Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah masanin gaibi Mai suturce
aibi mai yaye bakinciki Mai yafe zunubai Mai tsinkayan dukkan sirri da ke
zukata, muna gode masa kuma muna neman taimakonSa muna neman gafararSa muna
kuma tuba zuwa gare shi.
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu,
muna riko da shi (Allah) a dukkan al'amuranmu da yanayinmu.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake ba shi da
abokin tarayya.
Kuma na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, ya isar da
sako kuma ya sauke amana.ya yi nasiha ga al'uma ya yi jahadi don Allah
cancancin jahadi har mutuwa ta zo masa. Tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi da iyalanSa da sahabbanSa baki daya.
Bayan haka,
Mafi alherin zance shine maganar Allah, mafi alherin shiriya shi ne
koyarwar Annabi Muhammad, mafi sharrin al'amura shine fararrunsu, kuma dukkan
bid'ah bata ce, kuma dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah ku ji tsoron Allah cikin umarninsa ku hanu daga abin
da ya yi hani a kai ya kuma tsawatar. (ya ku
wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face
kuna musulmi)
Ya ku bayin Allah!
Lallai ga karewan kwanaki akwai abin lura, ga abin da ya shude kuma a
kwai tunatarwa da izina (Allah na juya dare da
wuni, lalle ga hakan akwai abin lura ga
ma'abota basira).
Ranaku da watanni da lokutan shekara, da shekaru na shudewa suna bin
junan su, burace – burace da ajali na karewa, wasu al'uman na riskan wasu, (Duk wanda ke
kanta zai kare sai fiskar Ubangijinka ma'aboci daukaka da karamci zai wanzu).
Ya
ku jama'ar Musulmai!
Hakika lokacin hunturu ya
fiskanto ku, sanyinsa mai gargadi ne, Allah ya yiwa jahannama izini da ta
numfasa a cikinsa, An karbo daga Abu Huraira
Allah ya kara yarda a gare shi yace :Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce : ( wuta ta koka zuwa ga Ubangijinta sai ta ce :" sashi na
ya ci sashi, sai Allah ya sanya mata numfasawa biyu :numfasawa daya a lokacin
hunturu,dayan kuma a lokacin bazara, shi numfasawarta na lokacin hunturu to
shine jaura, na lokacin bazara kuma shine wannan iska mai tururi)Bukhari da
Muslim ne suka rawaito.
An rawaito daga Umar dan khaddabi cewa
idan hunturu ya zo sai ya bibiyi talakawansa sai ya rubuta zuwa gare su : "Lalle
hunturu ya zo kuma shi makiyi ne to ku masa shiri na daga fatu da hoffofi da
safanni, ku riki fatu a matsayin riga 'yar ciki da ta waje, domin sanyi makiyi
ne mai saurin shiga (jiki) mai dadewa bai fita ba".
To ku bibiyi bayin Allah -masu
rauni- ku taimaka musu bisa sanyin hunturu, ku bibiye su don basu abinci da
tufafi da mayafi, ku nemi ladan su gurin Allah a ranar gamuwa, (Duk abin da ku ke ciyarwa na alheri to don kan ku ne, ba
wani abu da za ku ciyar face don neman yardar Allah, ba wani abu da zaku ciyar na alheri
face an cika muku shi, a halin ku ba zaa zalunce ku ba.)
Ya ku bayin Allah!
Ku yi lura da wadannan zamuna da lokutan
shekara da abin da ke cikinsu na maslahohi da hikimomi, da ace zamanin gaba
daya lokaci guda ne cikin lokutan shekara da wasu maslahohin an rasa su wato na
sauran fasalin, kamar da dukkan shekara bazara ce to da an rasa amfani da
maslahohin hunturu, haka ma in da kaka ne gaba dayansa ko damina dukaninsa.
Abin mamaki ta yaya zaa sabawa Ubangiji***
Ko ta yaya wani mai korewa
zai kore shi*
Cikin komai akwai alama tasa***
Da ke nuni cewa shi kadai
ne*
Ya ku jama'ar Musulmai!
Hunturu ya fiskanto, to maraba da ganimar masu
bautan Allah, da kuma kaka ta muminai, dare na tsawaita cikin shi sai su samu
rabon su na barci, sannan hakarkarinsu na yin nesa daga makwanci, don su yi
tsayuwan dare, wuninsa mai sanyi na gajarta don ya saukake musu wahalar azumi.
Allah Madaukakin sarki ya ce : (lallai masu tsoron Allah suna cikin lambuna da maremari.
Suna masu dibar abin da Ubangijinsu ya ba su, lallai su sun kasance masu
kyautatawa a gabanin haka(a duniya). Sun kasance a lokaci kadan na dare suke
yin barci. Kuma a lokutan asuba suna ta yin istigfari.)
Lokacin Hunturu -Ya ku bayin Allah! - Lokaci ne na kaka ga muminai, suna
kiwo cikin gonakan da'a ga Allah. Suna shakatawa a fagage na ibadoji zukatansu
na walwawa cikin dausayin kusantar Ubangiji, an samu saukin wahala da gajiya,
azumin bai gajiyar da su, ko dare ya kuntata gare su ga barcinsu ko tsayuwansu
na dare.
An rawaito daga Amir dan Mas'ud Allah ya
kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce :"Azumi cikin hunturu wata ganima ce na ruwan sanyi)Ahmad
da Tirmizi ne suka rawaito.
Abdullahi dan salam ya
ce :A yayin da Annabi ya zo garin Madina mutane sun yi cacarindo zuwa gare shi,
Sai na shigo cikin mutane don na gan shi, a yayin da na samu ganin fiskar shi
sai na tabbatar wannan fiskar ba na makaryaci ba ne,farkon maganar da ya fara
da ita ya ce : (ya ku mutane ku yada sallama ku ciyar da abinci, ku sada
zumunci, ku yi salla a halin mutane suna barci za ku shiga Aljannar Ubangijinku
da aminci).Ahmad da Tirmizi ne suka rawaito,kuma ya inganta shi.
Yayin da
mutuwa ta zo wa Mu'az Bin Jabal sai ya ce ga kuyangarsa : "kaiton ki shin
gari ya waye? Sai tace : a'a, sai ya kyale ta zuwa bayan wani dan lokaci sai ya
ce: ki duba, da ta duba sai tace ; "e" sai ya ce : Ina neman tsarin Allah daga safiyar
da za ta kai zuwa ga wuta, sannan sai yace : Maraba da mutuwa, maraba da bakon
da yazo ana halin talauci, duk wanda ya yi nadama ba zai rabauta ba, Allah ka
san ba wai ina bukatar zama a duniya ba ne sabo da tona sabbin rami na koramai
ba, ko dashen itatuwa ba, sai dai ina son zama ne don na dage da kokari a daren
hunturu mai tsawo, da kuma fiskantar kishin garji a lokacin tsananin zafi, da
kuma gogayya da malamai a sahun halkan ambaton Allah."
Ya ku bayin Allah!
A lokacin hunturu ne dare ke tsawaita wuni ke
gajarta, Hakika Allah ya sanya dare sutura, ya sanya barci kuma hutu, wuni kuma
don neman abin rayuwa.
(Allah ne
wanda ya sanya muku dare domin ku natsu a cikinsa, da rana mai ganarwa, lalle
Allah hakika Ma'abocin falala ne a kan mutane, kuma amma mafi yawan mutane ba
su godewa.)
Hakika
dimantan kwana ba barci wata cuta ce mai tafiyar da nashadi, mai kashe jiki, mai hana neman arziki da aiki, kuma yana
banzatar da lokuta, kuma yana shagaltarwa daga da'a, kuma ya sabawa sunna.
Allah
Madaukakin sarki ya ce :(kuma na daga cikin ayoyinSa barcinku a cikin dare da
wuni, da neman ku ga falalarSa, lalle a cikin wannan akwai ayoyi ga mutane masu
saurarawa.)
Annabi ya kasance yana kin barci
kafinta da zance bayanta –wato sallar lisha-
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan
abin jefewa. (kuma shi ne wanda ya sanya muku
dare ya zama tufa, da barci ya zama hutawa, da yini ya zama lokacin tashi).
Allah ya sa min albarka ni da ku a cikin
Alkur'ani.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah bisa datarwarSa da kyautatawarSa, tsira da amincin Allah su
tabbata ga Muhammad Mai kira zuwa ga yardarSa, tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi da iyalanSa da sahabbansa, da 'yan uwansa.
Ya jama'ar Musulmai!
Lalle ba abin da musulunci ya bari a halin
rayuwa , ya yi la'akari da sanjawar zamani da lokuta sai ya shar'anta hukunce
–hukunce na azima da sauki a yayin larura.
Na daga cikin abin da Allah ya ke daga
darajoji da shi, ya kuma kankare kusakurai da laifuka akwai gaggautawa zuwa ga
tsarki, wanda sharadi ne na ibadoji, kuma rabi ne na imani, kuma sharadi ne na
salla wanda yake rukuni ne na musulunci. To dagewa da jurewa da hakuri ga abin da aka ki, da
bauta ta hanyan amfani da ruwa a lokacin sanyi a hunturu, na cikin masu kankare
zunubai, An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara
yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce :"Ase ba zan nusar da ku ga abin da Allah ke goge zunubai da shi
ba, kuma ya daga darajoji da shi? Su ka ce : E ya Manzon Allah,sai yace :
Yalwata alwala a halin ba a so, da yawan taku zuwa ga masallatayya, da jiran
salla bayan idar da salla: Wancannin ku shi ne Ribadi )Muslim
ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah
Na daga cikin sauki irin na shari'a da hikima
na musulunci da rangwami da saukakawa mutane a yayin wahala mai bijirowa, da
cutuwa da ake tsammani (kuma bai sanya muku wani abu na kunci ba a addini)
Duk wani abu mai wahala na janyo saukakawa, (kuma
Allah bai dora wa rai sai abin da ya ba shi, Allah zai sanya sauki bayan
tsanani.
Musulunci ya shar'anta sauki yayin kunci da whala da larura, na daga ciki akwai mara lafiya,
Kai har ma mai laifiyan idan ya tsoracewa kansa, amfani da ruwa to an
shar'anta masa taimama da kasa, kamar yadda a ka shar'anta wa wanda ya ji ciwo
da ya yi shafa kan abin da ya rufe ciwon ko ma a kan maganin.
An karbo daga
Jabir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Mun fita a wata tafiya sai dutse ya samu wani mutum ya mishi rotse a
kai, sai ya yi mafarki sai ya tambayi mutanensa sai yace : ko ina da sauki ko
zan iya na yi taimama? Sai suka ce ba ka da wani sauki tunda za ka iya amfani
da ruwa, sai ya yi wanka sai ya mutu. Yayin da suka zo gun Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare sai aka bashi labarin hakan sai ya ce: sun kashe shi Allah ya kashe su, me ya sa ba
za su tambaya ba idan basu sani ba, ba komai ba ne maganin jahilci sai tambaya.
Ai daya yi taimama kawai da ya isan masa ya matse ko ya daure ciwon nasa da
tsumma, sai ya shafa kan ciwo ya kuma wanke sauran jikin nasa )
An karbo daga
Amru dan As Allah ya kara yarda a gare
shi ya ce : Na yi mafarki a dare mai dari a yakin zatus salasil, sai na
tausayawa kai na na yi taimama don in nayi wanka zan halaka.sai na yi
(jagorancin ) salla ga mutane na sallar asuba, sai su ka ambaci hakan ga Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai yace : ya Amru ka yi limanci
wa mutanenka a halin kana janaba? Sai na gaya mishi abin da ya hana ni wanka
nace ni na ji fadin Allah da ya ke cewa : (kuma
kada ku jefa kan ku ga halaka lalle Allah ya kasance mai tausayi ne a gare ku),sai Manzon Allah ya yi dariya bai ce komai ba. Abu Dauda
ya rawaito Albani kuma ya inganta shi.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق