma makwabta, shi ne a samu
labarin suna cikin koshin lafiya suna cikin ni'ma, shin bayan wannan ganima
akwai wani abu kuma na nema ? ku tafi a doron kasa ku yi dubi zuwa ga halin da
wadan su su ke ciki, domin ku san kaye na hali da daukaka da ni'ima a kuma kima
na ludufi, abin mamaki da girman Allah da rahamarSa Mahalicci, lallai halarto da ni'ima da gode wa Allah da harshe
da zuciya yana sanya karin samun rahama da ludufi .
Huduba ta biyu:
Musulmi
yana cika watan ramadana ne yana mai godiya da farin ciki saboda riskan cikan
shi yana lullube da rahamar Allah yayin shan ruwan shi ni'man Allah da
falalanSa yana mai gaggawa zuwa ga jefa farin ciki a al'umansa, sai ya fitar da
zakkan fidda kansa domin tsarkakewa ga mai azumi daga kazanta da wasa kuma ya
farantawa talakawa rayi ya wajaba ga musulmi haka kuma ga duk wanda
musulmi ke daukan nauyin shi, mikdarin shi shi ne sa'i daga cikin abincin gari.
An karbo
daga dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi shi da mahaifin shi ya ce :(Manzon Allah ya wajabta zakkan fidda kai sa'i guda na
dabino ko kuma sa'i guda na sha'iri bisa ga bawa da da na miji da mace da kuma
yaro da babba na daga musulmai kuma ya umarni da a fitar da shi kafin fitan
mutane zuwa sallah). Ya halatta gabatar da shi da rana daya ko rana
biyu saboda abin da aka rawaito daga ibnu Umar cewa sun kasance suna badawa
kafun fita eidi da rana daya ko rana biyu.
Tare da dakatar
da sallah da aka yi a masallatai da kuma wuraren sallah na idi saboda wannan
annoban an shar'antawa musulmai sallan idi a gidajensu a jama'a ko kuma a
daidaiku, kuma za a fara kabarbari ne tun daga faduwan ranar daren idi sannan
idan aka sallace ta a gida to sai a yanke kabarbarin tare da shiga salla. Ana sallatanta
sifanta ne rak'a biyu ba tare da huduba ba za a yi kabbaran harama a farko
sannan a yi kabarbari guda shida bayanta, a rak'a ta biyu kuma za a yi kabbara
na tashi sannan kuma a yi kabarbari guda biyar bayanta , lokacin sallar idi na
fara shigowa ne tun daga bayan hudowar rana da kuma bullowanta da mikidarin
mashi biyu ko kuma da mikidarin abin da bai gaza minti ashirin ba kuma zai ci
gaba lokacin nata har zuwa lokacin sallan walaha kafin shigan lokacin sallan
azahar da kusan sulusin sa'a, hakika hani ya zo daga Annabi tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi na hani ga sallah a lokacin da rana ke hudowa.
Allah ya karba mana ayyukanmu na kwarai da ayyukan ku na kwarai.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق