HUDUBAR MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH
HUSAINI ALI SHAIK 7\11\1439
HUDUBAR FARKO
A irin wannan zamani wanda kalubalen sa sun yi yawa , wanda hadarin sa
ya girmama ga dan adam , hadari irin na rayuka
da tsoracewa zuriyawa , da wahalhalu irin na neman abin masarufi, zuwa ga abubuwan da ba su da iyaka na ban
tsoro, wanda ke wucewa ga dan adam a wannan zamani cikin abinda ba zai kidanyu ba ko ya boyu ba
anan ne bukata zata girmama
lalura za ta tsananta zuwa ga sanin
abinda zai kai bayi zuwa ga himma
madaukakiya da kuma karfin azima
domin su riski maslahohi da ake fata
da abubuwan masu amfani da ake
bukata .
Lallai dan adam a
duk lokacin da yake da karfin basira da cikan yakini, da alkawarin Allah mai
tsarki to, a wannan lokacin ba zai juya kai zuwa ga abin da zai ba shi
tsoro ba muddim ya riki sababi ya kuma
dogara da mai kawo sababi sai dai ma ya
rabauta da manufofin sa kuma ya samu
nasara wurin cimma bukatun sa .
Lallai dan adam a duk
lokacin da ya maida al'amarin shi ga Allah
ya yanke zuciyar sa daga
ta'allakuwa ga halittu ya tashi da abin da Allah ya shar'anta a gare shi ,
na daga sabuba na zahiri da kuma
na shari'a zai zame ma'abocin himma
madaukakiya wanda hakika ya sabarwa kansa bi ta kan wahalhalu har ma abubuwan da suke
na tsanani sun saukaka a gare shi muddin
zuciyar sa ba komai a cikinta sai dogaro
ga Allah da kuma jingina zuwa gare shi, sabo da yana da yakini
da tabbaci na alkawarin Allah Allah Madaukakin sarki ya ce : ( Duk wanda ya
ji tsoron Allah to, Allah zai sanya masa
yayewa ya azurta shi ta inda bai zato, Duk wanda ya dogara ga Allah to Allah ne
mai isar mishi )
Wani daga cikin magabata yace : ( Da ace mutum zai dogara ga Allah da
gaskiyar niyya da sarakuna sun bukace
shi da na kasa da su, to ina ga wanda majibincinsa Mawadaci ne abin godiya ne
ta yaya zai bukaci wani?
Lalle duk wanda ya dogara ga Allah ya maida mishi lamuransa gabadaya
gare shi Mai tsarki yana kallon duniya
da lahira duka mulki ne na Allah, halittu dukkaninsu bayi ne na Allah, da
arziki da dalilanta duk a hanun Allah su ke, kuma yana ganin hukuncin Allah abu ne mai
zartuwa a doron kasa baki daya, sabo da haka ne ma Allah ya umarci bayinsa da
su dogara gare shi sai ya ce : (ka
dogara ga Rayayye da bai mutuwa) kuma ya ce : (Ga Allah kadai zaku dogara in
kun kasance muminai)
To duk wanda bai kula da umarnin Ubangijinshi ba zai fada cikin musibu
da tsanani kuma ba zai cin ma burinsa ba
ba zai kubuta daga abin da ya ke tsoro ba.
Tawakkali :Lafazi ne mai girman ma'ana mai da madaukakiyar manufa, Duk wanda ya dogara ga
Allah shi ne ya rike shi a matsayin wakil wanda ke tashi da al'amuransa ya lamunce mishi
gyaruwansa. Wanda ya isan masa a komai bai tare da wani jin nauyi ko wahala ba.
Mai dogaro ga Allah shi ne wanda yake da aminci da yakini game da
ubangijinsa ta yadda ba wani rabon shi
da zai kwace mi shi. Lallai
hukuncin shi baya canzawa kuma baya sauyawa
Allah madaukakin sarki ya ce : ( Arzikin ku yana cikin sama da abin da aka alkawarta muku , Na rantse da
Ubangijin sama da kasa lallai shi dinnan
gaskiya ne tamkar yanda kuke furuci ). Yana daga cikin ma'anonin wannan aya Allah madaukakin sarki bai tsaya ga lamunce azurta halittu ba kawai
sai da ya kara da rantsuwa akan haka , Hassan Allah ya mishi rahama ya ce :
(Allah ya tsinewa wasu mutane , Ubangijin su ya rantse musu amma ba su gaskata shi ba) an rawaito cewa mala'iku sun ce banu adama sun halaka sun fusata Ubangiji har sai da ya yi rantsuwa bisa ga azurta su Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Da kun dogara da Allah canancin dogaro da ya azurta ku kamar yanda ya ke azurta tsuntsu suna wayan gari a yunwace su yi yammaci a kwashe ) Ahmad ne da tirmizi da Ibn Maja suka rawaito shi kuma isnadin shi ingancecce ne a wurin malamai masu tantancewa.
(Allah ya tsinewa wasu mutane , Ubangijin su ya rantse musu amma ba su gaskata shi ba) an rawaito cewa mala'iku sun ce banu adama sun halaka sun fusata Ubangiji har sai da ya yi rantsuwa bisa ga azurta su Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Da kun dogara da Allah canancin dogaro da ya azurta ku kamar yanda ya ke azurta tsuntsu suna wayan gari a yunwace su yi yammaci a kwashe ) Ahmad ne da tirmizi da Ibn Maja suka rawaito shi kuma isnadin shi ingancecce ne a wurin malamai masu tantancewa.
Mai dogaro ga Allah Mabuwayi
da daukaka mai gaskiya ne a wurin dogaron sa ga Allah cikin saukake al'amuransa da kuma janyo misjhi amfani , da
tunkude cutarwa mai aminta ne da alkawarin
Allah kuma mai sakankancewa ne kan cewa
tare da mika al'amuran shi ga Allah zai cimma manufofin sa , kuma ya
kubuta daga abin da yake tsoro .
Mai dogaro ga Allah yana mika al'amarin shi ne ga Allah sabo
da yarda da yake da shi ga Allah da
kyautata zato a gare shi , shi dinnan zai yanke alakar sa da wanin Allah zai
yanke dubi zuwa ga sabuba bayan ya kimtsa
musu ya tashi da su , yana kuma barranta daga dabarar sa ko kokarin sa face ga Allah madaukaki mai girma sabo da kebanta da ya yi da halittawa da
gudanarwa da cuta da amfanarwa da kyauta
da hanawa , ya san kuma lallai abinda Allah ya so shi zai wakana abin da bai so
ba bazai faru ba .
Mai dogaro ga Allah yana
dogaro ne a dukkan al'amura da kuma sabuba
shi kuma sabuba kamar wasu tsani ne
wanda ba'a dogaro akan su, shi bawa zai kula da sabuba na zahiri sai dai ba zai
dogara akan su ba da zuciyar sa sai dai ma
ya dogara da mahalicci mai gudanarwa
kuma ya mika wuya a cikin hukuncin Ubangiji da kudurarsa da abin da ya so.
BAYIN ALLAH:-
Duk wanda ya tabbatar da tsoron
Allah kuma gaskata dogaron sa ga majibinci
to hakika ya samu babban abin
bukata .
Duk wanda ya mika al'amuran sa
ga Ubangijin sa ya dogara ga mahaliccin sa
yana mai kadaita shi ya koma gare
shi mai yawan kai kukan shi gare shi yana mai tuba
yana kuma bin dokokin shi yana
mishi da'a to, Allah zai sanya mishi
yayewa daga ko wani bakin ciki , kuma ya
sanya mishi mafita daga ko wani kunci
kuma ya azurta shi ta inda bai zata ba
kuma ya riski alheri mai yawa
kuma ya kare shi daga dukkan wani cuta da sharri karshen shi kuma ya zama rabauta da nasara da taimako
mai karfi Allah madaukakin sarki ya ce game da bawa na kwarai : (Kuma
ina mika al'amari na zuwa ga Allah lalle Allah masani ne ga bayinsa, sai Allah
ya kare shi daga miyagun abin da suka yi nufi sai mummunar azaba ta sauko ga
Fir'auna da mutanensa)
Allah madaukakin sarki ya ce : ( wadan da mutane suka ce da su wato hakika mutane sun tara (runduna) don ku ku ji tsoron su sai ta kara
musu ban gaskiya sai suka ce Allah ne
mai isar mana madalla da abin dogaro sai
suka koma da sakamako daga Allah da kari suka koma sumul tare da riba , wani abu mummuna bai same su ba suka bi
yardar Allah Allah mai falala ne mai
girma ).
An karbo daga dan Abbas Allah
ya kara yarda a gare shi HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL Annabi Ibrahim ya fade ta a lokacin da aka jefa shi a wuta kuma Annabi Muhammad ya fade ta lokacin da
suka ce ( Hakika mutane sun tara
runduna don ku ) Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa
(Duk mutumin da idan yazo fita gidan shi yana cewa BISMILLAHI
TAWAKKALTU ALALLAH WALA HAULA WALA
KUWWATA ILLAH BILLAH ) sai a ce da
shi an shiryar da kai , kuma an isar maka an baka kariya sai shedan kuma yayi nesa da shi Abu Dauda ne ya rawaito shi da Tirmizi da Nasa'i da isnadi ingantacce.
HUDUBA TA BIYU
YA KAI MUSULMI : -
Ka maida al'amarin ka zuwa ga Allah
ka yi dogaro na gaskiya gare shi
ka yi aiki da abin da ya shar'anta na sabuba ka aminta da cewa lallai wanda yake gudanar da al'amura daga
sama zuwa kasa masani ne
da abin da ya boyu da abin da ke
zuciya wanda ya iyakance dukkan al'amura
ta kowace fuska mai iko ne da cikakkiyar kudura ma'abocin
cikan abin da ya so yana kewaye
da kai da ludufi irin na ilimin sa da
kyautata gudanarwa , wanda ba wanda zai iya sani cikin halittu ko kuma wani
haziki ya fahimce shi , ka shagaltu da sha'anin ka ka kebe don bautawa
Ubangijinka ka samu yakini kan cewa duk
wanda ya dogara gare shi to fa ya isar masa, kuma zai kasance amintacce daga
hadura kuma ya samu cikakken natsuwa da
kwanciyar hankali .
Lallai duk wanda bai sani ba *** shin abin
da ake kauna ne alheri ko kuma abin da aka ki
To lallai ya dace ya maida abin da ya gagara a gare shi *** zuwa
ga wanda ya isar mishi
Ku saurara dukkan biyayya na
shi ne wanda game da tausayi *** ya fi
mamma da baba jin kai .
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق