الأربعاء، 20 مايو 2020

FALALAR SALLAR DARE DA KARATUN ALKUR'ANI

 

اللغة : الهوسا

التاريخ 8/9/1441هـ

Hudubar masallacin Annabi  na shaikh Abdullah Bin Abdurrahman Albuaijan

8/9/1441 AH 1/5/2020 AD

 

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya sanya da'a gare shi ya zama dalili ne na samun yardarSa, ya sanya yardarSa kuma a matsayin dalili ne na rabauta da AljannarSa ya kuma datar da mumunai zuwa ga bauta masa, sai suka kauracewa ababan jindadi da sha'awe sha'awensu suka fifita samun yardarSa.

Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya abin godiya abin girmamawa, shaidawar da zan hadu da Allah  da ita a halin ina ni kadai na tilo. Na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne Allah ya isa Mai shaida. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci abin kari mai yawa.

Bayan haka, lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabinmu Muhammad dan Abdullah, kuma sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta,

ya ku bayin Allah ina muku wasiya da ni kai na da tsoron Allah Mabuwayi da daukaka, to ita ce wasiyar Allah ga mutanen farko da na karshe, (Hakika mun yi wasiyya ga wadanda muka baiwa littafi kafin ku da ku kan ku da ku ji tsoron Allah).

    Ya ku bayin Allah! Biyayya ga Allah ita ce mafi alherin ganima da abin ribata, kuma yardarSa ita ce mafi alherin riba da abin nema, Aljanna an kewaye ta da abubuwan ki, wuta kuma an rufe ta da abubuwan sha'awa, abin sani za ku samu ladan ku cike a ranar alkiyama, to duk wanda a ka nesatar daga wuta aka shigar Aljanna to hakika ya rabauta.

Ya ku masu azumi!

Allah ya karbi biyayyarku, ya gyara halayenku, ya datar da ku cikin abin da ya rage a wannan wata, ya kuma rubuta muku tabbatuwa  bisa da'a a gare shi a tsawon ranakun zamani.

Ya ku jama'ar musulmi!

Ramadan wata ne na ibada da tuba, watan neman kusanci ne da komawa ga Allah, wata ne  na tuba da dawowa ga Allah da ikhlasi da khushu'i da sujudi da ruku'i, wata ne na azumi da tsayuwa, wata ne na biyayya  da kyautatawa da karatun Alkur'ani.

Ya ku masu azumi!

Karbabbiyar ibada na da tasiri a imani, tasirinta na ga zuciya da rai , gyara niyya da tsarkake rayuka da takawa da ikhlasi da khushu'i  ga Allah Mafi daukaka.

Tasirinta da ke gabbai da jiki; kamewa daga ayyukan sabo da abin da aka haramta da jurewa gun aikata ayyukan alheri da da'a.

To ku sa Allah a idanuwanku cikin ayyukanku, to shi Allah bai dubi ga surorinku ko jikunanku sai dai yana dubi ne ga zukatanku ne da ayyukanku , so da yawa wani mai azumin baida wani abu a azuminshi sai kishin ruwa da yunwa da gajiya sau da yawa wani mai tsayuwan dare bai da wani abu na daga tsayuwan shi sai hana ido barci da wahala.

Ya jama'ar musulmai :

Lallai Allah ya saukar da Alkur'ani a watan azumi  sai yace: (watan ramadana ne wanda aka saukar da Alku'ani yana shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu daga shiriya da rarrabewa) kuma Allah ya ce : (lallai mu muka saukar da shi a daren lailatulkadri ) (wa ya sanar da kai menene lailatulkadri)(lailatul kadri mafi alheri ne  daga wasu watanni dubu) (Mala'iku da Ruhi suna sauka a cikinsa da izinin Ubangijinsu saboda kowane umurni) (sallama ne shi daren har fitar alfajiri) kur'ani ya sauka a daren lailatul kadari na  ramadana zuwa baitul izza a sama ta duniya san nan ya sauka zuwa doron kasa a rarrabe cikin shekaru ashirin da uku  gorgodon abubuwan da ke faruwa da kuma sabuban sauka, to karatun kur'ni a watan da aka saukar da shi , na daga cikin mafificin ayyukan kusanci  saboda haka ne Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana fiskantan karatun kur'ani a cikin watan ramadan Jibrilu ya kasance yana zuwa mishi a ko wani dare a cikin watan ya yi bitan kur'ani da shi .

An karbo daga Ibnu Abbas Allah ya kara yarda a gare su ya ke  cewa:( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance mafi kyauta cikin mutane kuma kyautansa ya  fi kasancewa ne a watan azumi a yayinda ya ke haduwa da Jibril , jibrilu ya kasance yana haduwa da shi a ko wani dare na ramadan sai ya yi bitan Alkur'ani da shi to Annabi na da yawan kyautan alheri a yayin da ya hadu da shi sama da iska da ake turowa) .

To ya ku bayin Allah ku riki karatun Alkur'ani  ku karanta shi da tajwidin shi kuma ku nemi fahimtar ma'anoninsa ku yi tadabburinsa  , to an karbo daga abdullahi dan Mas'ud Allah ya yarda da shia ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbat a a gare shi ya ce:(Duk wanda ya karanta harafi  yana da kyakkyawa , kuma kyakkyawa na da kwatan kwacinta guda goma, ba zan ce alif lal mim harafi ne sai dai alif harafi ne lam harafi ne mim harafi ne) Tirmizi ne ya rawaito shi kuma ya inganta shi , kuma aga gare shi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(lallai wan nan alkur'ani wani abin ci ne to ku koya daga wan nan abincin iya iyawan ku lallai wan nan alkur'ani igiyan Allah ne kuma haske ne mai bbayyanawa  komin kuma waraka ne mai amfani kuma kariya ne ga wanda ya yi riko da shi da kuma tsira ga wanda ya bishi ba zai zame ba har ya zama abin zargi, ba zai kuma karkace ba har ya zama abin mikarwa ,kuma abubuwan mamakinsa ba za su kare ba kuma yawan maimaita shi ba zai tsufar da shi ba to ku yi tilawarsa , don lallai Allah zai ba ku lada bisa ga tilawarsa kyakyawa goma ga ko wani harafi amma ni ba zan ce alif lam mim sai de da: alif, da lam, da mim …. )  Dabrani ne ya rawaito .

An karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara yarda a gare su ya ce : Mazon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Ana cewa ga ma'abocin Alkur'ani a ranar alkiyama , ka karanta ka haura kuma ka yi tilawa kamar  yanda ka kasance kana tilawa a duniya domin matsayinka tana a'ayan karshe da ka karantata) Tirmizi ne ya rawaito .

To ku karanta Alkur'ani bayin Allah kar ku kaurace masa , na hore ku da kar  ku da yankewa  alkur'ani, na hore ku kada manta  Alkur'ani don hakan hasara ne da nadama, da juyawan hankali ne da abin zargi.

Muna neman tsarin Allah  da mu kasance  cikin wadan da  Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  zai kai karan    su wurin Allah ,   sabo da kauracewa kur'ani da suka yi :-  (kuma Manzo ya ce : Ya Ubangijina! Lalle mutanena sun riki wannan Alkur'ani abin kauracewa).

Ya ku bayin Allah ! Mafi girman ambaton Allah Mabuwayi da Daukaka shine Alkur'ani,  barin karanta shi kaura ce masa ne  da kuma juya masa baya Allah madaukakin sari ya ce :- (Duk wanda ya  kauda kai daga ambato na  (Alkur'ani) , to lallai ne rayuwa mai kunci ta tabbata a gare shi  ,kuma  muna tayar da shi a ranar kiyama yana makaho.   Ya ce  Ubangiji '' don me aka tayar da ni makaho , alhali kuwa na kasance mai gani ?  . Y a ce '' kamar wancan ne ayoyin mu suka je maka  sai ka mance su ,  kuma kamar haka a yau ake mance ka.

An karbo daga Abu Musa Al-ash'ari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce:- Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-    (misalin muminin da ya ke karanta kur'ani  kamar misalin tanjarin ne kamshin shi na da dadi dandanon shi ma na da dadi ,   kuma misalin muminin da baya karanta kur'ani  kamar misalin dabino ne, bai da kamshi kuma dandanon sa na da dadi , kuma misalin munafiki da yake karanta kur'ani kamar turaren wuta ne  kamshin shi na da dadi kuma dandanon shi na da dadi) Buhari da Muslum ne suka rawaito .Hakika Magabata sun kasance suna kwadayin karanta kur'ani  da lura da ma'anonin shi  suna da wuridin da suke yi ko wani rana  ba sa yankewa daga gare ta musamman a wannan watan. 

Watan  ramadana da aka saukar da alkur'ani a cikin ta , to ku kwadaici yawaita tilawar sa kada  na'urori na zamani da shirye-shirye masu shagaltarwa su yi gogayya da shi  

  YA KU BAYIN ALLAH:

A halin kuna wannan yanayi to ku nemi magani da waraka   da karatun alkur'ani  domin shi waraka ne da rahama ga muminai .

 Ku dukufa a kan shi a gidajen ku, a lokacin da ku ke kadaicen ku ko a bayyanen ku , ku karanta shi kuma  ku saurare shi a sauran lokutan ku .

Kuma wanda hakan ya mi shi nauyi ,  ko karanta kur'anin ya gagara a gare shi  to, ya saurari tilawar sa , domin shi ma mai sauraron abokin tarayyan mai karantawa ne a lada da sakayya .

Allah yana cewa : (Idan an karanta Alkur'ani to ku  saurare shi  ku yi shuru ko za ku samu rahama)

 

 

HUDUBA TA BIYU

Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah Masanin gaibi Mai yafe zunubai da sauran kusakurai da laifuka , kuma Mai yaye bakin ciki yana  shimfida hanunSa da dare don mai laifin yini ya tuba ,  kuma yana shimfida hanunSa da rana don mai laifin dare ya tuba .

 

 

YA KU BAYIN ALLAH:

Ku yiwa kanku hisabi kafin a mu ku  hisabi , kuma ku auna ayyukanku  kafin a aunaku  kuma kafin ayi kira gare ku : lallai su dinnan ayyukanku ne muke  kididdige  mu ku , sa'annan mu cika muku ita  duk wanda ya samu alheri to, ya godewa Allah , kuma wanda ya samu koma bayan haka to, kada ya zargi kowa sai kansa.   

(Duk wanda ya aikata  wani aiki kyakkyawa kwatankwacin kwayar  zarra zai gani, haka  kuma duk wanda ya aikata mummuna kwatankwacin kwayar zarra zai gani) 

 

 

YA KU BAYIN ALLAH:

Tsayuwar dare kusanta ne ga Allah  ba mai kiyaye ta sai muminai , haka kuma sunna ce da ba mai juriya  a kanta sai masu tsoron Allah ,   (Wadan da suke kwana don Ubangijinsu  suna  masu sujada da tsayuwa )  

Wadan da Allah ya ce  game da su :- (sasannin su  na nisanta daga wuraren  kwanciya ,  suna  kiran  Ubangijin su bisa ga tsoro da tsammani,  kuma suna  ciyarwa daga abin da muka azurta su . )

Sabo da haka  wani rai  bai san  abin da  aka boye  musu ba , na sanyin idanu , domin  sakamako  ga abin da suka kasance  suna aikatawa .

Wadan da Allah ya daukaka su (Lalle masu takawa suna a cikin lambunan ita ce  da maremari. Suna masu karbar abin da Ubangijinsu ya ba su ,  sun kasance  masu kyautatawa  a gabanin  haka (a duniya).  Sun kasance a lokaci kadan na dare suke yin barci . Kuma a lokutan asuba suna ta  yin istigfari)

Bayin Allah lokacin yin Tahajjud cikin dare  shi ya fi sabo da lokuta irin na kusanci Allah Madaukakin sarki ya  ce :- (Lalle ne tashin dare  shi ne  mafi  tsananin natsuwa ,  kuma mafi daidaituwa  ga magana )

Kuma lokaci ne da a cikin shi  Allah yake saukowa zuwa  saman duniya yana kira; shin akwai mai

roko na amsa mishi, shin akwai mai neman gafara na gafarta masa ? shin akwai mai tuba na karbi tubansa ? , kuma lokaci ne wanda ake bude kofofin sama ana amsa adu'a.

 karatun kur'ani shi ne mafi girman kusanci da munini zai  nemi kusanci da shi a wan nan lokaci, maganan Allah da kuma salla, mafi lokacin da kuma bawa ya fi kusa da UbangijinSa shi ne a lokacin da yake sujada (shin, wanda  ya ke mai tawali'u sa'o'in dare , yana mai sujada kuma yana mai tsayi ga sallah yana tsoron  lahira kuma yana fatan rahamar ubangijinSa  ).

Mafificin tsayuwa shi ne tsayuwan dare (sallar nafila) na ramadana, shi ne ya fi karfi a cikin sunnoni kuma na daga cikin mafificin nafilfilu, to an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Duk wanda ya yi tsayuwan ramadana yana mai imani kuma da neman lada za a gafarta mishi abin da ya gabata na daga zunuban shi kuma wanda ya yi tsayuwan lailatul kadri yana mai imani da neman lada za a gafarta mishi abin da ya gabata na daga zunubansa) ya zo a ckin sahihu muslim daga Urwatu dan Zubair cewa Ummul mu'minina A'isha Allah ya kara yarda a gare ta ta bashi labarin cewa:( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fita cikin dare sai ya yi salla a masallaci , sai wasu mutane su ka bi sallansa suka yi koyi da shi sai  da aka wayi gari sai mutane suka bada labarin hakan sai mutane suka hallara   sama da wadancan sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fito a dare na biyu sai mutane suka yi koyi da sallanSa sai mutane suka wayi gari suna ambaton hakan sai mutane suka cika masallaci a wannan dare na ukun sai Annabi  ya fito ya yi sallah sai mutane suka yi koyi da sallan shi yayin da aka zo dare na hudu masallacin ya kasa daukan jama'a Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai bai fito ba har zuwa lokacin da aka fita zuwa sallan asubahi yayin da aka kare sallan asuba sai ya juyo ya fiskanci mutane san nan ya yi Tashahhudi (Ashhadu alla ilaha illaallah wa ashhadu anna muhammadarrasulullah) sai ya ce : bayan haka lallai bai boyu mini ba sha'aninku na daren jiya sai de na tsoraci kar a farlanta muku sallan dare ne ku gagara yinta).

Mutane sun kasance bayan haka suna sallatanta  jama'a kashi –kashi, kuma  a daidaiku har zuwa lokacin da Umar dan kaddabi Allah ya kara yarda a gare shi ya hada su a mai karatu guda daya ,

An karbo daga Abdurrahman dan Abdu Alkari cewa ya ce : na fita tare da Umar dan kaddabi a cikin watan ramadana zuwa masallaci sai ga mutane su na warwatse a rarrabe wan nan na salla shi kadansa wasu jama'a  na  koyi da sallan sa , sai Umar ya ke cewa wallahi ; ni ina ganin da kun hada wadan nan mutanen bisa ga makaranci guda daya da zai fi dacewa sai ya hada su ga Ubayya dan ka'ab .

Bayan haka ya ku bayin Allah duk wanda niyarsa ta kasance ta gaskiya gurin azama ga yin salla a daya daga cikin masallatayya biyu masu alfarma,  ko wasunsu na daga masallatayya , amma ; hakan ya gagara yiwuwa a gare shi ko wani abu ya yi shamaki tsakanin shi da hakan sai ya yi salla a gidan sa to lallai ladansa na nan cikakke a rubuce insha Allahu ; domin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa:( lallai abin sani kawai ga ko wani mutum yana da abin da ya nufa ) kuma ya ke cewa :(Duk mutumin da ya himmatu da aikata wata kyakkyawa bai samu aikatata ba to za a rubuta mishi kyakkyawa guda) Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa : (Idan bawa ya yi tafiya ko ya yi rashin lafiya to za a rubuta mishi kwatankwacin abin da ya kasance yana aikatawa a halin yana mazaunin gida mai lafiya) .

Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa yayin da ya kusanto Madina yana dawowa daga yakin tabuka( lallai a garin Madina akwai wasu mutane da ba ku tafi wata tafiya ba ko kuma kuka keta wani kwari ba face kun yi tarayya da su a lada sai suka ce: ya Manzon Allah ahalin suna Madina ? sai ya ce : E, suna Madina uzuri ne ya hana su )

 to ku yi albishir     

 

  

  

   

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق