ترجمة الخطبة
اسم
المترجم :أمين سعد عبد الله
اللغة : الهوسا
التاريخ : 15-9-1441هـ
Hudubar Masallacin Annabi Na shaikh
Ahmad Dalib 15/9/1441AH/7/5/ 2020AC
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa,
muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda
Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai
shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake
ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma
manzonSa ne. tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da aminci
tabbatacce.
(Ya ku
wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu
face kuna musulmai)
(ya ku
mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta
matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji tsoron Allah da ku ke roko
da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance mai tsaro ne a kan ku.)
(ya ku
wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara
muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah
biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta
mai girma.)
Bayan haka, lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi
alherin shiriya ita ce shiriyar Annabinmu Muhammad, kuma sharrin al'amura sune
fararrunta, kuma dukkan bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta.
Ku sani ya ku bayin Allah lallai ba makawa bin hanyar zuwa lahira dole
sai da ilimi wanda ke yaye wa zuciya makanci, da kuma aiki wanda zai dauke wa
mutun shamaki na basira da iklasi wanda zai kubutar da mutun daga hasara na
faduwa da kuma tsoro wanda zai sa mutun ya kiyaye bala'o'i na rudi.
Dukkan halittu matattu ne sai
malamai, malamai kuma dukkansu masu bacci ne sai masu aiki, masu aiki kuma
dukkansu rudaddu ne sai wanda suke masu
iklasi, su kuma masu iklasi suna cikin wani hadari mai girma (shin , kuma wanda ya kasance matacce, sa'an nan Muka rayar da
shi Muka sanya wani haske dominsa, yana tafiya da shi , yana zama kamar wanda
misalinsa yana cikin duffai , shi shi kuma ba mai fita ba daga gare su ? kamar
wancan ne aka kawata wa kafirai abin da suka kasance suna aikatawa).
Abin mamaki dukkan mamaki ga mutumin da ya ke aiki amma bai damu da
sanin abin da ke gaba gare shi ba na daga al'amari ko labari, ko kuma ya nemi
sanin abin da zai zo bayan mutuwa gaba gare shi ta hanyar nazari da dubi ga
dalilai da kuma wa'azuzzuka da ayoyi da kuma gargadi ba. (shin ba su yi dubi ba a cikin mulkin sammai da kasa, da kuma
abin da Allah ya halitta daga kome kuma akwai tsammani kasancewar ajalin su,
hakika ya kusanta? to da wani labari a bayansa su ke yin imani) ( wanda Allah ya batar, to babu mai shiryarwa a gare shi kuma
yana barin su a cikin batarsu suna dimuwa) abin mamaki ya kaiton
makanci irin na zuciyarsa (shin to, ba su yi tafiya
ba a cikin kasa domin zukata wadanda za su yi hankali da su da kunnuwa da za su
yi saurare da su, su kasance a gare su ? domin lallai ne idanu ba su makanta,
amma zukata wadanda ke a cikin kiraza su ke makanta).
Abin mamaki dukkan mamaki ga malamin da ba ya wa'azantuwa da abin da ya
sani na yakini sai abin da ya ke gaba gare shi na daga musibu masu girma da
kuma abubuwa na cikas da ke gaba masu fadi ya tsorata daga kasala ya gargadu
zuwa ga jahadi da kuma aiki (ka ce, shi (Alkur'ani)
babban labari ne mai girma. ku, masu
bijirewa ne daga gare shi) ya kaiton hijabin idanuwansa (Bone ya tabbata ga masu nakkasawa) (wadanda su ke idan su ka auna daga mutane suna cika mudu)(kuma idan sun auna musu , da zakka , ko da sikeli , suna
ragewa)(shin wadancan ba su tabbata cewa
lallai su , ana tayar da su ba?) (domin
yini mai girma) (yinin da mutane ke tashi
zuwa ga Ubangijin halitta).
Abin mamaki dukkan mamaki, ga mai aiki wanda ya sarayar da iklasi ya
sarayar da mabudin samun kubuta ta hanyar lalata zuciyarsa (ka ce, ''Ni mutum
ne kawai kamarku, ana yin wahayi zuwa gare ni cewa : lallai ne abin bautawarku
Abin bautawa guda daya ne, saboda haka wanda ya kasance ya na fatan haduwa da
Ubangijinsa, to sai ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bautawa
Ubangijinsa.) kaito da hasaran faduwan mutum ya rasa riba! (kuma aka halaka dukkan 'yayan itacensa, sai ya wayi gari yana
juyar da tafunansa biyu , saboda abin da ya kashe a cikinta , alhali ita tana
kwance a rassanta, kuma yana cewa , kaitona dadai ban tara wani da Ubangijina
ba!) (kuma wata jama'a ba ta kasance a
gare shi ba, wadanda ke taimakon sa baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon
kansa ba) abin mamaki dukkan mamaki ga mai iklasi wanda ba ya duba
zuwa ga mua'amalar Allah Madaukaki tare da masoyanSa da ManzanninSa wadanda su
ne masu nusar da halittu daga wurin Allah sai ya halarto da tsoronsu, ga masoyi
na farko yana cewa (kuma a lokacin da Ibrahim ya ce
,''ya Ubangijina! Ka sanya wannan gari amintacce, kuma ka nisata ni ni da
'ya'yana daga bautawa gumakai) ya na shaida tsoron su masoyi cikakke
yana ce da shi (kuma an yi wahayi zuwa gare ka da
kuma zuwa ga wadanda su ke gabaninka , ''lallai idan ka yi shirka hakika,
aikinka zai baci ,kuma lallai za ka kasance daga masu hasara.)
To ya kai mai rudin kansa (To, a yau ba za a
karbi fansa daga gare ku ba . kuma ba za a karba daga wadanda su ke kafirai ba
makomarku wuta ce , ita ce mai dacewa da ku kuma makomarku din nan ta munana )
(shin, lokaci bai yi ba ga wadanda su ka yi imani
zukatansu su yi tawaliu ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya ? kada
su kasance kamar wadanda aka baiwa littafi a gabanin haka sai zamani ya yi tsawo a kansu , saboda haka zukatansu su
ka kekashe, kuma masu yawa daga cikinsu fasikai ne) .
Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin Alkura'ani mai girma .
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya isa, tsira da aminci
su tabbata ga Annabi zababbe da alayenSa da sahabbanSa ma'abota da'a da kuma
cika alkawari, da kuma wanda ya bi su da kyautatawa kuma ya bi sawu, lallai
Allah ya kira ku da sunan imani kuma da tsoronsa ya kira ku Ya gargade ku game
da faduwa irin na mantuwa da kuma radadi irin na hasara ya kuma sanar da ku
tserewan yanayi da halaye a ranan komawa, girman tasirin Alkura'ani da an
saukar da shi ne a kan duwatsu , ya kuma sanar da ku da kamalan sunayenSa
Madaukaki da kyawawa.
(ya ku wadanda su ka yi imani ! ku bi Allah
da takawa , kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da
takawa lallai Allah , Mai kididdigewa ne ga abin da kuke aikatawa) (kuma kada ku kasance kamar wadanda suka manta Allah shi kuma
Ya mantar da su rayukansu, wadannan su ne fasikai) ('yan wuta da 'yan Aljanna ba su daidaita . 'Yan Aljanna su ne
masu babban rabo) (Da Mun saukar da
wannan Alkura'ani a kan dutse, da lallai ka ga dutsen yana mai tawali'u, mai
tsatsagewa saboda tsoron Allahh , kuma wadancan misalai Muna bayyana su ne ga
mutane, da fatan za su yi tunani) (wanda ya saukar da Alkur'ani shi ne Allah,
wanda babu wani abin bautawa face shi, masanin fake da bayyane, Shi ne Mai
rahama Mai jin kai) (Shi ne Allah, wanda babu abin bautawa face Shi Mai mulki
Mai tsarki, aminci Mai amintarwa , Mai tsarewa , Mabuwayi , Mai tilastawa, Mai
kamun kai, tsarki ya tabbata a gare shi daga abin da suke yi na shirka da shi)
(Shi ne Allah, Mai halitta Mai ginawa, Mai surantawa, yana da sunaye masu kyau,
abin da ke a cikin sammai da kasa suna tsarkake Shi , kuma Shi ne Mabuwayi ,
Mai hikima).
Tsarki ya tabbata gare Shi Madaukaki bai halicce ku don wasa ko kuma don kazanta ba sai dai kawai domin ku nemi gafaran Shi kuma domin a muku rahama (shin, to kun yi zaton cewa Mun halitta ku ne da wasa, kuma lallai ku zuwa gare mu ba za ku koma ba?) (Allah Mamallaki, Gaskiya, Ya daukaka babu abin bautawa face Shi, Shi ne Ubangijin Al'arshi , mai daraja) (kuma wanda ya kira tare da Allah wadansu abubuwan bautawa na daban , ba yana da wani dalili game da shi (kiran) ba , to hisabinsa yana wurin Ubangijinsa kawai lallai ne kafirai ba su cin nasara) (kuma ka ce, ''Ya Ubangijina ! Ka yi gafara Ka yi rahama kuma Kai ne Mafi alherin masu rahama).
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق