HUDUBAR FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah,
wanda ya halicci sammai da kasa, ya sanya duhu da haske ina kyautata yabo a gare shi ina gode mishi da yammaci da safiya da lokacin sammako, na shaida ba abin bautawa
da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba
shi da abokin tarayya, wanda yace : ( kuma rayayyu
ba zasu yi daidai da matattu ba Allah na jiyar da wanda ya so, amma kai ba za
ka jiyar da wanda yake cikin kabari ba)
Na
shaida shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma manzonSa ne, ya yi gargadi a kan
gafala da gajiyawa, tsira da amincin Allah su tabbata gare shi,da iyalan shi da
sahabbansa wadanda suka samu babban falala da lada Bayan haka.
Ina muku nasiha da ni kai na da jin tsoron
Allah Allah Madaukakin sarki ya ce:-(yA ku
wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face
kuna musulmai).
Bibiyar
imani da ba shi kulawa na daga cikin sifar musulmi kuma abin nanatawar masu
hankali, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Imani na tsufa ya kode a cikin dayanku kamar yadda
tufafi ke tsofewa ya kode, to ku roki Allah Madaukakin sarki : da ya sabunta
muku imani a cikin zukatanku).
Kamar yanda tufafi ke tsofewa, ai wato kamar yanda sabon
tufafi yake tsofewa sabo da
dadewa ana amfani da shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (An ambaci zuciya ne kawai da zuciya sabo da
jujjuyawa da yake yi , misalin
zuciya kamar misalin gashi ne da aka
rataye ta a wani itaciya iska na kada ta
cikinta da wajenta)
Mumini na sabunta imaninsa , sabo
da imani ba ya tabbatuwa a hali guda,
sai dai yana gajiyawa sabo da dadewa
ya raunana sakamakon gajiyawa a bangaren ibada , ko daina ibada ko kuma
gafala daga Allah, da dulmuyar rayi a cikin sha'awe-sha'awensa to mutum wani halitta ne da ke da iyaka a
ikonsa, yana da rauni a fidirarsa yana
tsakanin gajiyawa da gajartawa Allah Madaukakin
sarki ya ce:-(An halicci dan adam a halin yana mai
rauni).
Duk wani abu da zai sami musulmi na yanke ibada
daga wani lokaci zuwa wani lokaci ko kuma zamewar kafarsa , to hakika baya kubuta
daga hukunci na Ubangiji daga ciki akwai
komawa zuwa ga Ubangiji da fadakar
zuciya Allah Mai tsarki da daukaka yana
son masu yawan tuba yana farin ciki da tubarsu, Annabi tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce:-
(Na
rantse da wanda raina ke hanun shi da
badon kuna aikata zunubai ba da Allah ya
tafiyar da ku ya zo da wasu mutane masu yin zunubai , kuma suna neman gafara
sai ya gafarta musu.)
Imani
na karuwa yana raguwa , yana karuwa da biyayya kuma yana raguwa da sabawa Allah
, idan zuciyar dayanku ta farka daga gafalarta,
ya rika ayyuka na da'a ya riki sabuba na imani to imaninsa zai karu ya yi karfi ko yakininsa ya yi karfi idan ya yi dubi zuwa ga ni'imomin Allah a gare shi sai kaunar sa ga Allah ta karu sai ya yi
lafazi na ambaton Allah ya gaggauta cikin tuba da ayyuka na alheri domin ya riski abin da ya gajarta da abin
da ya tsere mishi a dalilin gafala
sabo da haka ne lalle abin kwadayi ne
kwarai wurin bibiyan imani da
kuma aiki bisa daga darajar shi na daga cikin sifa na salihai , Abu Darda Allah ya kara yarda a gare shi
yana cewa: "Na daga cikin fikihun bawa ya rinka bibiyan imaninsa da abin da ya tawaya
daga gare shi , na daga cikin fikihun bawa
yasan cewa yana
karuwa ne shi ko yana raguwa".
Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya kasance
yana cewa sahabban shi , '' ku zo mu kara imani '' sai su ambaci
Allah Mabuwayi .
Ibn Mas'ud Allah ya kara yarda a gare shi yana
cewa a cikin adu'arsa (Ya Allah ka kara mana
imani da yakini da fahimta).
Mu'az bin Jabal -Allah ya kara yarda
a gare shi - yana cewa wani mutum
(zauna tare da mu , mu kara imani na wani lokaci).
Duk yanda imanin mumini ya kai kololuwa a daraja to ba zai aminta wa
kansa ba, tafarkinsa shi ne komawa zuwa ga Allah yana neman tabbatuwa a kan
tafarki, Allah Madaukakin sarki yace a harshen bayinSa muminai: (ya Ubangijinmu kar ka karkatar da zukatanmu bayan ka shiryar
da mu).
Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana yawaita fadinsa.: ya mai juya
zukata da basira tabbatar da zuciya ta bisa addininka).
Idan mumini ya san shaidan na dakonsa ne, to ya yi kokari don yayi yaki da fizgarsa, ya tunkude waswasinsa, ya
toshe kofofin yaudarasa, kada ya mika wuya, kada ya samu karayar zuci, yana mai neman agaji daga Ubangijinsa, Allah
Madaukakin sarki ya ce: ((To idan ka zo karanta
kur'ani to ka nemi tsarin Allah daga shaidan abin jefe wa. Lalle shi bai da iko
a kan wadanda suka yi imani, kuma suna dogaro ne ga Ubangijinsa)
Mafi alherin guzuri ga wanda ya ke neman
guzuri, kuma mafi alherin abokin tafiya a hanyar tabbatuwa bisa tafarki shine
riko da littafin Allah da aiki da shi, wanda ya yi riko da shi Allah zai kare
shi, wanda ya bi shi kuma Allah zai kubutar da shi.
Musulmi fadakakke yana yin kokari don ya ga ya
fita daga yanayi na gafala, da sharri na rauni da gajiyawa, sabo da zai ji
farinciki ne idan ya yi biyayya ga Allah, yana mai neman yardar Ubangijinsa, wani mutum ya tambayi Manzon Allah menene imani? Sai Manzon
Allah ya ce :( idan kyawawan ayyukanka suka burge ka munanan ayyukanka suka
bata maka rai to kai mumini ne).
Ta yaya zai gafala daga Allah ya gajiya daga
ibada wanda zuciyarsa akwai haske na Alkur'ani! Yana dandana halawar imani kuma
ya san cewa yana da Ubangiji mai tausayi wanda ke yafe kusakuran masu tuba kuma
yana gafarta zunubai, Allah Madaukakin sarki ya ce :
(kuma wanda ya aikata mummuna ko ya zalunci kan shi sannan ya nemi gafarar
Allah to zai samu Allah Mai gafara ne Mai jinkai)
Ambaton Allah da tunani cikin ayoyinSa yana
farkar da zuciya kuma yana kara imani kuma yana tsarkake zuciya; Allah Madaukakin
sarki ya ce : (Abin sani kawai, muminai sune wadanda
suke idan an ambaci Allah zukatansu su firgita, kuma idan an karanta musu
ayoyinsa sai su kara musu imani, kuma ga Ubangijinsu suke dogara.)
Ya dace ga musulmi ya dawo da ransa in ya
gafala, da gabbansa idan sun yi rauni ko gajiya a ibada, domin tsoron fushin
Allah da ukubarSa, na daga cikin Adu'ar Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi, (Ya Allah ina neman tsarinka
daga gushewar ni'imarka da juyawar afiyarka da azaba bagtatan da dukkan abin da
zai fusata ka,)
Zuciya kan karkata zuwa ga duniya a wasu lokuta
tana ta neman abin duniya ido rufe wasu lokuta, sabo da haka ne Allah ya umarce
mu da yawaita ambato, don a samu daidaito, a gare mu tsakanin neman abin duniya da sauke
nauyin wajibi na addini, : (ya ku wadanda suka yi
imani ku ambaci Allah ambato mai yawa ku yi tasbihi safiya da maraice).
Kamar yadda
zurfafawa cikin abubuwan da aka halatta da barna da wuce gona da iri cikin
al'adu yana haifar da gajiya Allah Madaukakin sarki ya ce : (ya 'yan adam ku riki adonku a gun dukkan masallaci ku ci
ku sha kada ku yi barna, lalle shi bai son mabarnata.)
Ba ya boyu wa ga masu hankali cewa abota da
masu raunin himma da marasa manufa kan
haifar da gajiya wa da gafala.
Idan musulmi bai ankara ba daga gafala da ya ke
ciki ya gaza tunkude gaza wa da yake da shi da rauni to sai sifa ta tsauri da
kekashewar zuciya ta yi galaba a kan shi da rauni da nauyi wajen sauke nauyin
ibada, da'a ta yi mishi wahala zuciya ta
yi tsatsa ya dushe hasken imani
Allah Madaukakin sarki ya ce : (Bone ya tabbata ga wanda zukatarsu suka kekashe daga
ambaton Allah wadancan suna cikin wata bata bayyananna).
Idan musulmi bai magance zuciyarsa ba to zai dangana da halin nan da
Allah Mai tsarki ya bada labari game da
ita, a fadinsa (sa'annan kuma zukatanku suka kekashe
daga bayan wancan, sabo da haka suka zama kamar duwatsu, ko mafi tsanani ga kekashewa, kuma lalle ne daga duwatsu
hakika akwai abin da maremari suke bubbuga daga gare shi, kuma lalle ne daga
gare su hakika akwai abin da ya ke tsatsagewa har ruwa ya fita daga gare su,
hakika, akwai abin da ya ke fadowa domin tsoron Allah, kuma Allah bai zama
gafili ba daga abin da ku ke aikatawa.)
Allah ya sa mana albaka ni da ku cikin
Alkur'ani Mai girma kuma ya amfanar da ni da ku da abin da ke ciki na ayoyi da ambato
mai hikima. Iya abin da ya sawwaka kenan cikin abin da zan fada tare da neman
gafarar Allah, kuma ku nemi gafararSa domin shi Mai gafara ne Mai jinkai.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda
ya amsa kiran wanda ya roke shi, musulmi na gode masa a sirrinsa da ganawarsa, na
shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin
tarayya ba wani Ubangiji koma bayanSa, na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne
kuma ManzonSa ne kuma zababbenSa ne,
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa wadanda
suka rabauta da kaunarSa kuma da yardarSa.
Bayan haka :To ina muku wasiyya da ni kai na da
jin tsoron Allah.
Duk wani
abu da ya samu musulmi na gafala kuma alama na gazawa ta afka mishi kafa ta
zame, to lalle kofar tuba a bude take, hanyoyin alheri birjik su ke, Allah na
son masu yawan tuba da komawa gare shi, kuma yana cewa a hadisul kudsi : (ya ku bayi na lalle ku masu yin kuskure ne cikin dare da
wuni, ni kuma mai gafarta zunubai ne baki daya, ku nemi gafara ta zan gafarta
muku).
Ku yi salati ga Annabin shiriya. Hakika Allah
ya umarce ku da hakan a littafinSa sai ya ce :(Lalle
Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku wadanda suka yi imani ku yi
salati a gare shi da aminci tabbatacce.)
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق