الجمعة، 20 يوليو 2018

DOGARO GA ALLAH A MUSULUNCI


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH  HUSAINI ALI SHAIK  7\11\1439
HUDUBAR FARKO
A irin wannan zamani wanda kalubalen sa sun yi yawa , wanda hadarin sa ya girmama ga dan adam , hadari irin na rayuka  da tsoracewa zuriyawa ,  da  wahalhalu irin na neman abin masarufi,  zuwa ga abubuwan da ba su da iyaka na ban tsoro, wanda ke wucewa ga dan adam a wannan zamani  cikin abinda ba zai kidanyu ba  ko ya boyu ba  anan ne  bukata zata girmama lalura za ta tsananta  zuwa ga sanin abinda zai kai bayi zuwa  ga himma madaukakiya  da kuma  karfin azima  domin su riski maslahohi da ake fata  da  abubuwan masu amfani da ake bukata  .
              Lallai dan adam a duk lokacin da yake da karfin basira da cikan yakini, da alkawarin Allah mai tsarki  to, a wannan lokacin  ba zai juya kai zuwa ga abin da zai ba shi tsoro ba muddim ya  riki sababi ya kuma dogara da mai kawo sababi  sai dai ma ya rabauta da manufofin sa  kuma ya samu nasara wurin cimma bukatun sa .
           Lallai dan adam a duk lokacin da ya maida al'amarin shi ga Allah  ya yanke  zuciyar sa daga ta'allakuwa ga halittu ya tashi da abin da Allah ya shar'anta  a gare shi ,  na daga sabuba na zahiri  da kuma na shari'a  zai zame ma'abocin himma madaukakiya  wanda  hakika ya sabarwa kansa  bi ta kan wahalhalu har ma abubuwan da suke na tsanani sun saukaka a gare shi  muddin zuciyar sa  ba komai a cikinta sai dogaro ga Allah  da kuma  jingina zuwa gare shi, sabo da yana da yakini da tabbaci na alkawarin Allah Allah Madaukakin sarki ya ce : ( Duk wanda ya ji tsoron Allah  to, Allah zai sanya masa yayewa ya azurta shi ta inda bai zato, Duk wanda ya dogara ga Allah to Allah ne mai isar mishi )
Wani daga cikin magabata yace : ( Da ace mutum zai dogara ga Allah da gaskiyar niyya  da sarakuna sun bukace shi da na kasa da su, to ina ga wanda majibincinsa Mawadaci ne abin godiya ne ta yaya zai bukaci wani?
Lalle duk wanda ya dogara ga Allah ya maida mishi lamuransa gabadaya gare shi Mai tsarki  yana kallon duniya da lahira duka mulki ne na Allah, halittu dukkaninsu bayi ne na Allah, da arziki da dalilanta duk a hanun Allah su ke,  kuma yana ganin hukuncin Allah abu ne mai zartuwa a doron kasa baki daya, sabo da haka ne ma Allah ya umarci bayinsa  da  su  dogara gare shi sai ya ce : (ka dogara ga Rayayye da bai mutuwa) kuma ya ce : (Ga Allah kadai zaku dogara in kun kasance muminai)
To duk wanda bai kula da umarnin Ubangijinshi ba zai fada cikin musibu da tsanani  kuma ba zai cin ma burinsa ba ba zai kubuta daga abin da ya ke tsoro ba.
Tawakkali :Lafazi ne mai girman ma'ana mai  da madaukakiyar manufa, Duk wanda ya dogara ga Allah shi ne ya rike shi a matsayin wakil  wanda ke tashi da al'amuransa ya lamunce mishi gyaruwansa. Wanda ya isan masa a komai bai tare da wani jin nauyi ko wahala ba.
Mai dogaro ga Allah shi ne wanda yake da aminci da yakini game da ubangijinsa ta yadda ba wani rabon shi  da zai kwace mi shi.  Lallai hukuncin shi baya canzawa kuma baya sauyawa   Allah madaukakin sarki ya ce : (  Arzikin ku yana cikin sama   da abin da aka alkawarta muku , Na rantse da Ubangijin sama  da kasa lallai shi dinnan gaskiya ne   tamkar yanda kuke furuci ).  Yana daga cikin ma'anonin wannan aya  Allah madaukakin sarki  bai tsaya ga lamunce azurta halittu ba kawai sai da ya kara da rantsuwa akan haka , Hassan Allah ya mishi rahama ya ce :
(Allah ya tsinewa wasu mutane  , Ubangijin su ya rantse musu amma ba su gaskata shi ba)   an rawaito cewa mala'iku sun ce    banu adama sun halaka sun fusata Ubangiji har sai da ya yi rantsuwa  bisa ga  azurta su  Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (  Da kun dogara da Allah canancin dogaro da ya azurta ku kamar yanda ya ke azurta tsuntsu suna wayan gari a yunwace  su yi yammaci a kwashe ) Ahmad ne da tirmizi da Ibn Maja suka rawaito shi  kuma isnadin shi ingancecce ne a wurin malamai masu tantancewa.
          Mai dogaro ga Allah Mabuwayi da daukaka mai gaskiya ne a wurin dogaron sa ga Allah cikin saukake al'amuransa  da kuma  janyo misjhi amfani  ,  da tunkude cutarwa  mai aminta ne da alkawarin Allah  kuma mai sakankancewa ne  kan cewa  tare da mika al'amuran shi ga Allah zai cimma manufofin sa ,  kuma ya  kubuta daga abin da yake tsoro .
     Mai dogaro ga Allah   yana mika al'amarin shi ne ga Allah sabo da  yarda da yake da shi ga Allah da kyautata zato a gare shi , shi dinnan zai yanke alakar sa da wanin Allah zai yanke dubi zuwa ga sabuba bayan ya kimtsa  musu ya tashi da  su ,  yana kuma barranta daga  dabarar sa ko kokarin sa  face ga Allah madaukaki mai girma  sabo da kebanta da ya yi da halittawa da gudanarwa  da cuta da amfanarwa da kyauta da hanawa , ya san kuma lallai abinda Allah ya so shi zai wakana abin da bai so ba bazai faru ba .
    Mai dogaro ga Allah yana dogaro ne a dukkan al'amura   da kuma sabuba  shi kuma sabuba  kamar wasu  tsani ne  wanda ba'a dogaro akan su, shi bawa   zai kula da sabuba na zahiri sai dai ba zai dogara  akan su ba da zuciyar sa  sai dai ma  ya dogara da mahalicci mai gudanarwa  kuma ya  mika wuya  a cikin hukuncin Ubangiji  da kudurarsa da  abin da ya so.
      BAYIN ALLAH:-
  Duk wanda ya tabbatar da tsoron Allah  kuma  gaskata dogaron sa  ga majibinci   to hakika   ya samu babban abin bukata   .
    Duk wanda ya mika al'amuran sa ga Ubangijin sa ya dogara ga mahaliccin sa   yana mai kadaita shi  ya koma gare shi  mai yawan       kai kukan shi gare shi  yana mai tuba  yana kuma  bin dokokin shi   yana mishi da'a  to, Allah zai sanya mishi yayewa daga ko wani  bakin ciki , kuma ya sanya mishi mafita daga ko wani kunci  kuma ya azurta shi ta inda bai zata ba  kuma ya riski alheri mai yawa  kuma ya kare shi daga dukkan wani cuta da sharri  karshen shi kuma ya zama rabauta da nasara  da taimako  mai karfi Allah madaukakin sarki ya ce game da bawa na kwarai : (Kuma ina mika al'amari na zuwa ga Allah lalle Allah masani ne ga bayinsa, sai Allah ya kare shi daga miyagun abin da suka yi nufi sai mummunar azaba ta sauko ga Fir'auna da mutanensa)     
            Allah madaukakin sarki ya ce : (  wadan da mutane suka ce da su wato  hakika mutane sun tara  (runduna) don ku ku ji tsoron su sai ta kara musu ban gaskiya sai suka ce Allah  ne mai isar mana madalla da abin dogaro  sai suka koma da sakamako daga Allah da kari suka koma sumul tare da riba  , wani abu mummuna bai same su ba suka bi yardar Allah  Allah mai falala ne mai girma ).
 An karbo daga dan Abbas Allah ya kara yarda a gare shi   HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL   Annabi Ibrahim ya fade ta  a lokacin da aka jefa shi a wuta  kuma Annabi Muhammad ya fade ta  lokacin da   suka ce (  Hakika mutane sun tara runduna don ku )  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa  (Duk mutumin da idan yazo fita gidan shi yana cewa BISMILLAHI TAWAKKALTU ALALLAH  WALA HAULA WALA KUWWATA ILLAH BILLAH  ) sai a ce da shi  an shiryar da kai  , kuma an isar maka an baka kariya  sai shedan kuma yayi nesa da shi  Abu Dauda ne ya rawaito shi da  Tirmizi da Nasa'i da isnadi ingantacce.
   
HUDUBA TA BIYU
YA KAI MUSULMI : -
Ka maida al'amarin ka zuwa ga Allah  ka yi dogaro na gaskiya gare shi  ka yi aiki da abin da ya shar'anta na sabuba ka aminta da cewa  lallai wanda yake gudanar da al'amura daga sama  zuwa kasa  masani ne  da abin da ya boyu  da abin da ke zuciya  wanda ya iyakance dukkan al'amura  ta kowace fuska  mai iko ne da cikakkiyar kudura  ma'abocin  cikan abin da ya so  yana kewaye da kai da ludufi irin na ilimin sa  da kyautata gudanarwa , wanda ba wanda zai iya sani cikin halittu ko kuma wani haziki ya fahimce shi , ka shagaltu da sha'anin ka ka kebe don bautawa Ubangijinka   ka samu yakini kan cewa duk wanda ya dogara gare shi to fa ya isar masa, kuma zai kasance amintacce daga hadura  kuma ya samu cikakken natsuwa da kwanciyar hankali .
    Lallai duk wanda bai sani ba *** shin abin da  ake kauna ne  alheri ko kuma  abin da aka ki
   To lallai ya dace  ya maida abin da ya gagara a gare shi *** zuwa ga wanda ya isar mishi
  Ku saurara dukkan biyayya na shi ne wanda game da tausayi  *** ya fi mamma da baba jin kai .
  


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق