الأحد، 15 ديسمبر 2019

SURAR DA KE BAYANIN DALILAN TSIRA DAGA HASARA


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Ahmad Bin Dalib 16-4-1441Ah/13-12-2019
Hudubar farko
Allah yana fadi a cikin littafinSa mai girma, kuma shi ne mafi gaskiyar masu magana. (Ina rantsuwa da zamani. Lalle mutum na cikin hasara. Face wadanda suka yi imani kuma suka yi aiki na kwarai kuma suka yi wasiyya ga juna da gaskiya kuma suka yi wasiyya da hakuri.)
Allah ya yi rantsuwa da Asr wato zamani ko kuma wani yanki na shi, wato lokacin yammaci, shi aka yi rantsuwa da shi kan cewa lalle jinsi na mutum na cikin hasara, to kowa duk wanda ya kasance haka to makomarsa gidan halaka tir da matabbata, sai Allah ya toge daga cikin hasararrun wadanda suka siffatu da sifofin nan guda hudu da ayoyi bayyanannu suka nuna:
Sifa ta farko ita ce  a fadinSa: "Face wadanda suka yi imani" Imani kuma asalin shi da kamalarsa bai samuwa sai da ilimi.
Sifa ta biyu ita ce  a fadinSa:" kuma suka yi aiki na kwarai" shi aiki na kwarai shi ne wanda aka yi shi don Allah kuma bisa koyarwar Manzon Allah.
 Sifa ta uku ita ce  a fadinSa Madaukakin ambato :" : "kuma suka yi wasiyya ga juna da gaskiya" Hakikaninta kira zuwa ga Allah.
Sifa ta hudu ita ce  a fadinSa Tabaraka wata'ala : " kuma suka yi wasiyya da hakuri." Wato suka Siffatu da wannan sifa mai kubutarwa daga hasara.
Duk wanda ya yarda da Allah a matsayin Ubangiji, kuma ya yarda musulunci shine addini, kuma ya yarda Muhammad  a matsayin Annabi kuma Manzo, ya san abin da Allah ya ke kauna, ya fahimci manufa na wahayin Allah, ya yi aiki na kwarai don Allah, ya tsarkake shi daga shirka, da bidia abin munantarwa, ya maida kansa kamili ta hanyar ilimi mai amfani da aiki na kwarai, sannan ya yi kokari wurin maida waninsa ma kamili ta hanyar kiransa zuwa ga gaskiyan da ya samu, ya yi wasiyya kuma ya nemi a mar nasiha da abin da zaa tambayi kowa a kabarinsa na sanin Allah da sanin Manzonsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da sanin addinin musulunci, sani da ke tare da dalilanta na  daga littafin Allah  da sunnan Manzonsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da kuma abin da aka karbo daga sahabbai da limamai na addini  masu shiryarwa. Kuma ya yi hakuri bisa imani da aiki na kwarai, da kuma kira zuwa ga Allah Mabuwayi da daukaka yana yin shi a aikace da neman sani da ilmantarwa, da kuma hakuri bisa abin da ke faruwa na cutarwa ga duk wanda ya  riki tafarkin Annabawa, to hakika wallahi ya tsira da hasara na rantse da Ubangijin zamani.
Sabo da cika na wannan sura mai girma tare da gajarcinta wajen bayanin abin da zaa umarci mutane don su tsira su rabauta Abu Abdullahi Imam Al shafi'i Allah ya jikan shi ya ke cewa: "Wannan sura da Allah bai saukar da wata hujja ba ga bayinSa sai ita to ta ishe su."
Ai da ta ishe su wajen tsaida musu hujja sabo da wajabcin riko da umarnin Allah na sharia, ta hanyar gaskata wahayi na Allah, da bin umarninSa da nesatan haninSa,da kudurta abin da Allah Mai tsarki  ya halatta.
Allah sa min Albarka ni da ku.

Huduba ta biyu
Allah Madaukakin sarki yana cewa  (ka sani cewa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma ka nemi gafarar zunubinka da na muminai maza da muminai mata Allah ya sa majuyarku da mazauninku).
 Sufyan Bin Uyaina  Allah ya masa rahama ya ce : "sai ya fara da ilimi kafi fadi da aiki,"  dukkan shiriya na cikin sanin ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, Addinin gaskiya gabadayansa ya kunshi neman gafara ne gurin Allah da tuba zuwa gare shi furuci da aiki,
Allah Mabuwayi da Dauka yana cewa  (Suna so su bice hasken Allah da bakunansu alhali kuwa Allah Mai kammala haskenSa ne ko da kafurai sun ki.shi ne wanda ya turo ManzonSa da shiriya da Addinin gaskiya don ya daukaka shi akan dukkan addinai ko da mushrikai sun ki)

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق