الجمعة، 20 ديسمبر 2019

FIDIRA


Hudubar Masallacin Annabi na Shaikh Aliyu bin Abdurrahman Alhuzaifi 23-4-1441 Ah 20-12-2019Ac
Da sunan Allah Mai rahama Mai jinkai.

Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mabuwayi Masani, wanda ya halicci mutum cikin mafi kyan tsari, wanda ya tausayawa mukallafai da saukar musu wannan littafi mai daraja, wanda ya yi baiwa ga halittu da ni'imomin da basu gidayuwa na daga falalarsa mai girma, ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi bisa ni'imominsa da baiwarsa da alherunsa da muka sani da wadanda bamu sani ba, ba abin bauta wa da gaskiya sai shi, Ma'abocin kyautatawan da bai katsewa   da  kyautayinsa dadadde, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, Mai rahama Mai jinkai, na kuma shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawansa ne kuma ManzonSa ne, mai shiryarwa zuwa ga tafarki mikakke, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga bawanka kuma Manzonka Muhammad da iyalansa da sahabbansa wadanda suka rabauta da daukaka na duniya, a lahira kuma suka rabauta da ni'ima na har abada.
Bayan haka, ku ji tsoron Allah wanda ya halicce ku ya baku duk abin da kuke kauna ya tunkude muku abin da kuka tsana, ya ku mutane! Ina tunatar da ku da ni kai na da ni'ima da ta fi kowacce, dukkaninta Allah ya ni'imta mutum da su, muddin ya kiyaye ta ya bata matsayinta cancancin matsayinta, ya kiyaye ta ya mutu a kanta to hakika ya samu sa'ida a rayuwarsa da bayan mutuwarsa sa'idar da bai zai taba tsiyacewa ba da ita har abada ya kuma rabauta da  alhairu, kuma ya tsira daga sharri da abubuwa masu halakarwa, Allah zai gyara dukkan lamuransa baki daya a rayuwarsa, kuma ya jikansa bayan mutuwarsa, kuma wannan shine babban rabo, idan mutum ya sauya wannan ni'ima mai girma ta hanyar kafurcewa ko munafunci ko da wani aiki da ke kishiyantar wannan ni'imar ya sarayar da ita da rashin kiyaye ta to hakika ya yi hasara mabayyaniyar hasara, ko da an hada mishi abubuwan jin dadin duniya da kyalakyalanta, to ba wani abu bane ita sai inuwa mai gushewa, kuma jindadi ne mai kaucewa, kuma ni'ima ce mai karewa jindadinta na tafiya ta bar hasara. Allah Madaukakin sarki yace (Rayuwar duniya ba wata aba ba ce face jindadi mai rudi) Allah Madaukakin sarki yace (ya ku mutane lalle alkawarin Allah gaskiya ne kada rayuwar duniya ta rude ku, kada wani mai rudi ya rude ku daga Allah.)
     Ya ku bayin Allah! Ko kun san wannan ni'ima mafi girma wanda Allah ya yi ga mutum ya kuma mutunta shi da ita? Lalle ita ce ni'ima ta fidira, to menene hakikanin fidira, ana nufi da fidira halin da Allah ya halicci mutum a kai, mai iya karbar kadaita Allah shi kadai ba Ubangiji koma bayanSa, kuma ba abin bauta bayan shi, mai kaunar Alheri mai kin sharri mai karkata zuwa ga biyayya, mai gano munin abubuwan da aka haramta, mai sanin gaskiya a dunkule, kuma masanin bata a dunkule, da ace wannan fidirar da Allah ya halicci mutum a kai ta kubuta daga shaidanun mutane da aljanu da abubuwa masu tasiri da ke iya sanja ta to da ta zabi tauhidi da musulunci, sai dai wannan fidira bata iya wadata da kanta wurin sanin gaskiya daki- daki daya -bayan daya kuma ta yi aiki da shi haka ma sanin sharri da bata daya bayan daya da nesatansu, to don haka ne Allah Mai tsarki ya turo manzanni, kuma na karshen su shine Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi don su kiyaye fidira  kuma su koyar da ita sharia su taimake ta da haske na wahayi a matsayin manhaji na rayuwa, na daga cikin dalili da ke nuni cewa fidira ita ce halin da Allah ya halicci mutum a kai da lafiyayyar dabi'a mai iya amsar addini mai son musulunci akwai fadin Allah Madaukakin sarki ( ka tsayar da mafiskantar ka ga addini kana mai totar izuwa gare shi kirar Allah ce wacce ya kera mutune a kanta, babu musanyawa ga addinin Allah)  Ibnu kasir Allah ya masa rahama yace a cikin tafsirisa : ( ma'anarsa Allah Madaukaki ya daidaita halittunsa gaba dayansu a kan fidira bisa dabia mikakkiya da ba a haifan kowa face a kan haka, ba fifiko tsakanin mutane cikin haka)  ta tike.
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Dukkan abin haihuwa ana haifansa ne akan musulunci to iyayensa ne ke yahudantar da shi ko kiristantar da shi ko majusantar da shi, kamar yadda dabba lafiyayya kan haifi lafiyaya babu wani abu da ku ke gani na gutsurarren hanci ko kunne.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
 An karbo daga Iyad dan  Himar Allah ya kara yarda a gare shi, yace watarana Annabi ya yi huduba sai ya fada a cikin hudubar tasa : lalle Ubangiji na ya umarce ni da na sanar da ku abin da baku sani ba. dukkan dukiyan da na bawa bayi na na halal , lalle na halicci bayi na akan addini hanifiya gabadayansu sai shaidanu suka zo musu suka batar da su daga addinin su. suka haramta musu abin da aka halatta musu suka umarce su da su yi shirka da abin da ban saukar da shi ba na hujja)  Muslim ne ya rawaito
Imamul Bagawi Allah  ya mishi rahama ya ce a cikin tafsirinsa: "Ance ma'nansa dukkan wani abin haifa ana haifansa ne a farkon halittansa bisa fidra wato dabi'u masu lafiya da halaye da suke a shirye don karban addini da zai tafi ne bisa lazimtar ta sabo da wannan addinin kyanshi na nan cikin hankali sai dai kawai zai kauce ne daga wannan zuwa wanin shi sabo da wata musiba da ta faru na daban kamar koyi ko kwaikwayo, da mutun zai kubuta daga wannan musibun to ba zai kudurta wani abu ba sai addini) . maganar ta kare.
 wato fidra ana nufi da ita mahalli na imani wanda shi ne dabia'n da mutun ya tafi a kan shi wanda aka halicce shi akanta  a halinsa na dan adam kuma zuciyarsa a shirye ta ke don karban ilimi mai amfani da aiki na kwarai,  ma'ana na biyu a tafsirin fidra shi ne hasken wahayi da ilimin sharia.
Ibnu abbas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : "Babu canji ga halittan Allah ai ga addinin Allah"
Imamul Buhari ya ce : "fadinsa la tabdila li kalkillah ma'ana babu canji ga halittan Allah lidinillahi wato dabiyun mutanen farko shi ne addinin mutanen farko addini da fidra kuma shi ne al islam .
maganan ya tike.
 To sai ya bayyana cewa fidra ita ce mahalli ko bigire na imani da addini shi ne abin da aka haifi mutun akai na daga halitta mikakkiya ko dabi'a mikakkiya wanda ana nufin da fidra shi ne halin da ya ke cikinta  na asali shi ne na shari'a da imani.
Zan koro misalai na wadannan ma'anoni biyu, kamar misalin fidira da aka haifi mutum a kai, kamar misalin fitila ne na wutan lantarki wanda aka sana'anta aka yi shi ya rika karbar  wutar lantarki, shi wutan lantarki kamar ilimi ne da wahayi da ke cikin zuciya idan aka hada kwan lantarki da wayan lantarki mai wuta sai ya yi haske ya haskaka ya bada launi, idan ba a hada su ba to ba dayansu da zai amfanar shi kadan shi wurin haskakawa, to haka nan ma fidira ba za ta amfanar da ma'abocinta ba sai da ilimi mai amfani da aiki na kwarai.
    Fidira ita ce abin da Allah ya karrama mutum da ita ya fifita shi da wannan fidira wacce da ita ne ya ke sanin ma'arufi ya ki abu na munkari  ya siffanta abu mai kyau da kyau ya munanta abu  mara kyau, idan fidira ta juya ta rushe to kuwa mutum ya zama mamaci ko da yana tafiya a  doron kasa, Allah Madaukakin sarki ya ce :( shin kuma wanda ya kasance matacce, sa'annan muka rayar da shi, kuma muka sanya wani haske dominsa yana tafiya da shi, yana zama kamar wanda misalinsa yana cikin duffai, shi kuma ba mai fita ba daga gare su.)
Fidirar mutum ba ta samun kiyayewa ta karu da haske da sheki ta cika a karfi da rayuwa face da ilimi mai amfani da aiki na kwarai, da imani da aiki na da'a, domin da'a ke ciyar da ita ta sanya ta ta yi karfi, kuma nesatan abubuwan da aka haramta na kare ta daga abubuwa  masu darkakewa, duk wani umarni na wajibi ko mustahabbi na kiyaye Fidira ya raya ta    Allah Madaukakin sarki ya ce :( ya ku wadanda suka yi imani ku amsa wa Allah kuma ku amsa wa  Manzo idan ya kiraye ku zuwa ga abin da yake rayar da ku).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( Abubuwa goma suna cikin fidira : rage gashin baki da barin gemu da yin aswaki da shaka ruwa da yanke kumba da wanke matattara da ke tsakanin yatsu,da cire gashin hamata, da tsarki da ruwa, wato istinja'i) Muslim ne ya rawaito.
 Idan wadannan ta'adodin na cikin  Fidira to wasunsu na daga farillu sun fi dace wa su shigo ciki,
An karbo daga Bara'u dan Azib Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da ni :idan kazo kwanciya to ka yi alwala, alwala irin na salla, ka kishingida a baryarka na dama, ka ce : ya Allah na mika rayi na a gare ka na fiskantar da fiska ta a gare ka, na fawwala al'amari na zuwa gare ka, na komar da baya ta zuwa gare ka, halin kwadayi da tsoro  gare ka, ba mafaka da matsirata daga gare ka sai izuwa gare ka, na yi imani da littafinka da ka saukar, da Annabinka da ka turo, to idan ka mutu to zaka mutu ne a kan fidira ka sanya su karshen abin da za ka fadi.)Buhari da Muslim ne suka rawaito.
 Idan fidira ta kasance ita ce sa'adar mutum ta hanyar gyaruwarta to lalacewarta kuwa ita ce daidaicewar mutum da walakantarsa da hasararsa to ya wajaba mutum ya nesaci abin da zai sanja ta ya lalata ta, kuma mafi hadarin aiki da zai sanja ta ya lalata ta shine shirka, wato hada Allah da wani a bauta, ko sifanta Allah da abin da ya tsarkaka daga shi, na daga da ko aboki, kamar fadin mushrikan larabawa kafin turo Manzo na cewa : Mala'iku 'ya'ya mata ne na Allah, da wanda ya yi irin wannan zance,
 An karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : Allah Madaukakin sarki ya ce :Dan Adam ya karyata Ni , kuma bai dace ya yi hakan ba, Dan Adam ya zage Ni kuma bai dace ya yi hakan ba, Amma karya ta Ni da yayi ita ce zaton sa da ya yi na cewa ba zan iya maida shi kamar yadda ya ke ba, amma zagi Na da ya yi shi ne cewa da ya yi ina da da, tsarki ya tabbata a gare Ni da na riki da,) Buhari ne ya rawaito. A hadisin Abu Huraira :Amma zaginsa gare Ni cewarsa : Allah ya riki da  Alhali kuwa Nine Allah tilo Assamad bai haifa ba kuma ba a haife shi ba, bai da wanda yake kininSa,
Wannan yayi nuni da fadinsu ya fi muni a kan masu bautan gumaka. shirka Allah ba ya gafarta shi sai da tuba Allah  Madaukakin sarki ya ce :( lalle wanda ya ke hada Allah da wani to hakika Allah ya haramta Aljanna a gare shi kuma babu wasu mataimaka ga azzalumai )
Na daga cikin abin da ya ke sauya fidra kuma ya bata ta akwai zunubai da aikata sabo Allah bai halaka alumman da su ka gabace mu ba face sabo da lalacewan fidransu da kuma ketare iyakansu daga umarnin Allah mabuwayi da daukaka Allah bai tsiratar da muminai ba da su ke tare da su face da gyaruwan fidrarsu Allah madaukakin sarki ya ce (sai muka tsiratar da wadanda suka yi imani sun kasance kuma suna jin tsoron Allah) ga wannan aya akwai abin lura cikin halaka mutanen ludu gaba dayansu ba wanda ya tsira daga cikin su ko da mutun daya saboda lalacewan fidran su da kuma juyawanta suna aikata alfahasha mai mummuna ba wanda ya tsira sai ludu amincin Allah su tabbata a gare shi da 'ya'yansa mata biyu
Sabo yana lalata fidra ta fiskan abin lura shi ne ko wani Annabi da Allah ya halaka alummarsa wasu sashi sun yi imani da shi sai Allah ya tsiratar da su daga shi amma mutanen ludu hakika sabo ya lalata musu fidrar su sai aka yi musu mafi tsananin ukuba a doron kasa
Na daga cikin abin da ya ke lalata fidra akwai yin zina domin yana da tasiri wurin kazanta zuciya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (mai zina ba zai yi zina ba a yayin da ya ke zina a halin yana mumini, Barawo ba zai yi sata ba a yayin da ya ke sata a halin yana mumini  mai shan giya ba zai sha giya ba ayayin da ya ke shan giya a halin yana mumini ) Buhari da Muslim ne suka rawaito daga Abi Huraira
  Ibnu mas'ud Alla ya kara yarda a gare shi ya ce: "An hada zina tare da shirka" yana nufin fadin Allah Madaukakin sarki (mazinaci ba zai aura ba face mazinaciya ko mushrika )
To fa giya ita ce ummul kaba'isi wato uwar kazanta Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ku nisaci ummul kaba'isi) Ibnu Hibban ne ya rawaito da baihaki daga hadisin usman Allah ya kara yarda a gare shi manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (giya matattara ce ta laifi) saboda tana rusa fidra ta lalata gudanarwa da hankali, kayan maye da miyagun kwayoyi su suka fi tsananin lalata fidra da hankali kuma su suka fi hatsari ga alumma, to giya illan ta kan iya zame wa kebabbiya ga mai shanta, kuma yana katangewa daga jin alkura'ani wanda shi ne sababin dukkan alheri, kuma yana kai ma'abocin shi zuwa ga ukuba.
 Na daga cikin abin da ya ke lalata fidra akwai zaluncin bayi ga junan su, rushewar duniya na ga zaluntar bayi sashin su ga sashe,   Allah madaukakin satrki ya ce (kuma wadancan alkaryu mun halaka su a lokacin da suka yi zalunci kuma muka sanya lokacin alkawarin ga halaka su)
Ya kai mutum rabautar ka da gyaruwarka da farincikinka da daidaituwan al'amuranka gaba dayansu da gadanka ga Aljanna mai ni'ima da tsirar ka daga azaban jahima na ga kiyaye daidaitacciyar fidira ta hanyar riko da wannan sharia ta musulunci mikakkiya, Allah Madaukakin satrki ya ce (kuma lalle wannan ne tafarki na yana madaidaici sai ku bi shi kuma kada ku bi wasu hanyoyi su rarraba ku daga barin hanya ta, wannan ne Allah ya muku wasiyya da shi ko za ku ji tsoron Allah)
 Allah ya sanya mini albarka ni da ku a Alkur'ani mai girma ya kuma amfane ni da ku da abin da ke cikinsa na ayoyi da ambato mai hikima.

Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai Mai karfi, Majibincin masu tsoron Allah, ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode masa bisa ga ni'imominSa da ba mai iya kididdige su sai shi, muna gode masa irin godiyar masu shukura, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya,  Allan mutanen farko da na karshe, kuma na shaida Annabinmu kuma shugabammu Muhammdu bawansa ne kuma ManzonSa ne mai gaskiya amintacce Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma Manzon ka muhammad da iyalansa da sahabbansa da wanda suka bi su da kyautatawa zuwa ranan sakayya, bayan haka ku ji soron Allah madaukaki cancancin soron shi ku kiyaye saba wa shari'arsa ba wanda zai rabauta cikin wanda su ka saba mishi. 
Ya ku bayin Allah ku kyautatawa kanku ta hanyar daidaituwa kan tafarki, hakika Allah ya kyautata muku da shiriya da nau'ka na karama ya kai mutun : ka tsarkake ranka daga kazantaccen abubuwa ka tsarkaketa ta hanyan amsa kira da karban abinda Ubangijinka ke kiran ka zuwa gare shi Allah Madukakin sarki ya ce (ku amsa wa Ubangijinku tun gabanin wani yini ya zo ba bu makawa gare shi daga Allah ba ku da wata mafaka a ranan nan kuma ba ku iya yin wani musu )
Idan ka amsa ya kai mutun ga umarni to za ka tashi da shi idan ka amsa kira ga hani kuma to za ka nesace shi, to hakika matsayinka zai daukaka a wurin Ubangijinka kuma ka karrama  kanka ka gode wa ni'man fidra wacce ta ke ita ce mafi girman ni'ma. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Allah na daga darajan wasu mutane da wannan Alkur'ani, kuma ya kan yi kasa da wasu dalilin shi)
da kuma abin da al ummu su ka canja wanda ta wofanta daga fidrar Allah ba su amsa kiran Manzanninsu ba sai su ka walakanta a wurin Allah kuma za su auka cikin tozarci da kuma hasara ) Allah madaukakin sarki ya ce:( saboda haka ko wannen su mun kama shi da laifinsa daga cikin su akwai wanda muka aika iskar tsakuwa akan sa kuma daga cikin su akwai wanda tsawa ta kama kuma daga cikin su akwai wanda muka birkice kasa da shi , kuma daga cikinsu akwai wanda muka nutsar, baya yiwuwa ga Allah ya zalunce su , amma sun kasan ce kan su su ke zalunta )

Ya ku bayin Allah! lallai Allah da mala'ikunsa suna salati ga Annabi, ya ku wadanda su ka yi imani ku yi salati gare shi da aminci tabbatacce .      

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق