الاثنين، 9 يوليو 2018

Nesatan majalisan mabarnata


Hudubar Masllacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  na shaikh Salahu Bin Muhammad Albudair 22/10/1439h
YA KU MUSULMAI:
Nisantar zama da masu sabo  da guje musu, da barin farfajiyan su  da kauracewa wuraren su  da yanke abokantaka da su da gujewa tafiya tare da su  abu ne da ke nuna hangen nesan mutum  da kuma basirar sa .
                   Kubuta daga Laila  da makwabciyarta *** shi ne kar ka bi  ta  kwari daga cikin kauyukanta
 Zukata na da rauni shubuhohi na yawan fizga, fitintinu na tasowa , masu  basira   suna nisantar majalisan wadanda suke da cutar zuci, masu bata imani  kuma suna kiyayan  abokantaka da   fitinannu fandararru daga sunna  masu kaucewa duk wasu harka na musulunci da kama kai da dabi'u irin na musulmai .
 Idan ka kasance  kai lafiyan ka kalau   amma ka yi abokantaka da maara lafiya  ka kasance aboki gare shi , to kai ma fa ka zama mara lafiya .
Duk wanda ya zauna a majalisan wasu mutane wadda a cikin shi akwai sabo ko bidi'a , to ya wajaba a gare shi ya musu inkari da hikima tare da daddadan kalma  da wa'azi mai kyau da kuma dalili wanda ke bayyana gaskiya , mai gusar da shubuha,   idan har yana da ikon ya yi inkarin kuma bai yi inkarin ba  to ya kasance  zai yi tarayya da su a alhaki,  idan ya gagara kuma yin inkari a gare su  to fa ya wajaba a gare shi da ya bar majalisar tasu , sabo da zaman tare da cakudaidainiya na haifar da sabo da  kuma  koyi da abun , da kuma kyaliya  ga munkari  da kuma kauna a zuciya , kuma ta iya yiwuwa ma  fitinar ta fado a kan shi , Amru dan Kais ya ce (  Kar ka zauna da ma'abota bata sai zuciyarka ta bata ) Allah madaukakin sarki ya ce : (Alhali hakika ya saukar a gare ku cikin alkur'ani cewa idan kun ji ayoyin Allah ana kafirta da ita ana isgili da ita wato kur'ani , to, kada ku zauna tare da kafiran nan sai sun kutsa cikin wani zancen ba wannan ba , hakika ku yayinnan in kuka zauna tare da su kamar su kuke a cikin zunubi ) Imamu Addabari ya ce  : (A cikin wannan aya akwai nuni na bayyane bisa ga hanin zama da ma'abota  bata , na ko wani iri a cikin su  'yan badi'a ne ko fasikai  yayin kutsawan su cikin batar su shaikhul Islam Ibn Taimiyya Allah ya yarda da shi ya ce :  (Baya halarta ga wani da  ya halacci majalisan da ake barna bisa son zabin shi ba tare da wani lalura ba  kamar yanda ya zo a hadisi  Manzon Allah tsira da  amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (duk wanda ya kasance ya yi imani da Allah da ranar lahira to kada ya zauna a teburin da ake shan giya a kanta )  An daukaka kara zuwa ga Umar dan Abdul'aziz game da wasu mutane da suke shan giya  sai ya bada umarni da a musu bulala sai a kace da shi lallai a cikin su akwai mai azumi, sai ya ce  ku fara da shi , ase ba ku ji fadin Allah madaukakin sarki (Alhali hakika ya saukar a gare ku cikin alkur'ani cewa idan kun ji ayoyin Allah ana kafirta da ita ana isgili da ita wato kur'ani , to, kada ku zauna tare da kafiran nan sai sun kutsa cikin wani zancen ba wannan ba , hakika ku yayinnan in kuka zauna tare da su kamar su kuke a cikin zunubi)   Umar dan Abdul-aziz Allah ya yarda da shi  ya bayyana  cewa  ( masu halartan wurin sabo kamar masu aikata shi ne)
           Sabo da haka ne malamai suke cewa  idan aka gayyace shi zuwa ga walima wanda cikin shi akwai barna kamar shan giya da goge baya halatta da ya je sabo da Allah madaukakin sarki ya umurce mu da mu hana barna gwargwadon iyawa, duk wanda ya je bisa zabin shi to hakika ya    sabawa Allah da Manzon sa sabo da barin abin da aka umarce shi da shi  na daga kin inkarin sa da hani game da shi .  to idan ya kasance  hakan  , to  ina ga wanda zai halarci majalisan shan giya bisa  zabin sa ba tare da wata lalura ba  kuma bai hana barnan ba kamar yanda Allah ya umarce shi , to fa ya zama abokin tarayyan fasikai a fasikancin su ,  to kenan ya zama kamar su .
     YA KU MUSULMAI :
Kar ku kara  yawan  'yan bidi'a da barna da sabo  daidai da rana guda  kar ku kasance cikin tarun ma'abota fitina da barna .
       An karbo daga Abdullahi Dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su  cewa wasu mutane cikin musulmai  sun kasance tare da mushrikai  suna  kara aukin mushrikai  a zamanin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , idan anyi harbi sai kifiya ya samu daya daga cikin su ya kashe shi  ko kuma ya soke shi  sai Allah ya saukar da fadin sa  ( Lallai wadan da mala'iku ke kashe su  mutane ne da suka zalunci kawunan su ) buhari ne ya fitar da shi .
      Duk wanda ya halarci majalisai na barna  domin debe kewa da su da farin ciki da aikin su  ko kuma ya yarda da aikin  ko ya yi kira zuwa gare su  ko ya karfafe su  ,  ko kuma ya karfafi  shafi  mai shubuha a yanar gizo  da kuma shafuka  wadda suke na barna  da fasadi  da shafuka masu adawa da  addinin mu   da akidar mu  da  dabi'unmu  da  garinmu  ya kuma sanya musu alamar yarda  da karfafa to hakika ya kara aukin su ne  ya zama kuma cikin su  .
  HUDUBA TA BIYU
YA KU MUSULMAI:
Kar ku bayyana sabo kar ku halatta abin da Allah     ya haramta kar ku rudu da fatawar masu sakaci da sassautawa   da kuma  tsaka-tsakiyan masu da'awan fikihu , masu bada fatawa ba tare da yakini ba ko kyautatawa ba  suna karkata zuwa ga daya bangare na bata da sunan sauki  da tsaka-tsaki da daidaito .
      Duk wanda ya bayyana sabo   ya aikata shi a fili to hakika ya fusata Ubangijin shi   kuma ya keta alfarmar shi  kuma ya raina ukubar sa  ya cutar da bayin Allah Muminai to ku ji tsoron Allah ya ma'abota musulunci kar ku rudu da ni'imomi da yalwa    kada ku yi amfani da kyauta da aka baku gurin aikata barna,  kada ku bayyana sabo alhali Allah ya muku ni'ima da rayuwa mai yalwa da abin sha mai kosarwa,  ga mutane a kewayen ku suna halin bakar yunwa na kashe su  da kuma mutuwa mai muni .

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق