الأحد، 5 يناير 2020

BARNA A KASA DA BAWA DUKIYA KARIYA A MUSULUNCI


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Husain bin Abdul'aziz Al- Ashaikh 8-5-1441Ah /3-1-2020Ac

Na daga cikin ginshiki na yanke a wannan addini namu akwai haramcin cin kazantacciyar dukiya, na daga cikin mafi munin dukiya na haram ribatar da wasu ke yi a ma'aikata ko watanta na yin awun gaba da dukiyar al'uma (sata) ko yi ma dukiyar ta'annuti, ta kowace fiska a ka yi ta ko ta wace hanya aka bijiro da ita. Allah Madaukakin sarki ya ce (ya ku wadanda suka yi imani kada ku ci dukiyarku  a tsakanin ku bisa bata sai dai ta hanyar kasuwanci bisa yarjejeniya daga gare ku.)  
To dukiyar kasa asalinta tana da alhurma sabo da mallakan al'uma ne baki daya, ana sarrafa ta ne wajen amfanin kowa da kowa, da maslahohin da ake tarayya a kanta.
To duk wanda ya riki wani aiki, kowani irin aiki ne to shi abin tambaya ne gaba ga Allah na dukkan nauyin da aka dora masa, to ba ya halatta ya yi gaban kansa a ciki face abin da ya zo daidai da koyarwar shariar Allah a kankanin abu ne ko babba, sawa'un cikin abu mai kima ne ko mara kima, da kuma abin da tsari ya shirya don cinma maslahohi na gabadaya da amfani iri iri na kowa da kowa.
Lalle sakaci cikin shanin kowane dukiya yana komawa ne ga bangaren wanda ya yi sakacin ko da wani ma'aikaci ne kuwa wannan laifi ne a mahanga na sharia tsarkakakkiya, haka ma yin rufa-rufa ga wani sabo da dangantaka ko abokantaka ko don neman wani anfanin kai, to duka sun shigo cikin satan dukiyar al'uma, kuma yana cikin barna a doron kasa da ha'intar shugaban kasa jagoran musulmai da kuma ha'intar al'uma, sakamakon abin da wannan ha'inci ya kumsa na hadura da ke barazana ga zaman lafiyar al'uma da tattalin arzikinta da habakanta da ci gabanta da yalwanta. Allah Madaukakin sarki ya ce (Duk wanda ya ci gululi zai zo da abin da ya ci na gululi  ranar alkiyama sa'annan a cika wa kowane rai  sakamakon abin da ya aikata kuma ba za a zalunce su ba).
Ana cewa  gallar rajulu fa huwa  yagullu wato mutum ya yi gululi idan ya yi ha'inci, Al'aghlal : shine cin amanar wani nauyi da aka dorawa mutum wanda ya hada dukkan nau'ukanta, kuma ana fassara ta da satan dukiyar al'uma ta dukkan fiskokin sata, sabo da haka ne a ke cewa ga mahauci ya yi gululi idan ya saci wani abu na nama bayan ya dauki fata.
   
   Allah Madaukakin sarki ya ce (kada ku yi barna a ban kasa bayan an gyara ta.)
Al'uma ba zata ta ba gyaruwa ta yi kyau ba sai kowa ya tashi da nauyin da ke kan shi na amana bisa yanayi mafi kyau, a yi taimakekeniya gurin kiyaye dukiyar al'uma, ta kowace hanya da ta sawwaka, Allah Madaukakin sarki ya ce game da AnnabinSa yusuf   (ka sanya ni a kan taskokin kasa, lalle ne ni, mai tsarewa ne, kuma masani.)
 Haka kuma a kissar musa game da yaran mata biyu na shuaibu ( ya Baba ka bashi aikin kodago, lalle ne mafi alherin wanda ka bawa aikin kodago shi ne mai karfi amintacce.)
  Lalle ribatar dama na aiki ko waninsa don a yi awun gaba da dukiyar al'uma ba bisa halacci ba na daga cikin manyan laifuka na zunubai da kuma munanan al'amura, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle wasu mutane na kutsawa cikin dukiyar Allah ba tare da hakki ba,to wuta ta tabbata a gare su ranar alkiyama) Buhari ne ya rawaito.
Ibnu Hajar Allah ya masa rahama yace : ( wato suna barna a dukiyar musulmai).
Lalle kalmar malaman fikihun musulunci ta nassatan cewa dukiyar al'uma kamar dukiyar maraya ne wurin wajabcin kiyaye ta, da haramcin dauka daga gare ta, da matsanancin kwadayin tafiyar da ita a gurarenta da suka dace ba tare da yin sakaci ba ko tawace fiska.
Ya 'Yan uwa a Musulunci
Na daga cikin abubuwa na bayyane da ke faruwa daga wasu ma'aikata na gabatar da wasu a matsayi da fifita su a kan wasu ba tare da cancanci ba, tare da fakewa da wata doka da ta fito daga shugaban kasa, don tabbatar da maslahar kowa da kowa na daga 'yan kasa, sai wannan ma'aikacin ya riki wannan kamar wata garabasa yana zaton tamkar dukiyarsa ne na aljihunsa, sai ya gabatar da wanda bai cancanta ba bisa wanda ya cancanta. Na daga cikin irin wannan akwai sakaci da wasu ke yi wajen bada kwangila ba bisa ka'ida ba, ko don maslahar kai, da wuce gona da iri wajen sanya farashin aikin, wanda in da na kan shi ne bai zai yarda da haka ba. Yana daga cikin sakaci na rashin kulawa  da dukiyar al'uma kamar lambuna da asibitoci da wuraren shakatawa  da hanyoyi da makamantarsu.
Yana daga ciki amfani da abin da yake mallakar hukuma ne wurin bukatun kai ba tare da izini da ke bisa tsari ba daga shugaban kasa.
Na daga cikin sakaci da wasu ke yi akwai tafiyar da magani  na kasa da makamantarsa da raba shi ba ga bigerin shi da ya dace ba,na daga ciki akwai kasuwantar da daukan aiki da cin riba a cikinsa, ko srayar da lokacin aiki ko jinkirta abin da aka dorawa mutum na aiki ta fiskar da ba haka ya dace ba, wadannan da makamantarsu na cikin nau'uka na barna, kuma ha'intar jagoran al'umar musulmi ne da ita kanta al'umar sabo da abin da ke ciki na barna  mai girma da sharri mai fadi wanda zai haifar da cutarwarsa mai tsanani, kuma zai kawo cikas ga ci gaban kasa da habakarta da ma mutanenta    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle sau da yawa wani na kutsawa cikin dukiyar Allah da manzonSa cikin abin da ransa ya so ranar alkiyama bai da wani abu sai wuta.) Tirmizi ne ya rawaito kuma yace Hadisi ne Hasan sahih, kuma Ibnu Hibban ma ya rawaito shi a littafinsa Sahih da sanadi ingantacce.

Ya ku bayin Allah
Lalle abin da yak e wajibi ga duk wanda ya biye wa ransa abin da ya raya masa har ya yi gaba da fadi da dukiyar al'uma ta ko wace irin hanya ce daga cikin hanyoyi da ya koma ga Ubangijinsa ya tuba ga Mahaliccinsa ya rabu da wannan kudin haramun ta hanyar maida shi ga taskar kasa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : : (Yana kan mutuum abin da ya sata har sai ya mayar da shi).Ahmad da Abu Dauda da Tirmizi ne suka rawaito kuma Tirmizi ya ce Hadisi ne ingantacce.

Malaman fikihu sun yi tarayya kan cewa duk wanda ya lalata wani abu na dukiyar al'uma to dole ne ya biya haka kuma in ya dauki wani abu daga ciki ba tare da hakki ba to ya dawo da shi ga taskar kasa wato Baitul mali na musulmai.
Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kafa mana wata ka'ida  ga duk wanda ya rike wata amana na musulmai da kada ya ribaci wani abu na aikin hukuma da makamancinsa ya yi amfani da shi cikin maslahar kansa, wannan shi ake cewa ilimin tsarin gudanarwa  Tushe da bada kariya ga dukiyar al'uma, sai yace ga wanda ya je tattaro dukiyar zakka bayan yace wannan naku ne wannan kuma an bani kyauta ne :   (To me ya sa dayanku ba zai zauna a gidan iyayensa ba ya ga ko za a kawo masa kyauta ko aa, na rantse da wanda rai na ke hanunSa dayanku ba zai dauki wani abu ba face ya zo da shi ranar alkiyama yana dauke da shi a wuyarsa.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Ku ji tsoron Allah yak u bayin Allah ku yi taimakekeniya dukkanku wurin kiyaye dukiyar al'uma ta dukkan hanyoyi da za ku iya yin hakan ku kiyaye kada ku yi sakaci da hakan Allah Madaukakin sarki yace : (ku yi taimakon juna bias da'a da takawa kada ku yi taimakekeniya a kan laifi da gaba)
Duk wanda ya biye wa ransa wurin sabo ko wani irin sabo ne da ya sani in ya faku daga idon mutane to fa  Allah na tsinkayar sirrinsa da bayyanensa ku tuna fadin Allah Madaukakin sarki : (ku sani lalle Allah yana sanin abin da ke cikin zukatanku to lalle ku kiyaye shi) da fadinSa  : (ya san maha'intar idanuwa da abin da zukata ke boyewa.)
Na daga cikin nusarwar Manzon Allah : (Duk namar da ta tsiro daga haram to wuta ce ta fi dace wa da ita). Kada ka gabatar da duniya mai karewa a kan lahira mai wanzuwa, kada ka shigar da wani abu ga kanka da iyalanka sai halal mai tsarki da dukiya tsarkakakkiya.
Ya zo cikin kissar yaron da mashi da ba a san daga ina ba ya kashe shi a yakin khaibar mutane na cewa barkan shi da samun Aljanna sai  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (A'a  ahir, na rantse da wanda rai na ke hanunSa lalle bargon da ya dauka a ranan khaibar kafin a raba ganima na babbaka da wuta a kan shi). Buhari da Muslim ne suka rawaito.
An rawaito daga Abubakar :"Duk wanda ya nemi arziki ta hanyar haram to zai rasa albarkan, ba za ka ga wani gurbi na kwarai ba a dukiyarsa idan ya ciyar da dukiyarsa gurin abincinsa to zai hadu da ukubarsa  a lahira, idan ya ciyar da iyalansa da shi to hakika  ya ha'ince su bai kyauta musu  ba, kuma ba abin mamaki ba ne in dansa ya zama mara biyayya a gare shi. Halayen wadanda yake daukan nauyi ya lalace, suka zama kwatankwacinsa kuma ya hadu da alhakin abin da ya aikata a rayuwarsa ta duniya kuma azabar lahira ta fi tsanani."

Huduba ta biyu
Ya tabbata daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : (Kafafuwan bawa ba za su gusa ba a ranar alkiyama har sai an tambaye shi game da rayuwarsa yadda ya tafiyar daita, da iliminsa cikin abin da ya tafiyar da shi da dukiyarsa ta wacce hanya ya same ta kuma ta yaya ya kasha ta, da jikinsa ta yaya ya tsofatar da shi).
Ku tsarkakar da hanyar ku ta neman abinci ku nesanci kazantattun hanyoyi za ku tsarkaka ku rabauta, za ku yi nasara kuma ku ji dadi.
Ibnu Taimiyya Allah ya masa rahama yace: "Abinci na hadewa ne ya cakudu da jiki  ya tsiro da shi sai ya zama kamar sinadari ne nasa, idan abincin ya zaman a kazanta ne sai jikin ma ya kazance sai wuta ta wajaba a gare shi, sabo da haka ne Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi y ace : (Duk namar da ta tsiro daga haram to wuta ce ta fi dace wa da ita). Aljanna tsarkakakkiya ce bam ai shiganta sai mai tsarki."
Abin da ake nufi da ci ya kunshi da wani abu da ya ke amfana da shi a kan saya a ji dadi a wannan rayuwa.  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق