الجمعة، 24 يناير 2020

SAKAMAKO MAI DACEWA


Hudubar Masllacin Annabi na SheikhAbdulmuhsin Bin Muhammad Alkasim  15-5-1441AH 10-1-2020 A
Hudubar farko
Sakamako mai dacewa
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa kuma muna neman taimakonsa
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu  da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya,kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.

Bayan haka, ku ji tsoron Allah -ya ku bayin Allah- cancancin tsoronSa, ku yi murakabarSa a halin sirri da ganawa,
Ya ku musulmai!
Allah ya kagi halittar halitu sai ya kyautata abin da ya sana'anta, tsarki ya tabbata a gare shi ya kuma kyautata addininSa da abin da ya shar'anta, Mai hikima ne kuma Masani, Adili ne Mai jinkai, cikin halittarsa da umarninSa akwai sunnoni da basu sabawa ko sauyawa game da halittunSa, daga ciki akwai sakawa bayi  daidai da ayyukan da suka yi, in na alheri to da alheri in na sharri to da sharri, (Sakamako mai dacewa) da kaddara da sharia duk sun yi taron dangi bisa hakan, Allah Madaukakin sarki yace : (To wanda ya aikata wani aiki  gwargwado nauyin zarra na alheri to zai gan shi. To wanda ya aikata  wani aiki  gwargwado nauyin zarra na sharri to zai gan shi).
Allah ya gandaya ladaddaki masu yawa ga ayyukan alheri wanda yake irin su kuma daidai da su, sakayyar kan kasance daga jinsin da'ar , shehun musulunci Ibnu Taimiyya  Allah ya masa rahama ya ce: (sakayya a ko yaushe daga na kasancewa daga jinsin aikin da  mutum ya yi ne).kuma babu wata sakayya ga wanda ya kyautata sai kyautatawa Allah Madaukakin sarki yace : (shin kyautatawa na da wani sakamako face kyautatawa).
Wanda ya kiyaye dokokin Allah da hakkokinSa to Allah ma zai kiyaye shi a duniya da lahira, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: (ka kiyaye Allah sai Allah ya kiyaye ka) Tirmizi ne ya rawaito
Idan bawa ya nemi shiriya da gaskiya sai Allah ya shiryar da shi Allah Madaukakin sarki yace : (Wadanda suka bi shiriya sai Allah ya kara musu shiriya).
Cika alkawarin Allah na daga cikin imani da shi da kuma da abin da ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya zo da shi, sakayyarsa shine Allah na saka wa ma'abocinsa da aljanna. Allah Madaukakin sarki yace : (kuma ku cika alkawari na zan cika muku naku alkawarin)
Wanda ya gaskata Allah sai Allah ya karrama shi da abin da ya ke so da kuma kari Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: (muddin ka yi wa Allah gaskiya to zai gaskata ka.) Nasa'i ne ya rawaito. Ibnu kayyim  Allah ya masa rahama ya ce: (Bawa bai da wani abu da ya fi amfani kamar gaskiyarsa ga Ubangijinsa, duk wanda ya mu'amalanci Allah da gaskiya cikin dukkan al'amuransa sai Allah ya mishi abin da ya fi abin da ya ke yi wa waninsa na kyautatawa).
Iya gwargwadon kusantar bawa ga Ubangijinsa ta hanyar da'a da ibada iya kusancin Allah gare shi, Allah Madaukakin sarki ya ce a  hadisul kudusi : : (muddin bawa na ya kusance ni da taki to zan kusance shi da zira'i, idan ya kusance ni da zira'i zan kusance shi da ba'i) Buhari ne ya rawaito.
Bawa na da abinda ya zata daga ubangijin sa in alkairi ne to zai samu alheri in kuma ya munana zato to zai samu kwatankwacin haka manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ina inda bawa na ya zace ni) bukari ne ya rawaito
Kuma tauhidi shi ne tushen alheri da sa'ada duk wanda ya hadu da Allah da shi to zai rabauta da aljanna Aa farkon lamari ko karshen sa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Allah madaukakiun sarki ya ce (ya dan adam da za ka zo mini da cikin kasa na kusakwarai sannan ka hadu da ni ba ka hadani da wani to da zan zo maka da cikin kasa na gafara  )tirmizi ne ya rawaito
Duk wanda ya kyautata a wan nan duniya da imani da tauhidi to a lahira yana da aljanna da ganin ubangiji mai daukaka Allah Madaukakin sarki ya ce : (ga wadanda  su ka kyautata suna da kyakkyawa da klari ) sallah na da kofa a cikin aljanna da za a rika kiran masu yinta daga gare shi saboda sheki na gabban alwala  da tsarki za a gane wannan alumma ranar alkiyama da shi Mnzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce(lallai aluamma ta za a kira su ranar alkiyama suna masu hasken goshi da kafafuwa sakamakon gurbin alola ) bukari da muslim ne suka rawaito
(kayan ado da bawa  ya ke sawa yana isa ga mumini har inda alolan sa ya isa ) muslim ne ya rawaito
Mai kiran sallah ya na daga muryanshi da shelantawa na sallah sai sakayyarsa  ya zama daga jinsin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (mai kiran sallan shi ne mafi tsawon wuya a mutane ranar alkiyama )  muslim ne ya rawaito (ba wanda zai ji iya sautin mai kiran sallah aljani ne ko mutun  ko itaciya ko dutse face ya yi mishi  shaida ranar alkiyama  ) bukari ne ya rawaito Allah ya yi izini a daukaka masallatayya a ambaci ku sunan shi a cikin su  duk wanda ya gina wa Allah masallaci alhlin yana nemar  yardan Allah to Allah zai gina mishi kwatan kwacin shi  a alja) bukari da muslim na su ka rawaito
Kuma sadaka dalili ne na imani kuma rance ne abin ribanyawa a wurin Allah  duk wanda ya ciyar da wani abu to Allah zai maye  mishi  da abinda ya fii shi na alheri
Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Allah madakakin sarki ya ce : ya kai dan adam ka ciyar zan ciyar da kai ) bukari da muslim ne suka rawaito
(ba wata rana da bayi za su wayi gari a cikin shi face malayiku biyu sun sauka dayansu sai ya ce ya allah duk mai ciyarwa ka maye mishi daya kuma ya ce : ya allah duk mutumin da ke kame hanu to ka bashi lalatacce  ) Bukari da muslim ne su ka rawaito
  (ku ci ku sha ababan farin ciki sakamakon abin da ku ka gabatar a ranakun da su ka shude )
Mujahid Allah ya mishi rahama yace : (Ta sauka ne akan masu azumi). Za a kirayesu ne ta kofan rayyan kuma warin baskin mai azumi ya fi kamshin turaren almiski a wurin Allah
 Duk wanda ya mutu yana halin ihrami to za a tashi yana mai talbiya,
Ambaton Allah na raya zukata kuma yana sa karfin jiki, ma'abotansa basu da sakayya da ya fi Allah ya ambace su, Allah Madaukakin sarki ya ce : (ku ambace ni zan ambace ku)    Duk wanda ya ambaci Allah a wani hali to Allah zai ambace shi a hali mafi kyau Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin kudsi (Ni ina tare da shi idan ya ambace ni, idan ya ambace ni a zuciyarsa sai na ambace shi a zuciya ta, idan kuma ya ambace ni cikin jama'a ne to sai na ambace shi a jama'ar da suka fi alheri a kan su.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Majalisai na zikiri dausayi ne na aljanna, bawa na da abin da ya ke so a cikinta gun Ubangijinsa, wasu mutane uku suka fiskanto Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, dayansu sai ya ga wani wuri a majlisin sai ya zauna a wurin amma dayan sai ya zauna a bayansu, amma na ukun sai ya juya baya ya tafi sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :Ase ba zan baku labari game da mutanen nan uku ba? Shi na farkon su ya nemi mafaka a gurin Allah sai Allah ya ba shi, shi dayan kuma sai ya ya ji kunya sai Allah ma ya ji kunyarsa, amma dayan sai ya juya baya sai Allah ma ya juya masa baya. Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Addini daukaka ne ga ma'abotansa, to duk wanda ya taimaki addinin Allah to shi wanda zaa taimaka wa ne  Allah Madaukakin sarki ya ce :(Lalle Allah zai taimakawa wanda ya taimaki addininSa)
Wanda ya nusar ga alheri to yana da lada kwatankwacin ladan wanda ya yi aikin, kuma wanda ya sunnanta wata sunna kyakkyawa to yana da ladanta da ladan wanda ya yi aiki da ita har zuwa ranar alkiyama.
Kuma jarabawa sunnar Allah ce a halittunSa, kuma girma sakayya na ga girman jarabawar, duk wanda ya rungumi kaddara ya yarda to yana da yardar Allah, wanda ya yi fushi kuma zai hadu da fushin Allah.
Hakuri wajibi ne a umarni da hani da kuanyar shiga Aljannama kaddara, duk wanda ya jure ya yi hakuri to Allah zai bashi juriya da hakuri, duk wanda ya nemi sanin Allah a halin sauki to  Allah zai kawo mishi dauki yayin tsanani.
Gyaruwan al'uma na ga ilimi, :(wanda ya bi wata hanya yana mai neman ilimi to Allah zi saukake mishi da shi hanyar zuwa aljanna.)Muslim ne ya rawaito shi.
Dukkan dan Adam mai kuskure ne kuma mafi alherin masu kuskure sune masu tuba).

   
Wanda Allah ya datar da shi zuwa ga tuba sai ya fiskanci Allah yana mai tuba to Allah zai karbi tubansa kuma ya bashi lada  Allah Madaukakin sarki ya ce : (wanda ya tuba bayan zalunci da ya yi ya kuma gyara to Allah zai karbi tubarsa.
 Mumini idan mutuwa ta zo mishi sai a mishi albishir da yardar Allah da karamarSa, to sai ya zama ba wani abu da ya fi soyuwa a gare shi sama da abin da ke gaba gare shi sai ya kaunaci gamuwa da Allah sai Allah ma ya so haduwa da shi,  duk wanda ya muamalanci halittu da alheri sai Allah ya muamalance shi da kwatankwacinsa a duniya da lahira. Kuma mafi karamcin halittu shine Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, duk wanda ya mishi salati guda to Allah zai mishi guda goma, Ansarawa (sahaban Annabi na madina) ba mai son su sai mumuni, wanda ya so su Allah zai so shi.
Kuma Allah na tausayawa masu tausayi ne cikin bayinSa, duk wanda ba ya tausayawa mutane to Allah ma ba zai tausaya mishi ba, Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (wanda bai tausayi to ba zaa tausaya mishi ba) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Wata mace mazinaciya ta tausaya wa kare sai Allah ya mata rahama ya gafarta mata.
Wadanda suka fi dacewa da kyautatawa sune 'yan uwa makusanta, wanda ya sada zumuncinsa sai Allah ma ya sada masa.
Akwai aminci cikin sallama wa mutane, Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ku yada sallama za ku samu aminci) Ibnu Hibban ne ya rawaito.
Wadanda ya kankan da kai sabo da Allah to zai daukaka shi, Allah bai karawa bawa wani abu sabo da yafiya face buwaya, Allah Madaukakin sarki ya ce : (su yi rangwami su yi afuwa shin ba ku son Allah ya muku gafara ne).

Ibnu kasir Allah ya mishi rahama yace : (To lalle sakayya na daga jinsin irin wannan aiki to kamar yadda zaka yafe wa wanda ya ma laifi kai ma za a yafe maka haka nan kamar yadda ka yi rangwami kai ma za a ma rangwami ).
Duk wanda ya kaunaci wani bawa don Allah to Allah zai kaunace shi, haka duk wanda ya yi wa dan'uwansa adu'a a bayan idonsa to sai mala'ikan da aka wakilta da shi ya ce :amin kai ma Allah ya baka kwatankwacinsa.
Kuma buda wa wani a majlisai  sakayyarsa na daga jinsinsa,     Allah Madaukakin sarki ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani da Allah idan an ce da ku ku buda a majlisai to ku buda Allah zai buda muku).
Duk wanda ya yafe wa musulmi to Allah ma zai yafe masa kurakuransa ranar alkiyama.
Allah na kasance wa tare da mutum kamar yadda mutum ke tsayawa dan'uwansa musulmi,
Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya tsaya wurin biya wa dan uwansa bukata to Allah ma zai kasance cikin biya masa bukata, duk wanda ya yaye wa musulmi wani bakinciki to Allah ma zai yaye masa bakinciki daga bakincikin ranar alkiyama, duk wanda ya rufa asirin wani musulmi to Allah ma zai rufa asirinsa ranar alkiyama)Buhari da muslim ne suka rawaito.
(duk wanda ya yassara wa mara galihu to shi ma Allah zai yassara mishi duniya da lahira. Allah na taimakon bawa muddin bawa na taimakon dan'uwansa) Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya yafe wa halittu  shi ma Allah zai yafe masa, duk wanda ya 'yanta bawa, Allah zai 'yanta shi daga wuta gaba a madadin gaba. Duk wanda ya ci bashin dukiyar mutane yana nufin ya biya to Allah zai biya mishi, duk wanda ya wadatu da Allah da kuma abin da ya bashi to, to Allah zai wadata shi kuma ya isan mishi, Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya nemi wadatar Allah to Allah zai wadata shi) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Idan mutum ya kame kai daga haram da rokon mutane to Allah zai sanya shi ya zama mai kame wa, Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Lalle ne duk wanda ya nemi ya zama mai kamun kai to Allah zai maida shi mai kamewa.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Ba wani bawa da zai tausayawa wani bawa face shi ma Allah ya tausaya masa, Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Ya Allah duk wanda ya jibinci wani abu na jagoranci a cikin al'umata ya kuma tausaya musu to ya Allah ka tausaya masa.) Muslim ne ya rawaito.
 Alheri na zuwa da alheri ne, ta daya hanun kuma shi ma sharri na zuwa da sharri ne, to sakayyar mummuna ita ce mummuna kwatankwaciyarta. (Kuma ba a saka muku face da abin da ku ka kasance kuna aikatawa.)
Wanda zuciyarsa ta makance daga ganin gaskiya sai Allah ya makantar da ganinsa a Matattara, (Kuma wanda ya kasance a nan makaho to a lahira yana makaho kuma mafi bace wa bisa tafarki).
Duk wanda ya kaucewa gaskiya bayan ya santa to Allah zai karkatar da zuciyarsa daga shiriya ya jefa mishi shakku da tabewa.  (Kuma a yayin da suka karkace sai Allah ya karkatar da zukatansu).
Bijirewa alheri da addini karshensa tube rigar imani ne,  
Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma hakika idan aka saukar da wata sura sai sashinsu ya yi dubi zuwa ga sashi(su ce), shin wani mutum yana ganinku? Sa'anan kuma sai su juya. Allah ya juyar da zukatansu, domin hakika su mutane ne da ba su fahimta.)
Duk wanda ya bar da'a  ya shakala yinta da gangan to Allah zai tabar da shi ya mantar da shi kansa ya bar shi cikin azaba, Allah Madaukakin sarki ya ce : (sun mance  Allah sai ya manta da su)
Lalacewar badini akibar ta kara lalacewar, Allah Madaukakin sarki ya ce : (A cikin zukatansu akwai wata cuta sai Allah ya kara musu wata cuta.)
Duk wanda ya yi shamaki wa basirarsa daga addini to Allah zai masa shamaki daga ganinsa ranar sakayya, Allah Madaukakin sarki ya ce : (A a ha lalle ne su a wannan ranar abin shamakacewa ne daga Ubangijinsu).
Shirka shine mafi girman zunubi  to duk wanda ya ta'allaka zuciyarsa da wani abu ba Allah ba sai a kyale shi da shi, duk wanda ya nufi riya ko sum'a  neman a ji da aikinsa  sai a saka mishi da irin aikin shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce : (Duk wanda ya yi sum'a(neman aji) to sai Allah ya sa a ji shi wanda ya  yi riya sai Allah ya mai da shi mai riya) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Mai bauta wa wanin Allah tababbe ne a duniya da lahira,
 Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma suka riki gumaka baicin Allah domin su kasance mataimaka a gare su. A aha za su kafirta da ibadar su kuma su kasance makiyansu.)
Wanda ya yi wani aiki ya hada Allah da wani a cikinsa sai Allah ya bar shi da shirkansa, wanda ya kasance yana bautawa wani abu baicin Allah to zai bi shi cikin wutar jahannama, duk wanda ya rantse da wani addini bisa karya koma bayan musulunci to ya koma kamar yadda ya ambata, duk wanda ya suranta sura zaa azabtar da shi da ita ranar alkiyama, kuma a kallafa masa da ya busa masa rai, kuma ba zai iya busawa ba, duk wanda ya nemi yardan mutane wajen fusata Allah, to Allah zai yi fushi da shi kuma ya sanya mutane ma su yi fushi da shi, duk wanda ya tsani haduwa da Allah da Allah to Allah ma ya tsani haduwa da shi, duk wanda ya nufi ya yi kaidi da yaudara da makirci da hila ga addini to Allah zai mishi daurin talala kuma in ya tashi ya mishi kamun ba zata, Allah Madaukakin sarki ya ce : (su ka yi makirci kuma Allah ya shirya musu sakamakon makircinsu Allah shi ne ya fi makirai sakamakon makirci ) kuma ya ce : (suna  yaudaran Allah shi kuma ya na maida musu   yaudaran su )
Wanda ya jinkirta salla Allah zai jinkirta shi  Manzon Allsah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (wasu mutane ba za su gushe ba suna yin jinkiri har sai Allah ya jinkirta su ) muslim ne ya rawaito  duk wanda ya ki yin sujjada a duniya sai a hana shi yinta ranar alkiyama  Allah Madaukakin sarki ya ce (ranar da ake  yayewa ga makengema kuma a kira su zuwa ga sujjada ba za su samu daama ba )(gannansu ta na wulakance saboda wulakanci tana lullube su ana kiransu a duniya zuwa sujjada alhalin sauna masu lafiya ) girman kai shi ne dagun kai a kan gaskiya ga halittu sai a tada ma'botan shi kamar kwayan zarra mutane na taka su duk wanda ya yi karya guda daya da ta yadu to lallai Allah ranar alkiyama zai juya muka mukinsa zuwa keyasa mazinata wani harshen wuta zai rika zuwa musu tun diga kasansu Allah ya na debe albarkan riba  maciyinshi kuma za a rika wurwurishi da duwatsu a cikin bakin shi  ranar alkiyama duk wanda ya boye ilimi Allah zai sanya mishi linzami irin linzami na wuta ranar alkiyama duk wanda ya ci gululi zai zo da abinda ya ci na gululi ranar alkiyama duk wanda ya hana saurar ruwa Allah zai ce da shi ranar alkiyama a yau zan hana ka falalata kamar yanda ka hana abinda ba hanunka ne ya aikatashi ba duk wanda ya sha giya a duniya san nan bai tuba ba to an haramta mishi ita ranar alkiyama wanda ya sanya alhariri daga cikin maza a duniya to ba zai sanya ta ba a lahira wanda kuma ya yi da'awa irin da'wa na karya domin ya kara dukiya ba abinda zai kara mishi a wurin Allah sai talauci butulcewa ni'ma yana shelanta gushewanta Allah ba ya canja wani abu na ni'ma tare da mutane da jin dadi na rayuwa har sai sun canja daga kawunan su da zalunci da sabo izgilanci da addini da ma'botan addini sakayyansa na daga jinsinsa wanda ya yi izgilanci ga bayin Allah Allah ma zai mar izgili alaman munafiki shi ne kin mutanen madina na daga nasarawa wanda kuma ya ki su Allah zai ki shi duk wanda ya kashe rayi tare da wani abu to za a rika azabtar da shi da wannan abun har ranar alkiyama , mai sata na miji ya shinpida hanunshi ne akan barna saboda haka ta cancanci a yanketa ,duk wanda ya yi kazafi wa kuyangansa ko kuma bawansa alhali kuma shi ya barranta daga wannan to za amishi bulala ranar alkiyama za a kafawa   mahayinci tuta wanda za a sanshi da shi a ranar alkiyama duk wanda ya la'anci wani abu wanda wannan abun bai cancanci hakan ba to la'nan zata dawo kanshi Allah ya tsine wa wanda ya tsine wa iyayenshi zalunci duhhai ne ranar alkiyama duk wanda ya yi zalunci gorgodon kaidi na taki Allah zai nadeshi daga kassai guda bakwai
Yanke zumunci na makusanta yafi muni akan waninsa Allah yana cewa ga mahaifa (ba ki yarda na sadar da wanda ya sadaki ba na yanke wanda ya yankeki ba ) bukari da muslim ne suka rawaito Allah ya yi alkawarin narkon azaba ga wadanda suke azabtar da mutane ba tare da hakki ba Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (lallai Allah yana azabtar da wadanda suke azabtar da mutane a duniya ) muslim ne ya rawaito riskar da cutarwa da wahalarwa ga halittu karshensa baya haifar da da mai ido Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (duk wanda ya cutar to Allah ma ya cutar da shi duk wanda ya wahalar to shi ma Allah ya wahalar da shi) tirmizi ne ya rawaito , duk wanda aka bawa wani abu na jagoranci na musulmai sai ya kuntata musu ko kuma ya shamaki tsakaninshi da su gameda bukatunsu to Allah ma sai ya yi shamaki tsakaninshi da shi duk wanda ya bibiyi al'auran mutane to Allah ma zai bibiyi al'aurarsa har sai ya kunyatashi a gidansa mai cin nama yana kekketa mutuncin mutane da harshensa zai zo ranar alkiyama yanada farata daga karafunan nuhas bagwanja yana pippige fiskansa da su wanda ya ji zancen wasu mutane wanda suke suna kin hakan za a kwararamishi a kunnenshi harsashi na narkakken dalma ranar alkiyama garin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi amintacce ne duk wanda ya bada tsoro ga mutanenta Allah ma zai tsorata shi wanda ya kasance yanada mata biyu ya karkata zuwa ga dayansu zai zo ranar alkiyama tsaginshi a karkace idan bawa ya bude kofan roko to Allah zai bude mishi kofan talauci rowa da kamkame hanu yana goge albarka kuma yana wajabta tsananin hisabi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (kada ka kididdige Allah ma sai ya kididdige maka) bukari da muslim ne suka rawaito
Bayan haka ya ku musulmai :
Allah mai dubi ne ga bayinsa kuma yana dakonsu a madakata kuma zai sakanya wa kowa abunda ya aikata sakayya na daga jinsin aikin wanda ya yi daidai da shi a alheri ne ko na sharri kamar yanda ka ke hisabi kaima za amaka hisabi duk wanda ya nufi ya san makomansa a wurin Ubangijinsa to ya duba abinda ya ke da shi a wurin Allah domin Allah yana saukar da bawa ne inda bawa ya saukar da kansa
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jifa
Duk wanda ya yi aiki na kwarai to don kansa wanda kuma ya munana to don kansa Ubangijinka bai zama mai zalunci ba ga bayi Allah sa mini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma

                     Huduba ta biyu
dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawansa dukkan godiya bisa ga datarwansa da kuma baiwansa , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya ina mai girmama sha'ninsa na shaida cewa annabin mu Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalanshi da aminci tabbatacce mai kari

ya ku musulmai
duniya gida ne na aiki lahira kuma gida ne na sakayya Allah ya kan gaggauto wa bawansa da wani sakayya a nan duniya shi ni'man da ke hade da godiya ga ma'bota da'a albishir ne  , su kuma musibu tare da hakuri daukaka ne ko kankaran zunubai , amma mai sabo wanda ya juya baya to idan an jarrabeshi to wannan ukuba ce da gaggawa abinda ya ke gurin Allah shi ya fi tsanani idan kuma an jinkirta ukubarsa to jinkirin da Allah ya misahi kamar  daurin talala ne
sannan ku sani Allah yana umurtan ku da salati da aminci ga annabin sa.              

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق