الجمعة، 24 يناير 2020

FALALAN GARIN MADINA


Hudubar Masllacin Annabi na SheikhAbdullah Bin Abdurrahman Abuaijan   29-5-1441AH 24-1-2020 A
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa kuma muna neman taimakonsa muna neman gafararsa
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu  da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, yana halitta abin da ya so kuma ya zabi abin da ya so, wanda ya kagi sammai da kasa, komai a kaddare ya ke a gare shi, na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne amintacce, cikamakin Annabawa da manzanni, ya isar da sako, ya sauke amana  ya kuma yi nasiha ga al'uma, ya yi jahadi don Allah cancancin jahadi har mutuwa ta zo mishi, Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa baki daya.
Bayan haka,
Mafi alherin zance shine maganar Allah, mafi alherin shiriya shi ne koyarwar Annabi Muhammad, mafi sharrin al'amura shine fararrunsu, kuma dukkan bid'ah bata ce, kuma dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah ku ji tsoron Allah cikin umarninsa ku hanu daga abin da ya yi hani a kai ya kuma tsawatar. Ku sani duk wani babba da karami abu ne rubutacce a littafi  (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah kuma rayi ya yi dubi ga abin da ya gabatar don gobe, ku ji tsoron Allah lalle Allah Masani ne ga abin da ku ke aikatawa)
Ya ku jama'ar musulmai!
Allah kan zabawa fifiko mahalli da wuri kamar yadda ya ke zaba mishi lokaci da zamani, da ahali, da mataimaka, hakika Allah ya fifita awasu sassa a doron kasa sai suka zama sune mafi daukakan garuruwa kamar yadda ya sanya makka masaukar wahayi, kuma alkibla ga musulmai, kuma ya sanya ta uwar alkaryu kuma gari mai aminci da masallaci mai alfarma, gurin da zukatan mumunai ke karkata zuwa gare shi.
Garin Madina ya samu daukaka ne sabo da hijiran Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a nan ne musulunci ya yadu, ana ce da shi Daiba
Zama ya yi dadi a cikinshi tsakanin duwatsun shi biyu harami ne kuma shi ne masulala na I'mani da mafakarsa da masaukinsa kuma da makoncinsa da mabinnansa
Ya ku bayin Allah :
Hakika Allah ya daukaka garin madina ya fifitashi kuma ya umarci annabinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da ya yi hijira zuwa gare shi ya haramta abinda ke tsakanin duwatsun shi biyu ya tsine wa duk wanda ya yi barna a cikin shi kuma kokuma  ya bada mafaka ga mabarnaci a cikin shi to ku bawa garin hakkin shi kuma ku ji alhurman da ya ke tattare da shi  an karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Madina  harami ne daga kaza zuwa kaza ba a'a yanke itaciyansa ba a'a farsar da barna a cikinsa to duk wanda ya farar da barna a cikinsa to tsinuwan Allah ta tabbata a gare shi da mala'iku da mutane baki daya) Buhari ne ya rawaito
An karbo daga A'mir dan Sa'ad daga baban shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (lallai ni na haramta tsakanin duwatsun garin madina guda biyu da atsinke kayansa ko a kashe abin farautansa ) Muslim ne ya rawaito
Kuma an karbo daga Aliyu Allah ya kara yarda a gare shi lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (garin Madina haram ne daga  A'ir zuwa kaza duk wanda ya farar da barna a cikinsa to tsinuwan Allah ta tabbata a gare shi da Mala'iku da mutane baki daya ba za a karba mishi nafila ko farilla ba ) Buhari ne ya rawaito
Ya jama'ar musulmai
Madina masulala ne na i'mani Allah ya ambace shi da gida da kuma i'mani, a cikinsa ne alkura'ani ya yi ta sauka mai dumbin yawa, a ciki ne aka shar'anta hukunce hukunce, rukunnai suka kafu, zaman lafiya ta tabbatu,   
   Daga nan ne tutocin musulunci suka taso a ka bude garuruwa, Allah ya daukaka addininSa ya taimaki bawanSa ya rusa makiyanSa,
Daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lalle imani na sulalewa zuwa Madina kamar yadda maciji ke sulalewa zuwa raminsa.) Muslim ne ya rawaito.
Madina sulke ne mai bada kariya, kuma garkuwa ne mai tsawo, ya kore kazantarsa yana tsarkake mai dadinsa, mala'iku na tsaronsa daga kofofinsa, firgicin Masih-Addujjal ba zai shige shi ba, ko annoba, daga Anas dan Malik, Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ba wani gari face dujjal zai taka shi face Makkah da Madina, ba wani kofa daga cikin kofofinta face Mala'iku na jere cikin sahu suna kare su, sannan Madina zai kada da mutanen cikinsa girgizawa uku, sai Allah ya fitar da duk wani kafiri da munafuki,) Buhari ne ya rawaito.
Daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (A kofofin Madina akwai Mala'iku annoba ko dujjal ba zai shiga garin ba) Muslim ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah ! ma'abocin Kazanta ko kaidi bai da mazauni a garin Madina, amincin Allah ya tabbata a gare shi,
Daga Aisha diyar Sa'ad ta ce na ji Sa'ad Allah kara yarda a gare shi ya na cewa, na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya na cewa :Ba wanda zai yi wa mutanen madina kaidi face ya narke kamar yadda gishiri ke narkewa a ruwa,) Buhari ne ya rawaito.
An karbo daga Jabir Allah kara yarda a gare su ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : Madina tamkar zuga zugi ne ya kore kazantarsa ya tace mai tsarkinsa.) Muslim ne ya rawaito.  
Lalle Ibarahim ya haramta Makkah ya mar adu'a da albarka, kuma lalle Annabi ya haramta Madina ya yi mar adu'a da ribin abin da Annabi Ibrahim ya roka wa mutanen  Makka An karbo daga Abdullahi bin zaid Bin Asim cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( Lalle Ibrahim ya sanya alfarma ga Makka ya yi adu'a ga mutanenta, lalle ni kuma na sanya alfarma ga Madina kamar yadda Ibrahim ya sanya wa Makka, ni kuma na roki Allah game da sa'in madina da mudunsa da ribin abin da Ibrahim ya roka wa mutanen makka) Muslim ne ya rawaito.  
   Daga Anas -Allah ya kara yarda a gare shi- daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ya Allah ka sanya albarka ga Madina ribin abin da ka sanya a makka).  Buhari ne ya rawaito.

Ya ku bayin Allah!
Lallai Madina ya kasance mafi soyuwan gari ga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana nuna masa kauna da wafa'i kuma yana bayyana hakan karara An karbo daga A'isha Allah ya kara yarda a gare ta tace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ya Allah ka sanya mana kaunar Madina kamar yadda ka sa mana kaunar Makka ko ma sama da haka. Ya Allah ka sa albarka ga sa'inmu da mudunmu ka inganta mana shi, ka kaurar da Annoban zazzabinsa zuwa juhfa)  Buhari ne ya rawaito.
   Daga Anas -Allah ya kara yarda a gare shi- idan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya dawo daga tafiya ya hangi gine –ginen Madina sai ya saki dabbarsa in yana kan dabbarsa ne sai ya kada ta sabo da kaunar Madina.) . Buhari ne ya rawaito.
Ya kasance idan ya fiskanto Madina sai ya kara sauri idan dutsen Uhud ya bayyana gare shi sai yace : wannan dutse ne da ya ke sonmu mu ma muna son shi,
An karbo daga Abu Humaid yace mun fita tare da Manzon Allah a yakin tabuka ya koro hadisin sannan ya ce : sai muka fiskanto har muka zo wadil kura sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :( Lalle ni zan kara sauri wanda ya ke so cikin ku to ya yi sauri tare da ni wanda ya so kuma ya zauna, sai muka fita har muka kusanto Madina sai yace : Wannan Daba ne wannan dutsen Uhudu ne shi dutse ne da yana son mu muna son shi). Muslim ne ya rawaito.
Hakika zukatan masu ziyara ta ta'allaku da Madina kuma ya bar wasu abubuwa na tarihi a zukatansu na  tsananin kauna sai zukatansu ta tausasa zuwa ga garin suna masu tsanani shauki , ya Allah ka sanya mu daga cikin masu son sa (garin ke nan)
Ya jama'ar musulmai :
Madina shi ya fi muku alheri kar ku ki shi   Allah ya zabe shi ga Annabin ku to ku zabi abinda ya zaba ku ladabtu da kusanci ku san hakkin makobci an karbo daga abi  Zuhair Allah ya kara yarda da a gare shi ya ce  na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa (za a bude garin yaman wasu mutane za su zo suna kora dabbobinsu suna daukan iyalansu da ma wadanda suka biye musu, Madina yafi alheri agare su da sun sani za abude Sham sai wasu mutane su zo suna kora dabbobinsu sai su dibi iyalansu da ma wadanda suka musu da'a alhali Madina yafi alheri a gare su da sun kasance suna sani kuma za a bude  garin Iraki sai wasu mutane su zo suna kora dabbobinsu sai su dibi iyalansu da ma wadanda suka musu da'a alhali Madina yafi alheri a gare su da sun kasance suna sani) Bukari ne ya rawaito
An karbo daga ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Duk wanda zai mutu a Madina to ya mutu a cikinsa lallai ni  zan yi  ceto ga wanda ya mutu a cikin shi ) Tirmizi ne ya rawaitoshi kuma ya inganta shi
An karbo daga A'mir dan Sa'd daga babansa Allah ya kara yarda a gare su ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Madina ya fi alheri a gare su da sun kasance suna sani duk wanda ya bar garin halin ya tsani garin to Allah zai sanja shi da wani wanda ya fi alheri ba wani da zai tabbata a ciki ya yi hakuri da  wahala da tsanani irin nashi face na kasance mai ceto a gare shi ko mai shaida a gare shi ranar alkiyama) Muslim ne ya rawaito ,Allah ya samini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma

Huduba ta biyu  
Ya ku bayin Allah
  lallai Madina na da daukaka da falala to ku nemeshi da alhurma da kima da wasu laduba da ya ya wajaba a yi ladabi a iyakoki na harami dama masallacin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi haka nan kuma da wurinda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke lallai adabi tare da shi yana raye kamar yimishi ladabi ne a bayan ya rasu hakika Allah ya umarci a yi ladabi gaba gare shi a kuma yi kasa da murya , Allah madaukakin sarki ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani kada ku sha gaban Allah da Manzonsa ku ji tsoron Allah lallai Allah mai ji ne  masani )(ya ku wadanda su ka yi I'mani kar ku daga sautukanku sama da sautin Annabi kada kuma ku bayyana zance a gare shi kamar yanda sashinku ke daga murya ga sashi don kada ayyukanku su rushe a halin baku sani ba)( lallai wadanda su ke kankan da sauti gaba daManzon Allah wadan nan su ne wadanda Allah ya jarabi zukatansu da takawa suna da wata gafara da lada mai girma )(lallai wadanda su ke kiranka a bayan dakuna mafiya yawansu basu da hankali ) (da a ce sun yi hakuri har ka fito zuwa gare su da ya kasance mafi alheri a gare su Allah mai gafara ne mai jin kai )
ku ladabtu ya ku bayin Allah a gaba gare shi da kyakyawan laduba an karbo daga Sa'ib da yazid ya ce : na kasance ina tsaye a masallaci sai wani ya jefeni da tsakuwa sai na duba sai naga Umar dan kaddabi ne sai ya ce je ka taho  min da wadancan mutane guda biyu sai na taho mishi da shi sai ya ce : ku waye ? ko kuma daga ina ku ke sai suka ce : daga garin Dayif sai ya ce : da kun kasance mutanen garin Madina ne da na jiyar da ku a jikinku (da na azabtar da ku) kuna daga muryan ku a masallacin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ? ) Buhari ne ya rawaito .
Allah ka daukaka musulunci da musulmai .      

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق