الاثنين، 30 يوليو 2018

'YAN UWANTAKA A MUSULUNCI


HUDUBAR  JUMA'A NA MASALLACIN ANNABI NA  SHAIK ALIYU AL-HUZAIFI  14\11\1439
HUDUBAR FARKO
Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mabuwayi mai hikima , mai rahama mai jin kai ina kyautata yabo ga  Ubangijina  ina kuma gode masa bisa  ni'imomin sa wadanda muka sani da wadan da ba mu sani ba  to shi din nan ahli ne na  a ambace shi ba za a manta shi ba a kuma gode mishi ba za a saba mishi ba ,  shi ne mawadaci mai karamci , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaadai yake bashi da abokin tarayya , madaukaki mai girma  na shaida Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad  bawan sa ne kuma Manzon sa ne  wanda Allah ya fifita shi akan bayin sa ga dukkan dabi'u na karamci , ya Allah ka yi dadin tsira da  aminci bisa ga bawan ka kuma Manzonka   Muhammad da iyalan sa da sahabban sa  masu shiryarwa zuwa ga tafarki mikakke  bayan haka ku ji tsoron Allah  ta hanyar neman kusanci zuwa gare shi da neman yardan shi da barin abubuwan da ya haramta su  ba masu rabauta sai masu tsoron Allah    ba masu hasara sai masu sabon  Allah mabarnata  .
             Ya ku musulmai  :
Mumini  shi  mai karfi ne da imanin sa  sa'annan kuma mai karfi ne da 'yan uwan sa,   Mumini yana karkata ne zuwa ga imanin sa da  Ubangijin sa a lokacin tsanani  da bakin ciki  kuma yana riko da  imanin sa  da Ubangijin sa a lokacin da wasu shubuhohi suka bulla    da kuma sha'awe –sha'awe   kuma yana ganin haske ne da imanin sa a lokacin duhun fitintinu da musibu Allah sai ya kare shi da imanin sa lokacin sauki da lafiya da faraga  domin kar ya fada ya halaka  cikin jin dadin abubuwan da aka haramta .
      Allah yakan raya shi da imanin sa a duniya irin rayuwa mai albarka  mai walwala  abin yarda  mai amfani   kyakkyawa mai kyakkyawan karshe  da imanin sa da Ubangijin sa ne zai riski daraja madaukakiya  bayan mutuwa  Allah madaukakin sarki yake cewa: (  lallai wadan da suka yi imani suka yi aiki na kwarai Ubangijin su zai shirye su   dalilin imanin su  kwaraimai na gudana a karkashin su  a cikin lambuna masu ni'ima  adu'a an su a cikinta shi ne  tsarki ya tabbata a gare ka ya Allah  gaisuwan su kuma a cikinta aminci   , karshen da'awar su shi ne dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai  , ).
                      An karbo daga salman Allah ya kara yarda a gare shi  daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Abin mamaki da al'amarin mumini lallai dukkan al'amarin sa alheri ne  ba wanda yake da wannan face mumini  idan abin jin dadi ya same shi sai ya gode to sai hakan ya zama alheri a gare shi idan kuma cuta ya same shi sai ya yi hakuri sai hakan ya zama alheri a gare shi  ) Muslim ne ya rawaito
              To shi mumini  madaukaki ne  mai walwala ne kuma wanda ya yi dace ne da imanin sa  kamar yanda mumini  yana da karfi ta hanyar 'yan uwan sa   domin 'yan uwantaka na musulunci ya fi karfi akan 'yan uwantaka na jini sabo da haka ne ma    gado ke datsewa tsakanin musulmi da kafiri, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Musulmi baya gadan kafiri haka kafiri baya gadan musulmi) Buhari da Muslim ne suka rawaito   daga hadisin Usama dan Zaid Allah ya kara yarda a gare su , to, 'yan uwantaka na Musulunci ya fi girma  akan alaka  da zumunci  da dunkulewa  Allah madaukakin sarki ya ce : ( muminai maza da muminai mata sashin su waliyyai ne ga sashi    suna umarni  da kyakkyawa kuma suna hani ga mummuna  suna kuma tsaida sallah suna kuma bada zakka kuma suna yiwa Allah da'a da Manzon sa wadan nan Allah zai jikan su , lallai Allah mabuwayi ne mai hikima) . Allah madaukakin sarki ya ce : ( Lallai muminai 'yan uwan juna ne)     Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Musulmi dan uwan musulmi ne ba zai zalunce shi ba ba zai tabar da shi ba) .  muslim ne ya rawaito shi
                To 'yan uwantaka na musulunci yana kasancewa ta hanyar taimakekeniya  a addini da karfin hadin kai  Allah madaukakin sarki ya ce  ga Annabin shi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : (  Shi ne wanda ya karfafe ka da taimakon shi  da kuma muminai ya kuma hada zukatan su  da ka ciyar da duk abin da ke doron kasa gaba daya da ba ka iya hada zukatan su ba sai dai Allah shi ya hada zukatan su, lallai shi din nan mabuwayi ne  mai hikima ) kuma Allah madaukakin sarki ya ce : ( Ya ku wadanda kuka yi imani  ku ji tsoron Allah cancancin tsoron shi  kada ku mutu face kuna musulmai , ku yi riko da igiyan Allah  baki daya  kar ku rarraba  ku ambaci ni'imar Ubangiji a gare ku zamanin da kuka kasance makiya juna   sai kuka zama 'yan uwa sabo da ni'imar Allah  ,   a da kun kasance a gabar rami  na wuta   ya tsamo ku daga gare ta  )
          'Yan uwantakan addini yana kasancewa ne   ta hanyar taimakekeniya  wurin tabbatar da maslahohi  da tunkude barna  da bada kariya  ga al'umma  daga masu ketare iyaka  Allah madaukaakin sarki ya ce: ( ku yi taimakekeniya akan da'a da kuma tsoron Allah , kada ku yi taimakekeniya akan laifi da kiyayya ) Allah madaukakin sarki ya ce : ( Ya kasance a cikin ku akwai wata al'uma da tana kira zuwa  ga alheri, kuma suna  umarni da kyakkyawa  , kuma  suna hani da  mummuna  wadannan sune masu rabauta ).
     'Yan uwantaka na musulunci  yana kasancewa ta hanyar jin kai da tausayawa juna  da kuma  taimakekeniya  , da kuma  hadin guiwa  wurin samar da abin da al'uma ke bukata  da kyakkyawan tsarin rayuwa  Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce : ( Misalin muminai cikin kaunar su da son junan su da tausayawa junan su kamar  gangan jiki ne guda     idan wani gaba ya tabu da rashin lafiya  sai sauran jikin ya amsa  da zugi da rashin bacci ) Buhari ne ya rawaito da muslim daga Hadisin Abu Musa Al-ash'ari  
       Na daga cikin abin da ke kawo dadin rayuwa akwai wanzuwar kauna a tsakanin  musulmai   Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (   Na rantse da wanda raina yake hanun shi  ba za ku taba shiga aljanna ba har sai kun yi imani  , ba za ku yi imani ba kuma har sai kun so junan ku  , ase ba zan nusar da ku  bisa ga aabin da idan kun aikata shi za ku kaunaci junan ku ba  to ku yada  sallama a tsakanin ku .,
    YA JAMA'AR MUSULMI:
     Rayuwa fa ba za ta daidaita ba har sai kun tashi da hakkoki na 'yan uwantaka na musulunci   ,  to abubuwan da suke na wajibi akwai wanda suke  na Ubangiji madaukakin sarki , wannan shi ne wajibi mafi girma  da kadaita Allah da bauta mishi ,  daga ciki kuma akwai abin da yake hakki ne na  halittu  ,   kuma hakkokin musulmai iri uku ne :-
            Mafi girman su shi ne fifita wani akan kai (isar) wato gabatar da bukatar musulmi   da hakkin shi akan hakkin kai  wannan ita ce daraja da muhajirun suka rabauta da ita da kuma ansar Allah ya kara yarda a gare su  Allah madaukakin sarki ya ce: (Wadanda suke zaune a madina suka kudure imani tun gabanin su  suna son wanda yayi hijira gare su ya yi kaura  basa hasada da abinda ya basu   suna fifitawa 'yan uwan su a kan kansu  koda akwai wani bukata a gare su izuwa  abinda suka fifita   wani da shi , wanda aka kiyashe shi kwadayin kansa   wadancannin ka   su ne hakikanin marabauta ).
        Wannan na maimaituwa a ko wani zamani   da ko wani wuri  idan imani ya cika  tarihi ya kiyaye mana   wasu sifofi na fifita wani akan kai masu yawa a lokuta daban-daban  
 Daraja  na tsakatsakiya kuma daga cikin darajoji na 'yan uwantaka  shi ne mutum musulmi ya    so wa dan uwansa abin da ya so wa kan sa an karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (     Imanin dayan ku ba zai cika  ba har sai ya so wa dan uwan shi abin da yake so wa kanshi) Buhari da Muslim ne suka rawaito
         Mafi daraja na kasa kuma  wanda musulmi zai tashi da shi game da hakkin dan uwan shi musulmi shi ne ka kame sharrin ka daga gare shi ,  ba za ka zalunce shi ba a jini ne ko dukiya ko mutunci  , ba za ka zare harshen ka ba akan shi   ko hanun ka  ko kuma ka tawaye mishi wani hakkin  da yake na shi ne  ,  ko ka hana shi hakkin sa  tare da yin kokari  yin abin da Allah zai datar da kai zuwa gare shi na alheri, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da Abu zarri (kuma ka kame sharrinka daga mutane, domin hakan sadaka ne gare ka a kan ka,)
Ya ku musulmai!
Lallai abin da ya fi cutar da 'yan uwantaka na musulunci shine bidi'a mai batarwa, don dan bidi'a yana kiyayya ga duk wanda  bai aminta da bidi'arsa, ba abin da zai hada zukatar musulmai sai akidar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da sahabbansa da wadanda suka bi su da kyautatawa , su ne masu son juna don Allah, na karshen su na son na farkonsu, Allah Madaukakin sarki ya ce: ( Wadan da suka zo bayansu suna cewa  :Ya Ubangijinmu ka gafarta mana  da 'yan uwan mu da suka gabace mu da imani kar ka sanya kulli cikin zuciyarmu game da wadan da suka yi imani ya Ubangijinmu kai mai tausayi ne mai jinkai)
Na daga cikin abin da ke cutar da 'yan uwantaka ta musulunci akwai fifita duniya akan lahira, da mutuwa don ita. Har ya zama  mafi yawan mutane kan haka suke 'yan uwantakarsu, da gina kiyayya kan kawar duniya da jin dadinta.
Na daga cikin abin da ke cutar da 'yan uwantaka  zalunci da yaduwar wannan zalunci ta hanyar hana mutane hakkokinsu, ko kwace hakki, don rayin dan adam na tsanan duk wanda ya zalunce ta, kuma tana neman daukar fansa, daga gare shi,
Na daga cikin abin da ke cutar da 'yan uwantaka  na musulunci akwai hasada, domin yana janyo gaba da kiyayya.
Na daga cikin abin da ke haifar da illa ga 'yan uwantaka na musulunci mutum ya rika ganin kansa  a matsayin kamili  ya ke  ganin waninsa  da reni da tawaya. To ga ku jama'ar musulmi jikunanku sun hadu a farillu  na musulunci, a hajji da juma'a da  sallar jam'i da sallolin idi, to ku hada zukatanku a kan akidar magabata na kwarai, da kur'ani da sunna , ku tuna cew za ku koma ga Allah Madaukaki, ku bar duk wani abu da ke kange ku daga gaskiya, ku tsaya gaba ga Ubangijinku huntaye tsirara, ba kaciya, ba wani abu tare da ku sai kyawawan ayyukanku da munana, to ku zo wa kyawawan ayyuka ku kiyayi munanan ayyuka,Allah Madaukakin sarki ya ce : (ku yi gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijinku  da Aljanna fadinta ya kai sammai da kasa an tanade ta don masu tsoron Allah. Wadan da suke ciyarwa a lokacin sauki da tsanani, da masu hadiye fushi da masu yafiya ga mutane, Allah na son masu kyautatawa,)
Allah sanya mini albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma,
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah a kowane hali, muna neman tsarin shi daga hali irin na 'yan wuta, wadan da ayyukansu ya jefa su cikin wulakanci da azaba, ina gode wa Ubangiji na bisa ga kyauta mai girma,Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya Mai girma Maabocin daukaka, Na shaida Annabin mu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne.
Allah ka yi dadin tsira a gare shi da sahabbansa da iyalai, bayan haka ku ji tsoron Allah ku mishi biyayya, ku kiyayi fushinsa  da bushewar ido cikin saba masa, ya ku bayin Allah hakika hujja fa ta tsayu a kanku, hanya ta bayyana a gare ku, kuma duk wasu uzurori sun yanke, to ku fiskanci aiki kada buri ya rude ku, Allah Madaukakin sarki na cewa : (Ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijin ku ku kiyayi wata rana da Mahaifi ba zai fanshi dansa ba ko shi  da ya fanshi mahaifinsa  da wani abu ba, Alkawarin Allah gaskiya ne kada rayuwar duniya ta rude ku, kada kuma wani abin rudi ya rude ku daga Allah)
To ku tuna mutuwa da abin da ke bi mata na daga azaba  da ba mai kubutar da mutum daga shi sai ayyuka na kwarai, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ku yawaita ambato mai datse jin dadi, wato mutuwa ,
Ya ku bayin Allah lale Allah da Mala'ikunsa su na  salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce,
Har karshen Adua.    
  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق