Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah Mai mulki Tsarkakakke Mai aminci, Ma'abocin daukaka da
karramawa, Ubangijinmu sunayenSa sun tsarkaka,sifofinSa sun daukaka,shi yana
nan ne kamar yadda ya yabi kanSa, ba zamu iya kididdige yabo a gare shi ba, yabo
ya tabbata a gare shi duniya da lahira a koyaushe,Ina kyautata yabo ga Ubangiji
na kuma ina gode mishi,bisa ga abin da ya bada na baiwa da falaloli da alheri
daban daban wadanda muka san su da wadanda ba mu san su ba,shine majibincin
ni'imtarwa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah.ba shi da abokin
tarayya Ma'abocin buwaya da babu zalunci. Na shaida Annabinmu kuma shugabanmu
Muhammad bawansa ne kuma manzonSa ne, wanda aka turo shi da haske
bayyananne,wanda da shi ne Allah ya gusar da shirka da duhu, ya Allah ka yi
dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma ManzonKa Muhammad da
iyalansa da sahabbansa masu karamci.
Bayan haka ku ji tsoron
Allah ya ku bayin Allah ta hanyar kusantar shi da nagartattun ayyuka,da ki da
nesatan munanan ayyuka, duk wanda ya ji tsoron Allah to Allah zai jibince shi,wanda
ya bi son ransa ya fifita duniyarsa to ya yi kan shi hasara ya sarayar da
ni'ima dawwamammiya a lahirarsa,Allah Madaukakin sarki ya ce :(To duk wanda ya yi dagawa ya fifita rayuwar duniya,to
lalle (wutar) Jahima ita ce makoma,To amma wanda ya ji tsoron matsayin
Ubangijinsa ya hana rayi ga sha'awe sha'awenta to Aljanna ita ce makoma.)
Ya ku musulmai ! Allah Tabaraka
wa taala ya kiraye ku da suna na imani sifa mafi daraja ga mutum, da cewa ku yi
tawassuli gare shi da ayyuka nagari ku kiyaye su daga abin da zai bata su sai
Allah yace : :(ya ku wadanda suka yi imani ku ji
tsoron Allah ku nemi kusanci zuwa gare shi ku yi jahadi a tafarkinSa ko zaku
samu rabauta.)
Wasila :kusanci ya hada
dukkan da'a: wato bin umarni da barin hani, wasila ta tattaro gabadayan
hanyoyin da'a, da dukkan kofofin alheri
da abinda ke tsiratarwa daga ukuba.
Kuma abinda yafi game dukkan hanyoyin ayuka na gari , da kuma
yin katanga daga abubuwa masu halakarwa shi ne ; ambaton Allah Tabaraka wa ta'ala
, kuma shi ke kammala farillu da wajibabbu
ya kuma kankare tawaya da aka
samu a ibadodi, ladan kewawan ayuka na
girmama tare da shi kuma
ya goge munanan ayuka , ladan shi ya kai lada da
falalar sa da girman matsayin sa
wurin daraja da daukaka da haske da alheri wanda ya kai har Allah ya farlan ta shi a
salla da hajji da kuma sauran ayuka na
da'a ,
kuma shari'a ta kwadaitar bisa ga
dukkan yanayi ko hali , kuma rukunin
addini na farko shi ne ambaton Allah madaukakin sarki , da
fadin na shaida ba abiun bautawa da gaskiya sai Allah madaukakin sarki , kuma
na shaida Annabi Muhammadu Manzon Allah ne,
kuma dukkan shari'o'i na musulunci
ta zo da wannan zikiri da
kuma rarrabewa game da wannan shahada ,
to shaidawa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah tauhidi ne ga abin bauta tsarki ya tabbata a gare shi kuma .
(Ya ku wadan da suka yi imani , kada ku gabata (da kome)
gaba ga Allah da Manzon sa kuma ku yi da'a ga Allah da takawa lalle
Allah mai ji ne masani ) .
Allah
bai yi umarni ba da a yawaita wani abu kamar yanda ya yi umarni da a yawaita
zikiri (Ya ku wadanda su ka yi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa kuma ku yi tasbihi a gare shi safiya da
maraice ).
Face
abinda ya zo na daga sallama , yawaita
salati da aminci ga shugaban halittu tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi , misali fadin sa tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi (Ku
yawaita yi min salati a ranar juma'a, domin ana bijiromin da salatinku a gare
ne)Hadisingantacce Ahmad ne ya rawo da Abu daud
da ibnu ha ya rawaito Allah y7a kara yarda da shi, da kuma fadinSa tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi, duk wanda ya yi salati gud to Allah zai
yi mishi salati goma kuma ya yafe masa kusakure goma, kuma a daga shi da
darajoji goma) Hadisi ne ingantacce da Nas'I ne ya rawaito da ibnu Ha daga
hadisin Annas dan Maiki).
Wamma salati da aminci
sakayya ne gaAnnabinmu daga musulmi sakayya ga musulmi ga Annabi) kuma
adu'a ne a gare shi bisa ga abin da ya tabbatar na addini, kuma ya yi jahadi
mafi kamala, da abin da ya bada na ya daga alheri
mai yalwa da nasiha na gaskiya to dukkan alheri ga musulmi Allah ya gudanar
da shi ne, haka ma dukkan lada Allah ya
gusdanar da shi ne ta hanu Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare
shi , kuma aljanna tafarkin sa ne . Yin salati agare shi ibada ne ga
Allah mabuwayi da daukaka na daga cikin abin da ya zo a falalar zikiri (ku ambaci Allah ambato mai yawa ko zaku rabauta). Da fadin Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi,: misalin wanda ya ke
ambaton Ubangijinsa da wanda bai ambaton sa, misalin matacce ne da rayayye,)
Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Daga hadisin Abu musa Allah ya kara yarda a
gare shi
(Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce ase ba zan baku labarin mafi alheri da tsarkaka na daga ayukan alherin ku , a wurin
mamallakin ku kuma ya fi daga darajojin
ku kuma ya fi alheri a gare ku daga
ciyar da azurfa da zinari kuma ya fi
alheri a gare ku da ku hadu da makiya a
wurin mamallakin ku , ku sare wuyan
shi kuma ya sare wuyan ku sai suka ce e , ya Manzon Allah sai ya ce ambaton Allah ).
Hadisi
ne ingantacce Ahmad ne ya rawaito shi da Tirmizi da Hakim
daga Hadisin Abi Darda Allah ya kara yarda a gare shi
(An
karbo daga Abu sa'id Al-khudri Allah ya kara yarda a gare shi ya ce an
tambayi Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi wace ibada ce tafi daraja a wurin Allah ranar alkiyama sai ya ce ;-
masu ambaton Allah dayawa Tirmizi ne ya rawaito )
An karbo daga Abdullahi Dan Busur Allah ya
kara yarda a gare shi ya ce :- Wani
mutum ya zo wurin Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce :- Lallae shari'o'i na musulunci sun
yawaita a gare ni to a bamu kofa da zamu
yi riko da shi gamamme sai ya ce kada
harshen ka ya gushe yana danye daga
ambaton Allah mabuwayi da daukaka Ahmad
ne ya rawaito da Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibban ).
Shi zikiri yana tsarkake ayyuka kuma ya cika tawayanta da shi
ne ma 'abocin shi ke riskan abin da ya sere, yana goge zunubai,
Ambaton Allah mai tsarki da daukaka na da matakai guda uku: 1.Matakin farko
Anbaton Allah daga wanda ya so.kuma saki, kuma zai bashi lada Allah da karamcinsa da da kyautar sa.
Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi,ya ce Allah madaukaki ya ce: (Ni ina
inda bawa na ya zace, ni ina tare da shi,in ya ambace ni idan ya ambace ni a
ransa sai na ambace shi a rai na.)Buhari da muslim ne suka rawaito daga hadisin
Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi.
2 mataki na biyu shine mataki
na tsakiya shine musulmi ya ambaci Ubangijinsa da harshensa, a wani lokaci ya
gafala daga halarto da ma'anan na abinda yake anbatawa a zuciyarsa, to shi ma
yana cikin alheri mai girma ladan wannan matsayi ba wanda zi kididdige shi sai
Allah, shine ya fi lada akan mataki na farko sabo da karn furuci da harshe
Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi,ya ce: (Lalle mutum
ya kan yi furuci da wata kalma ta yardar Allah ba tare da ya kula da ita ba
amma Allah zai daga darajan shi da ita) Buhari ne ya rawaito daga hadisin Abu
Huraira.
3. Mataki na uku na zikiri
shi ne Harshe ya yi ambato na zikiri kuma zuciya na tare da shi wurin fahimta
ta sakon zikirin tare da halarto da girman Allah Mabuwayi da Daukaka lokacin
zikirin,wannan matakin na zikiri shi ya fi kowanne a matakan zikiri,ma,abocin
shi shine na gaba gaba wurin alheri, mafi daukaka na darajoji. Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce: (Bawa ba zai mutu ba a halin ya shaida ba abin bautawa
da gaskiya sai Allah, kuma ni Manzon Allahyana mai gaskiya har zuciyarsa face
ya shiga Aljanna.) Ahmad ne ya rawaito daga hadisin Rafa'at Aljuhani Allah ya
kara yarda a gare shi. A wannan hadisi an samu daidaiton harshe tare
da zuciya wurin anbato.
An karbo daga Abu Huraira
cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da shi: (Duk wanda ka hadu da shi bayan wannan kango yana mai
shaida wa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah zuciyar sa na sakankancewa da
shi to ka mar albishir da Aljanna. Muslim ne ya rawaito. Ma'ana
anbaton Allah tsarki ya tabbata a gare shi, shi ne kyautata yabo ga Allah
Mabuwayi da daukaka da Tahlili(cewa la'ilaha illallah) da Kabbartawa
cewa Allahu Akbar, da godiya da tasbihi da lahaula wala kuwwata illa billah
Ma'abocin girma da daukaka da yawaita istigfar da yawaita adu'a, da
salati da aminci bisa ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi na
daga cikin zikiri, da tsarkake Ubangijinmu Madaukaki daga dukkan tawaya da
tsarkake shi daga dukkan abin bai dace ba da matsayinSa da kimarSa da buwayarSa
da girmame girmamenSa da cikar kamalarsa da kyaunSa, da kore kamanta shi da
daya daga cikin halittunSa Madaukaki da tsarkakakke. Mafi girman yabo shi ne tabbatar
da godiya ga Ubangijin talikai shine a yabe shi da sunayenSa kyawawa da sifofinSa Madaukaka, da ayyukanSa
masu hikima,kamar yadda ya ke a Ayatul kursi da karshen suratul Hashri,
da girmama Ubangijinmu. Ta hanyar anbaton Ubangijinmu shima ta haryar anbaton
ni'imominSa ga halittu. Allah Madaukakin Sarki ya ce : (ya ku mutane ku tuna ni'imar Allah a kan ku, shin kuna
da wani Mahalicci koma bayan Allah da zai azurta kudaga sama da kasa).
Allah mai tsarki da daukaka
yace (ku
tuna ni'imar Allah a kan ku a yayin da kun kasance makiya sai ya hada zukatarku
sai kuka zma 'yan uwan juna da ni'imar Allah bayan kun kasance kuna gaban rami
na wuta sai ya tseratar da ku daga gare ta). Da sauran ayoyi da
Zikiri abu ne mai sauki a harshe
mai nauyi a mizani ba a samun fa'idodi da shi kuma zukata basu tsarkaka da shi
ayyuka su gyaru da rayuwa face akwai kaunar Allah da kaunar ManzonSa tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi,
Mafi falalan zikiri shine
Karatun Alkur'ani, don shine ya kunshi dukkan yabo ga Ubangijin talikai, ya
kuma ambaci ni'ima da da bayanin sharia daki-daki ya kwadaitar bisa dukkan
alheri.ya yi gargadi bisa dukkan sharri.
Ya ku musulmai wannan shi ne
ambato cikin alherinSa da albarkansa da amfaninsa da haskensa.
Amma game da ladansa yana da
abin da ido bai gani ba zuciyar mutum bata taba hararo wa ba,na daga cikin
ladan zikiri akwai abin da ya zo daga Abu Huraira Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi,ya ce: (Duk wanda ya ce :"Ba
abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya mulki
da yabo na shi ne yana da iko ga dukkan komai" a farkon wuninsa, zai
kasance a gare shi daidai da 'yanta wuyaye goma kuma zaa rubuta mishi lada dari
a goge mishi alhaki dari, zai zame kariya ne a gare shi daga shaidan a wannan
wunin nasa, har ya yi yammaci kuma ba wanda zi zo da irin wannan abin da ya zo
da shi face mutumin da ya yi aiki sama
da wannan.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
An
karbo daga Umma Hani Allah ya kara yarda a gare ta ta ce , na ce ya Manzon
Allah: Umarce ni da wani aiki da zan yi ina zaune sai yace : ki tasbihi ga
Allah sau dari domin yana daidai da 'yanta wuyaye dari ga 'ya'yan isma'il, ka
gode wa Allah guda dari domin yana daidai da dawakai dari da sirjinsu da linzamin su suna dauke da kaya a
tafarkin Allah, ki yi kabbarori dari domin yana daidai da rakumi dari da aka sa
musu alama a wuyansu karbabbu,ki yi halala dari zai cika tsakanin sama da
kasa,) Hadisi ne hasan, Ahmad ne ya rawaito da Nasa'I da Hakim.
An
karbo daga Nu'uman dan Bashir Allah ya kara yarda a gare shi yace Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Na daga cikin abin da ku
ke ambatawa na girman Allah Akwai: subhanallahi walhamdu lillahi wa la'ilaha
illalahu ana furta su a saman al'arshi da sauti kamar kukan zuma, ana
anbata su da masu yin su, hadisi ne ingantacce ibnu maja ne ya rawaito da
Hakim.
Daga
Mu'azu Allah yarda da shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi yace :"yan aljanna basu da na sani face ga sa'a da ta wuce su
basu ambaci Allah ba a cikinta,) Hadisi ne sahihi Dabarani ne ya rawaito. Da na
sani da suke yi sakamakon abin da suka gani ne na girman lada na zikiri, Na
daga cikin lada na zikiri yana kiyaye ma'abocin shi daga shaidanu,
An
karbo daga Haris dan Haris Al'as'ari Allah ya kara yarda a gare shi daga Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace :Allah ya umarci yahya
dan zakariyya da ya umarci banu Isra'ila da wasu kalmomi biyar daga ciki akwai
ambaton Allah, domin misalin haka kamar misalin mutum ne, makiyi ya fito a
bayan shi yana yakan shi har yazo wani katang da zai kare shi sai tare kansa
daga gare shi, haka nan ne bawa ba ya iya kare kansa daga shaidan sai da mbaton
Allah) Hadisi ne ingantacce.Tairmizi ne ya rawaito da Ibnu hibbanda Hakim.
Mafi girman lada na zikiri
shine rabauta da Aljanna da tsira daga wuta kuma yardar Allah ya fi girma. Na daga
cikin falalan zikiri Allah zai kare ma'abocin shi daga damuwoyi da tsanani da
abubuwa masu halakarwa, Allah Madaukakin sarki ya ce: (kuma ba don ya kasance cikin masu tasbihi ba da ya zauna a cikinsa
har zuwa ranar da zaa tada su,)
Na daga cikin ladansa Allah tsarki ya
tabbata a gare shi zai daga anbaton ma'abocinzikiri a duniya da lahira Allah
Madaukakin sarki ya ce: (ku ambace ni zan anbace
ku ku gode min kada ku kafurce min)
Na daga cikin ladansa ya na
kara karfin ruhi da gangan jiki, yana taimakawa wurin ibada yana kangewa daga
abin da aka haramta, kuma yana saukake arziki da shi, An karbo dagaAbdullahi danAmrAllah ya kara yarda a gare shi ya ce nuhu ya ce ga dan sa kuma ina ma wasiya
da cewa tsarki ya tabbata ga Allah domin ita ce salati halittu da tasbihinsu da
ita ake azurta halittu)Hadisi ne ingantacce nasa'I ne ya rawaito da
Hakim
Na daga cikin ladan zikiri akwai
barranta daga munafunci, kuma shine musiba mafi girma a addini, manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Manzon Allah ya kasance yana
zaben kalmomi dunkulallu a wurin adu'o'i da zikiri, na daga cikin dunkulallun
aduo'i akwai abin da Annabi ya koyar da Juwaira
diyar Haris Allah ya kara yarda a gare ta, Tsarki ya tabbata ga Allah da
godiyarsa adadin halittunSa da yardar kansa da nauyin Al'arshinSa da tawadan
kalmominSa,tsarki ya tabbata a gare shi daidai adadin halittunSa,tsarki ya
tabbata a gare shi gwargwadon yardarsa tsarki ya tabbata ga Allah daidai nauyin
Al'arshinSa. Tsarki ya tabbata ga Allah kwatankwacin tawadan kalmominSa. Muslim
ne ya rawaito.
An
karbo daga Abu Umama Allah ya kara yarda a gare shi yace: Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Ashe ba zan koyar da kai fiye da
zikirinka da ka ke yi dare zuwa wuni da
wuni zuwa dare ba, Tsarki ya tabbata ga Allah iya adadin abin da ya halitta,
tsarki ya tabbata a gare shi cikin abin da ya halita, tsarki ya tabbata adadin
dukkan komi, tsarki ya tabbata a gare shi cikin dukkan komai tsarki ya tabbata a gare shi adadin abin da littafin sa ya kididdige , tsarki ya tabbata gare shi
cikin abin da littafin shi ya
kididdige godiya ya tabbata ga Allah
adadin abinda ya halitta , godiya ya tabbata ga Allah cikin abin da ya halitta
godiya ya tabbata ga Allah adadin dukkan komai , godiya ya tabbata ga Allah cikin dukkan komai
, godiya ya tabbata ga Allah adadin abin
da ya iyakance , godiya ya tabbat ga
Allah cikin abinda littafin sa ya
kididdige Hadisi ne Hassan Bazzar ne ya rawaito shi da Dabarani .
Allah madaukakin sarki ya ce :- (Da masu ambaton
Allah da yawa maza da masu ambaton Allah da yawa mata Allah ya tanada musu
gafara da kuma lada mai girma) .
Allah ya sanya mini albarka
ni da ku cikin Alkur'ani mai girma .
HUADUBA NA BIYU:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai majibincin salihai a mishi biyayya ya gode asaba mi shi ya gafarta ina godewa Ubangijina bisa ga ni'imomi wanda wanin sa ba zai iya kididdige su ba wanda muka san su da wanda ba mu san su
ba na shaida ba abin bautawa da gaskiya
sai Allah shi kadai yake ba shi d
aabokin tarayya mai yawan azurtawa ma 'aboci karfi kuma na shaida Annabin mu kum shugaban mu
Annabi muhammad bawan sa ne kuma Manzon sa ne,
amintacce Ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga bawan ka
kuma Manzon ka Muhammad da iyalan shi da sahabban shi har zuwa ranar
sakayya .
BAYAN HAKA:
Ku ji tsaoron Allah da aikata ayyuka na gari da uyin nesa daga abubuwan da aka haramta .
YA KU BAYIN ALLAH:-
Ku yi gudu zuwa ga Allah daga
gafala da juya baya da rudi irin na dogon buri domin ku dinnan kuna da lokaci da aka yanka
mu ku , wanda ke kusanto da duk wani abu
na nesa yake kodar da duk wani sabon abu ,
hakika Allah ya umarce ku da koyi da Manzo tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
a fadin sa madaukaki :- (Hakika kuna da abin
koyi mai kyau ga Manzon Allah ga duk wanda
ke fatan Allah da ranar lahira ya
kuma ambaci Allah da yawa ).
An
karbo daga Aisha Allah ya kara mata
yarda ta ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance
yana ambaton Allah a duk halin da ya ke . Muslim ne ya rawaito)
Zaid Dan Aslam ya ce '' Musa alaihissalam ya ce:-
'' Ya Ubangiji ka mini ni'ima mai yawa
to ka nusar da ni zuwa ga abin da zan gode maka mai yawa sai ya ce ka ambace ni da yawa ,
to, idan ka ambace ni da yawa to
hakika ka gode mi ni , idan kuma ka
manta ni to, hakika ka butulce mi
ni Baihaki ne ya rawaito a cikin
Ashhu'ab .
Magabata
na kwarai Allah ya yarda da su sun kasance
suna dimantan ambaton Allah tabaraka wata'ala sabo da cikar kaunar su ga
shi .
(Abu
Huraira ya kasance yana da wani zare a cikin shi akwai kulli dubu ba ya bacci har sai ya yi tasbihi da shi ,
Abu Nu'aim ne ya rawaito a cikin Alhilya
) .
Galibin maganan Ibn Sirin shi
ne subhanallahil azim (tsarki ya tabbata ga Allah mai girma ), Khalid Dan
Ma'adan ya kasance yana tasbihi ko wani rana dubu araba'in na tasbihi banda
abin da ya ke karantawa na Alkur'ani Abu Nu'aim ne ya fito da shi a cikin Alhilya .
Musulmi a wannan zamanin ya fi tsananin bukatan zuwa ga zikiri sakamakon abin da ya yawaita na
fitintinu da kuma abin da ya ke zo ma
zukata na gafala , da kuma abin da ya sami basira na
daga sha'awe-sha'awe da shubuhohi da bin soye-soyen rayuka da kuma abin da ya yawaita na rudi
da kawar duniya da adon ta, ya dace musulmi ya rika daga littatafan azkar abin da
zai bude mishi ido kuma ya nemi fahimtar sa ya yi aiki da shi , na daga cikin mafi amfanin littatafai na
ambato ko zikiri akwai TUHFATUZZAKIRINA
da wanin shi,
YA
KU BAYIN ALLAH:-
Lallai
Allah da Mala'ikun sa suna salati ga
Annabi
(Ya
ku wadan da suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce …………………………)
zuwa karshen adu'a.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق