الأحد، 3 نوفمبر 2019

FALALAN ZIKIRI A MUSULUNCI


Hudubar Masallacin Annabi na sheikh Aliyu Bin Abdurrahman Alhuzaifi 4-3-1441AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mai mulki Tsarkakakke Mai aminci, Ma'abocin daukaka da karramawa, Ubangijinmu sunayenSa sun tsarkaka,sifofinSa sun daukaka,shi yana nan ne kamar yadda ya yabi kanSa, ba zamu iya kididdige yabo a gare shi ba, yabo ya tabbata a gare shi duniya da lahira a koyaushe,Ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi,bisa ga abin da ya bada na baiwa da falaloli da alheri daban daban wadanda muka san su da wadanda ba mu san su ba,shine majibincin ni'imtarwa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah.ba shi da abokin tarayya Ma'abocin buwaya da babu zalunci. Na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma manzonSa ne, wanda aka turo shi da haske bayyananne,wanda da shi ne Allah ya gusar da shirka da duhu, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma ManzonKa Muhammad da iyalansa da sahabbansa masu karamci.
Bayan haka ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah ta hanyar kusantar shi da nagartattun ayyuka,da ki da nesatan munanan ayyuka, duk wanda ya ji tsoron Allah to Allah zai jibince shi,wanda ya bi son ransa ya fifita duniyarsa to ya yi kan shi hasara ya sarayar da ni'ima dawwamammiya a lahirarsa,Allah Madaukakin sarki ya ce :(To duk wanda ya yi dagawa ya fifita rayuwar duniya,to lalle (wutar) Jahima ita ce makoma,To amma wanda ya ji tsoron matsayin Ubangijinsa ya hana rayi ga sha'awe sha'awenta to Aljanna ita ce makoma.)
Ya ku musulmai ! Allah Tabaraka wa taala ya kiraye ku da suna na imani sifa mafi daraja ga mutum, da cewa ku yi tawassuli gare shi da ayyuka nagari ku kiyaye su daga abin da zai bata su sai Allah yace : :(ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku nemi kusanci zuwa gare shi ku yi jahadi a tafarkinSa ko zaku samu rabauta.)
Wasila :kusanci ya hada dukkan da'a: wato bin umarni da barin hani, wasila ta tattaro gabadayan hanyoyin da'a, da dukkan kofofin alheri  da abinda ke tsiratarwa daga ukuba.
 Kuma    abinda yafi  game dukkan hanyoyin ayuka na gari , da kuma yin katanga daga abubuwa masu halakarwa    shi ne ; ambaton Allah Tabaraka wa ta'ala , kuma shi ke kammala farillu da wajibabbu    ya kuma kankare tawaya  da aka samu a ibadodi,  ladan kewawan ayuka na girmama  tare da shi    kuma  ya goge munanan ayuka    ,   ladan shi ya kai lada  da  falalar sa da girman matsayin sa  wurin daraja da daukaka da haske da alheri   wanda ya kai har Allah ya farlan ta shi a salla  da hajji da kuma sauran ayuka na da'a  ,  kuma shari'a ta kwadaitar  bisa ga dukkan yanayi  ko hali , kuma  rukunin  addini na farko shi ne ambaton Allah madaukakin sarki  ,  da fadin na shaida ba abiun bautawa da gaskiya sai Allah madaukakin sarki , kuma na shaida Annabi Muhammadu Manzon Allah ne,  kuma dukkan  shari'o'i  na musulunci    ta zo da wannan zikiri  da kuma  rarrabewa game da wannan shahada , to shaidawa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah  tauhidi ne ga abin bauta  tsarki ya tabbata a gare shi  kuma .

        (Ya ku wadan da suka yi imani , kada ku gabata (da kome) gaba ga Allah da Manzon sa kuma ku yi da'a ga Allah da takawa  lalle  Allah mai ji ne masani ) .
Allah bai yi umarni ba da a yawaita wani abu kamar yanda ya yi umarni da a yawaita zikiri  (Ya ku wadanda su ka yi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa  kuma ku yi tasbihi a gare shi safiya da maraice ).
Face abinda ya zo na daga  sallama  , yawaita  salati da aminci ga shugaban halittu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ,    misali fadin sa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Ku yawaita yi min salati a ranar juma'a, domin ana bijiromin da salatinku a gare ne)Hadisingantacce Ahmad ne ya rawo da Abu daud  da ibnu ha ya rawaito Allah y7a kara yarda da shi, da kuma fadinSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, duk wanda ya yi salati gud to Allah zai yi mishi salati goma kuma ya yafe masa kusakure goma, kuma a daga shi da darajoji goma) Hadisi ne ingantacce da Nas'I ne ya rawaito da ibnu Ha daga hadisin Annas dan Maiki).
Wamma salati da aminci sakayya ne gaAnnabinmu daga musulmi sakayya ga musulmi ga Annabi) kuma adu'a ne a gare shi bisa ga abin da ya tabbatar na addini, kuma ya yi jahadi mafi kamala, da abin da ya bada na ya daga   alheri mai yalwa  da nasiha na gaskiya  to dukkan alheri ga musulmi Allah ya gudanar da shi  ne, haka ma dukkan lada Allah ya gusdanar da shi ne ta hanu Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi , kuma  aljanna tafarkin sa ne .  Yin salati agare shi ibada  ne   ga Allah mabuwayi da daukaka na daga cikin abin da ya zo a falalar zikiri (ku ambaci Allah ambato mai yawa ko zaku rabauta).  Da fadin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,: misalin wanda ya ke ambaton Ubangijinsa da wanda bai ambaton sa, misalin matacce ne da rayayye,) Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Daga hadisin Abu musa Allah ya kara yarda a gare shi

(Manzon Allah tsira da  amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ase ba zan baku labarin mafi alheri da tsarkaka  na daga ayukan alherin ku , a wurin mamallakin ku  kuma ya fi daga darajojin ku  kuma ya fi alheri a gare ku daga ciyar da azurfa da zinari  kuma ya fi alheri a gare ku da ku hadu da makiya  a wurin mamallakin ku ,  ku sare wuyan shi   kuma ya sare wuyan ku  sai suka ce e , ya Manzon Allah   sai ya ce ambaton Allah ).
Hadisi ne ingantacce Ahmad  ne  ya rawaito shi  da Tirmizi  da Hakim  daga Hadisin Abi Darda Allah ya kara yarda a gare shi

(An karbo daga Abu sa'id Al-khudri Allah ya kara yarda a gare shi ya ce an tambayi  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wace ibada ce tafi daraja  a wurin Allah ranar alkiyama   sai ya ce ;-  masu ambaton Allah dayawa Tirmizi ne ya rawaito )

 An karbo daga Abdullahi Dan Busur Allah ya kara yarda a gare shi  ya ce :- Wani mutum ya zo wurin  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce :- Lallae shari'o'i  na musulunci sun yawaita a gare ni  to a bamu kofa da zamu yi riko da shi gamamme  sai ya ce kada harshen ka  ya gushe yana danye daga ambaton Allah   mabuwayi da daukaka Ahmad ne ya rawaito da Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibban ).



 Shi zikiri yana  tsarkake ayyuka kuma ya cika tawayanta da shi ne  ma 'abocin shi ke  riskan abin da ya sere, yana goge zunubai, Ambaton Allah mai tsarki da daukaka na da matakai guda uku: 1.Matakin farko Anbaton Allah daga wanda ya so.kuma saki, kuma zai bashi  lada Allah da karamcinsa da da kyautar sa.
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce Allah madaukaki ya ce: (Ni ina inda bawa na ya zace, ni ina tare da shi,in ya ambace ni idan ya ambace ni a ransa sai na ambace shi a rai na.)Buhari da muslim ne suka rawaito daga hadisin Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi.
2 mataki na biyu shine mataki na tsakiya shine musulmi ya ambaci Ubangijinsa da harshensa, a wani lokaci ya gafala daga halarto da ma'anan na abinda yake anbatawa a zuciyarsa, to shi ma yana cikin alheri mai girma ladan wannan matsayi ba wanda zi kididdige shi sai Allah, shine ya fi lada akan mataki na farko sabo da karn furuci da harshe
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce: (Lalle mutum ya kan yi furuci da wata kalma ta yardar Allah ba tare da ya kula da ita ba amma Allah zai daga darajan shi da ita) Buhari ne ya rawaito daga hadisin Abu Huraira.
3. Mataki na uku na zikiri shi ne Harshe ya yi ambato na zikiri kuma zuciya na tare da shi wurin fahimta ta sakon zikirin tare da halarto da girman Allah Mabuwayi da Daukaka lokacin zikirin,wannan matakin na zikiri shi ya fi kowanne a matakan zikiri,ma,abocin shi shine na gaba gaba wurin alheri, mafi daukaka na darajoji.   Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce: (Bawa ba zai mutu ba a halin ya shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ni Manzon Allahyana mai gaskiya har zuciyarsa face ya shiga Aljanna.) Ahmad ne ya rawaito daga hadisin Rafa'at Aljuhani Allah ya kara yarda a gare shi. A wannan hadisi an samu daidaiton harshe tare da zuciya wurin anbato.
An karbo daga Abu Huraira cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da shi: (Duk wanda ka hadu da shi bayan wannan kango yana mai shaida wa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah zuciyar sa na sakankancewa da shi to ka mar albishir da Aljanna. Muslim ne ya rawaito. Ma'ana anbaton Allah tsarki ya tabbata a gare shi, shi ne kyautata yabo ga Allah Mabuwayi da daukaka da Tahlili(cewa la'ilaha illallah) da Kabbartawa cewa Allahu Akbar, da godiya da tasbihi da lahaula wala kuwwata illa billah Ma'abocin girma da daukaka da yawaita istigfar da yawaita adu'a, da salati da aminci bisa ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi na daga cikin zikiri, da tsarkake Ubangijinmu Madaukaki daga dukkan tawaya da tsarkake shi daga dukkan abin bai dace ba da matsayinSa da kimarSa da buwayarSa da girmame girmamenSa da cikar kamalarsa da kyaunSa, da kore kamanta shi da daya daga cikin halittunSa Madaukaki da tsarkakakke. Mafi girman yabo shi ne tabbatar da godiya ga Ubangijin talikai shine a yabe shi da sunayenSa  kyawawa da sifofinSa Madaukaka, da ayyukanSa masu hikima,kamar yadda ya ke a Ayatul kursi da karshen suratul Hashri, da girmama Ubangijinmu. Ta hanyar anbaton Ubangijinmu shima ta haryar anbaton ni'imominSa ga halittu. Allah Madaukakin Sarki ya ce : (ya ku mutane ku tuna ni'imar Allah a kan ku, shin kuna da wani Mahalicci koma bayan Allah da zai azurta kudaga sama da kasa).
Allah mai tsarki da daukaka yace  (ku tuna ni'imar Allah a kan ku a yayin da kun kasance makiya sai ya hada zukatarku sai kuka zma 'yan uwan juna da ni'imar Allah bayan kun kasance kuna gaban rami na wuta sai ya tseratar da ku daga gare ta). Da sauran ayoyi da
Zikiri abu ne mai sauki a harshe mai nauyi a mizani ba a samun fa'idodi da shi kuma zukata basu tsarkaka da shi ayyuka su gyaru da rayuwa face akwai kaunar Allah da kaunar ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,
Mafi falalan zikiri shine Karatun Alkur'ani, don shine ya kunshi dukkan yabo ga Ubangijin talikai, ya kuma ambaci ni'ima da da bayanin sharia daki-daki ya kwadaitar bisa dukkan alheri.ya yi gargadi bisa dukkan sharri.
Ya ku musulmai wannan shi ne ambato cikin alherinSa da albarkansa da amfaninsa da haskensa.
Amma game da ladansa yana da abin da ido bai gani ba zuciyar mutum bata taba hararo wa ba,na daga cikin ladan zikiri akwai abin da ya zo daga Abu Huraira  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce: (Duk wanda ya ce :"Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya mulki da yabo na shi ne yana da iko ga dukkan komai" a farkon wuninsa, zai kasance a gare shi daidai da 'yanta wuyaye goma kuma zaa rubuta mishi lada dari a goge mishi alhaki dari, zai zame kariya ne a gare shi daga shaidan a wannan wunin nasa, har ya yi yammaci kuma ba wanda zi zo da irin wannan abin da ya zo da shi face mutumin da ya yi  aiki sama da wannan.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
An karbo daga Umma Hani Allah ya kara yarda a gare ta ta ce , na ce ya Manzon Allah: Umarce ni da wani aiki da zan yi ina zaune sai yace : ki tasbihi ga Allah sau dari domin yana daidai da 'yanta wuyaye dari ga 'ya'yan isma'il, ka gode wa Allah guda dari domin yana daidai da dawakai dari da sirjinsu da linzamin su suna dauke da kaya a tafarkin Allah, ki yi kabbarori dari domin yana daidai da rakumi dari da aka sa musu alama a wuyansu karbabbu,ki yi halala dari zai cika tsakanin sama da kasa,) Hadisi ne hasan, Ahmad ne ya rawaito da Nasa'I da Hakim.
An karbo daga Nu'uman dan Bashir Allah ya kara yarda a gare shi yace Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Na daga cikin abin da ku ke ambatawa na girman Allah Akwai: subhanallahi walhamdu lillahi wa la'ilaha illalahu ana furta su a saman al'arshi da sauti kamar kukan zuma, ana anbata su da masu yin su, hadisi ne ingantacce ibnu maja ne ya rawaito da Hakim.
Daga Mu'azu Allah yarda da shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :"yan aljanna basu da na sani face ga sa'a da ta wuce su basu ambaci Allah ba a cikinta,) Hadisi ne sahihi Dabarani ne ya rawaito. Da na sani da suke yi sakamakon abin da suka gani ne na girman lada na zikiri, Na daga cikin lada na zikiri yana kiyaye ma'abocin shi daga shaidanu,
An karbo daga Haris dan Haris Al'as'ari Allah ya kara yarda a gare shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace :Allah ya umarci yahya dan zakariyya da ya umarci banu Isra'ila da wasu kalmomi biyar daga ciki akwai ambaton Allah, domin misalin haka kamar misalin mutum ne, makiyi ya fito a bayan shi yana yakan shi har yazo wani katang da zai kare shi sai tare kansa daga gare shi, haka nan ne bawa ba ya iya kare kansa daga shaidan sai da mbaton Allah) Hadisi ne ingantacce.Tairmizi ne ya rawaito da Ibnu hibbanda Hakim.
Mafi girman lada na zikiri shine rabauta da Aljanna da tsira daga wuta kuma yardar Allah ya fi girma. Na daga cikin falalan zikiri Allah zai kare ma'abocin shi daga damuwoyi da tsanani da abubuwa masu halakarwa, Allah Madaukakin sarki ya ce: (kuma ba don ya kasance  cikin masu tasbihi ba da ya zauna a cikinsa har zuwa ranar da zaa tada su,)
  Na daga cikin ladansa Allah tsarki ya tabbata a gare shi zai daga anbaton ma'abocinzikiri a duniya da lahira Allah Madaukakin sarki ya ce: (ku ambace ni zan anbace ku ku gode min kada ku kafurce min)
Na daga cikin ladansa ya na kara karfin ruhi da gangan jiki, yana taimakawa wurin ibada yana kangewa daga abin da aka haramta, kuma yana saukake arziki da shi, An karbo dagaAbdullahi danAmrAllah ya kara yarda a gare shi  ya ce nuhu ya ce ga dan sa kuma ina ma wasiya da cewa tsarki ya tabbata ga Allah domin ita ce salati halittu da tasbihinsu da ita ake azurta halittu)Hadisi ne ingantacce nasa'I ne ya rawaito da Hakim  
Na daga cikin ladan zikiri akwai barranta daga munafunci, kuma shine musiba mafi girma a addini, manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Manzon Allah ya kasance yana zaben kalmomi dunkulallu a wurin adu'o'i da zikiri, na daga cikin dunkulallun aduo'i akwai abin da Annabi ya koyar da Juwaira diyar Haris Allah ya kara yarda a gare ta, Tsarki ya tabbata ga Allah da godiyarsa adadin halittunSa da yardar kansa da nauyin Al'arshinSa da tawadan kalmominSa,tsarki ya tabbata a gare shi daidai adadin halittunSa,tsarki ya tabbata a gare shi gwargwadon yardarsa tsarki ya tabbata ga Allah daidai nauyin Al'arshinSa. Tsarki ya tabbata ga Allah kwatankwacin tawadan kalmominSa. Muslim ne ya rawaito.
An karbo daga Abu Umama Allah ya kara yarda a gare shi yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Ashe ba zan koyar da kai fiye da zikirinka da ka ke yi dare zuwa wuni  da wuni zuwa dare ba, Tsarki ya tabbata ga Allah iya adadin abin da ya halitta, tsarki ya tabbata a gare shi cikin abin da ya halita, tsarki ya tabbata adadin dukkan komi, tsarki ya tabbata a gare shi cikin dukkan komai  tsarki ya tabbata a gare shi  adadin abin da littafin sa  ya kididdige , tsarki ya tabbata gare shi cikin abin da littafin shi  ya kididdige  godiya ya tabbata ga Allah adadin abinda ya halitta , godiya ya tabbata ga Allah cikin abin da ya halitta godiya ya tabbata ga Allah adadin dukkan komai ,  godiya ya tabbata ga Allah cikin dukkan komai , godiya ya tabbata ga Allah  adadin abin da ya  iyakance , godiya ya tabbat ga Allah cikin abinda  littafin sa ya kididdige  Hadisi ne Hassan    Bazzar ne ya rawaito shi da Dabarani .

Allah madaukakin sarki ya ce :- (Da masu ambaton Allah da yawa maza da masu ambaton Allah da yawa mata Allah ya tanada musu gafara da kuma  lada mai girma)  .
Allah ya sanya mini albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma  .
HUADUBA NA BIYU:
 Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga  Allah  Ubangijin talikai majibincin salihai  a mishi biyayya ya gode  asaba mi shi ya gafarta  ina godewa Ubangijina  bisa ga ni'imomi  wanda wanin sa ba zai iya kididdige su ba  wanda muka san su da wanda ba mu san su ba  na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah    shi kadai yake ba shi d aabokin tarayya mai yawan azurtawa ma 'aboci karfi  kuma na shaida Annabin mu kum shugaban mu Annabi muhammad bawan sa ne kuma Manzon sa ne,  amintacce Ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga  bawan ka   kuma Manzon ka Muhammad da iyalan shi da sahabban shi har zuwa ranar sakayya .

 BAYAN HAKA:
Ku  ji tsaoron Allah  da aikata ayyuka na gari da  uyin nesa daga abubuwan da aka haramta .

 YA KU BAYIN ALLAH:-

Ku yi gudu zuwa ga Allah daga gafala  da juya baya  da rudi irin na dogon buri  domin ku dinnan kuna da lokaci da aka yanka mu ku ,  wanda ke kusanto da duk wani abu na nesa yake kodar da duk wani sabon abu ,  hakika Allah ya umarce ku da koyi da Manzo  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a fadin sa madaukaki :- (Hakika kuna da abin koyi mai kyau ga Manzon Allah ga duk wanda  ke fatan Allah da ranar lahira  ya kuma ambaci Allah da yawa  ).

An karbo daga Aisha Allah ya  kara mata yarda ta ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana ambaton Allah a duk  halin  da  ya ke . Muslim ne ya rawaito)
Zaid  Dan Aslam ya ce '' Musa alaihissalam ya ce:- '' Ya Ubangiji ka mini ni'ima mai yawa  to ka nusar da ni zuwa ga abin da zan gode maka mai yawa  sai ya ce ka ambace ni da yawa  ,  to,  idan ka ambace ni da yawa to hakika ka gode mi ni ,  idan kuma ka manta ni to,  hakika ka butulce mi ni  Baihaki ne ya rawaito a cikin Ashhu'ab .


   Magabata na kwarai Allah ya yarda da su sun kasance  suna dimantan ambaton Allah tabaraka wata'ala sabo da cikar kaunar su ga shi  .
(Abu Huraira ya kasance yana da wani zare a cikin shi akwai kulli dubu  ba ya bacci har sai ya yi tasbihi da shi , Abu Nu'aim ne ya rawaito a cikin Alhilya   )     .

Galibin maganan Ibn Sirin shi ne subhanallahil azim (tsarki ya tabbata ga Allah mai girma ), Khalid Dan Ma'adan ya kasance yana tasbihi ko wani rana dubu araba'in na tasbihi banda abin da ya ke karantawa na Alkur'ani   Abu Nu'aim ne ya fito da shi a cikin Alhilya .

Musulmi a wannan zamanin  ya fi tsananin bukatan  zuwa ga zikiri  sakamakon abin da ya yawaita na fitintinu   da kuma abin da ya ke zo ma zukata na gafala ,   da kuma  abin da ya sami  basira na  daga  sha'awe-sha'awe  da shubuhohi da bin soye-soyen rayuka   da kuma abin da ya yawaita  na rudi  da kawar duniya da adon ta,   ya dace  musulmi ya rika daga littatafan azkar abin da zai bude mishi ido   kuma ya  nemi fahimtar sa ya yi aiki da shi ,  na daga cikin mafi amfanin littatafai na ambato ko zikiri akwai TUHFATUZZAKIRINA   da wanin shi,

  
YA KU BAYIN ALLAH:-

Lallai Allah da Mala'ikun sa suna salati  ga Annabi
(Ya ku wadan da suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce …………………………) zuwa karshen adu'a.

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق