الخميس، 19 يوليو 2018

kyautata sakayya a musulunci


Hudubar Juma'a na Masallacin Annabi  29-10-1439 AH /12-7-2018 M
Shaikh Abdulbari Bin Awad Assubaiti

Na daga cikin abin da ya ke jigo ne ga musulmi da dabiunsa : mutunta ma'abota mutunci, da sakanya  kyautatawa da mafi kyau, wannan wata dabi'a ce mai girma a musulunci  gun mu'amala, wato sakanya ta kyautatawa a musulunci  ita ce kyautatawa kwatankwacinta. Allah Madaukakin sarki ya ce :( Babu wani sakamako na kyautatawa sai kyautatawa) Arrahman 59
 Shi musulmi bai manta  ma'abotar  falala a kansa, duk wanda ya mishi wani ihsani zai tuna kyautatawarsa, zai kuma gode masa ya kimanta alherin da suka masa, ba zai manta ba a duk rintsi na rayuwa, da matsaltsalun  fitintinunta, da duk wanda wani dankon zumunci da kauna ya hada su, da wata muamala da ta wakana a baya, ko da an samu wani sabani  na wata  rana ko rashin fahimtar juna, Allah Madaukakin sarki ya ce : (kar ku manta falala da ke tsakanin ku) Bakara
Manzon Allah shi ne shugaban masu wafai ( mafi kyautata sakayya). Ya koyar da mu mafi kyan kyautata sakayya, ya kuma bayyana  falalar matarsa Khadija a halin tana raye da bayan mutuwarta , ya kasance yana yawaita ambatonta da gode mata da nema mata gafara yana cewa : Ai lalle ita ta kasance kaza da kaza,   wasu lokutan ma ya kan yanka akuya ya yayyanka ya turawa kawayen khadija) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
Lokacin da musulmai suka yi nasara a yakin Badar suka kama mutum saba'in cikin kuraishawa Manzon Allah sai ya fadi kalmarsa  shahararriya :( Da Mud'am dan Adiyyi na raye sannan ya min magana kan wadannan doyaya da na mika mishi su) Bukhari ne ya rawaito. Tare da cewa Mud'im dan Adiyyi ya mutu kafuri, amma kafurcin sa bai hana a ambata alherinsa  da ya yi ba, da karrama shi da abin da ya dace.
Kissoshin Annabawa na cike da ambaton falalar masu falala,  na daga ciki akwai abin da ya zo a kissan Musa Amincin Allah ya tabbata a gare shi da mahaifin mata biyu da ya shayar da su.
Allah Madaukakin sarki yace : (Sai dayarsu ta zo masa tana tafe  cikin kunya sai ta ce: baba na hakika yana kiranka don ya saka maka ladan shayarwa da ka mana) sai musa ya hadu da sakayyar kyautatawarsa  wanda mahaifin mata biyun ya saka masa sabo da mutuncinsa.
Musulunci  ya daga darajan wanda ya kyautata ma ya ma ihsani, har ma ya karfafi da ka saka mishi,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Bai gode wa Allah duk wanda bai gode wa mutane) Ahmad ne ya rawaito da isnadi ingantacce da Ibnu Hibban a sahih nasa Ma'anarsa shi ne Allah bai karbar godiyan bawa bisa kyautatawarsa zuwa gare shi muddin bawan bai gode wa mutane bisa kyautatawarsu gare shi. Kuma yana butulce wa kyautatawar su. Sabo da gamewar abubuwa  biyun. Kuma na daga cikin ma'anar hadisin : Duk wanda al'adarsa butulce wa ni'imar  mutane  da rashin gode musu ,to haka nan zai rika butulce wa Allah ya bar gode masa   madaukakin sarki.  yana daga cikin ma'anarsa : - cewa duk wanda baya godiya ga mutane to fa; tamkar wanda baya godiya ga Allah ne  .
       Yana daga cikin sifofi na maida martani mai kyau  wanda ma'abota cika alkawri mai kyau suke sakayya da shi  , ya kunshi fadi da aiki  da ma zuciya  Allah madaukakin sarki ya ce :- (Idan an gaishe ku da gaisuwa  to ku gaida mai gaishe ku da  mafi kyau daga gare ta ko ku maida irinta .) ( To ku mayar da mafi kyau daga ita )
      Idan Musulmi ya mayar da gaisuwa da kwatankwacinta  ko da mafi kyau daga ita , kuma kyakkyawa  kwatankwacinta ko wadda ya fi ta! , daddadan kalma da kwatankawacinta ko wacce ta fita kyau , kyauta da kwatankwacinta ko wadda ya fi kyau daga ita,    to zuciyar mu sai su  tsarkaka  , zumincin mu sai ya karfafa  dankon zumuncin mu sai ya yi kwari,  sai sabani tsakanin mu ya yaye  .
       Matakin farko na maidawa ma'abota falala falalar su  shi ne;  yarda da falalar tasu ,  da kuma tabbatar da cancancin  godiya gare su , to wannan kuma  wata dabi'a ce da yake kan musulmai da ya dace su lizimce ta ; wanda Annabin rahama ya fiskantar zuwa gare ta  , kuma ya yi kira zuwa gare ta .
          Cika alkawari na daga cikin  kyautatuwan  Imani   Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ( Duk wanda ya  aikata muku wani abu mai kyau to ku saka mishi ) Abu Dauda ne ya rawaito da Nasa'i  da Ahmad da isnadi ingantacce
     A cikin hadisin Hakim da Baihaki    Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fiskanci tsohuwa  da fara'a  da annashuwa    yayin da ta fita Aisha Allah ya kara yarda a gare ta   sai ta tambaye shi  sai ya ce : (Ya Aisha ai ita dinnan ta kasance  tana zuwa mana a zamanin kadija , kuma lallai kyautata alkawari na daga cikin imani ) Albani ya fitar da shi a   cikin silsila ingantacce .
Musulunci ya saukaka hanyoyin sakanyawa ma'abota falala  da abin da mutum Musulmi zai iya ; da kalma mai dadi, da adu'a gare shi na alheri  da kuma  haduwar musulmi da dan'uwan shi Musulmi  cikin sakun fiska da fara'a  , wannan na daga cikin cikan wannan addinin da laduban sa  da kyawunsa  don a samu wanzuwar  zumunci da kauna da soyayya
.An karbo daga Abu zarri Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (   Kar ka raina wani abu na daga aiki mai kyau ko da a ce ka hadu da dan'uwan ka ne cikin sakin fiska ) muslim ne ya rawaito.
    Kyautata yabo da gaskiya  :- Yana daga cikin nau'ukan mayar da abu mai kyau ga ma'abota falala, An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (  Duk wanda aka yiwa kyauta to, ya yi sakayya game da shi wanda bai samu ba kuma ya kyautata yabo , domin lallai wanda ya kyautata yabo to ya yi godiya  wanda kuma ya boye to ya butulce  wanda kuma ya siffantu da abin da ba a bashi ba to kamar wanda ya  saka tufafi biyu ne na karya) Abu dauda ne ya rawaito shi da Tirmizi da isnadi mai kyau   .
    Na daga cikin  nau'i na maida martani mai kyau  ga ma'abota falala saka musu  da yin adu'a mai kyau  gare su,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:  ( Idan ba ku samu abin da za ku saka musu da shi ba  , to ku yi musu adu'a  har  sai kun san hakika kun  saka musu ) Abu Dauda ne ya rawaito shi da Nasa'i da Ahmad da isnadi mai kyau.
        Daga Usama Dan Zaid Allah ya kara yarda a gare su shi da Baban shi ya ce :- Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-(Wanda aka  kyautata a gare shi, sai ya ce : ga wanda ya mishi wannan aikin: Allah ya saka maka da alheri hakika ya kai kololuwa cikin   yabo) Tirmizi ne ya fito da shi da Nasa'i  da isnadi mai kyau.
    Wanda ya ara maka dukiya yana da kyau ka kyautata  wajen  biyan  bashin da maidawa da godiya.
   A cikin rayuwar Musulmi akwai bangarori na mutane  ma'abota falala,wadanda  kyautatawansu tsayayye ne kuma falalar su dauwamamma ce, kyautatawan su kuma yalwatacciya ce,  kuma wanda ya fi su girman falala shi ne Manzon Al'umma  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wanda Allah ya fitar da mu a dalilin shi daga duhu zuwa haske.
      Yana daga  cikin  mafi  yawan falala ga mutum a cikin mutane    kuma wanda yafi hakki a gare shi  na cika alkawari da kyautatawa  akwai iyaye biyu  wadanda suka kyautata zuwa gare shi suka bashi tarbiya tun yana karami  Allah madaukakin sarki ya ce :- (  Ubangiji ya yi umarni da kyautatawa iyaye kyautatawa idan dayan su ya isa girma  nan gare ka ko dukkan su su biyu to kada ka ce da su affafairan  kada kuma ka yi musu tsawa ka gaya musu magana mai girma mai taushi )   kuma Allah madaukakin sarki ya ce : (   Ka tausasa musu janubinka  mai taushi  horarre  don jin kai gare su ,  ka ce : ''Ubangiji  ! ka jikan su  kamar yadda suka jikaina  lokacin da suka rene  ni  ina dan karami ) .
    Daliban ilimi suna da wani nau'i  na wajibin cika alkawari  da kyautatawa ga malaman su  ta hanyar yi musu adu'a; sakamakon falala da suke da shi akan su,  Abu Hanifa ya yi adu'a wa malamin shi Hammad    Abu Yusuf shi ma  ya yi adu'a wa malamin shi Abu Hanifa , Imamu Ahmad Bin Hambal Allah ya mi shi rahama ya ce : (  Ban taba kwana ba tun shekara talatin da suka wuce har sai na yi adu'a  ga Shafi'i  na kuma nema mishi gafara .
       Mata da miji a tsakanin su akwai   kyautatawa da ke bin juna  da kuma kyakkyawa a tsakanin su ,  wanda ko wannen su ya kyautatawa dan'uwan sa kamar wani ado ne a  rayuwar sa  wanda ko wannen su dadin rai ne da amfani a zuciyan dan uwan sa ,  to kiyaye wannan alkawarin da kyautata mu'amala  da dauke kai daga kusakuran juna  na cikin sakayya mai kyau  domin lallai kyawawa suna tafiyar da munana, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( kada wani  mumini ya tsani  wata  mumina  idan har ya ki wasu dabi'u daga gare ta to akwai wasu dabi'un nata da zai gamsu da su ) muslim ne ya rawaito .
            HUDUBA TA BIYU
 Lallai abin da ya faru mai radadi na kwanannan wanda ya kasance  kafin wasu 'yan kwanaki a garin BURAIDA  wanda har ya kai ga an kashe wani jami'in tsaro  lallai  abun takaici ne da ke nuni ga jahilci da rashin hankali da dimuwa  lallai wannan tunani ne irin na da'ish masu kafurtawa  ,  suna furta numfarfashin su a jikon karshe na rayuwar su , alhali mu kuma muna da yakini cewa tunanin su  zai zo ya faku batan su kuma zai zo ya fado , wanda yake so   ya karya zaman lafiyan mu  ya kuma girgiza amincin mu ,to ba zai cinma manufarsa ba  kuma ba zai kai ga cimma muradinsa ba  kuma zai koma da hasara bayyananne  da falalan Allah  sa'annan tare da bibiyan jagororin al'amuran mu , da fadakan jami'an tsaron mu  da kuma malaman mu  Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuraishawa sun bautawa Ubangijin   wannan dakin  sabo da sabawan su da tafiya  ta dari da ta damuna  su bautawa Ubangijin wannan dakin  wanda ya ciyar da su sabo da yunwa ya amintar da su don tsoro ).
      Hakika duniyar Musulmi suna samun albishir na gaba daya  haka nan ma jama'ar Afganistan musamman  da taron karawa juna sani kan zaman lafiya da mai hidima a masallatayya guda biyu madaukaka  ya yi kira zuwa gare shi  wanda kungiyan hadin kan musulmai na duniya ya shirya a garin makka mai daraja  ,   wanda ya kwadaitar bisa watsi da harkan kashe-kashe da rarrabuwa , da kuma kira zuwa ga gyara da hadin kai   da komawa zuwa ga hukunce-hukunce na shari'a a yayin husuma da sabani .
           Wannan sako na zaman lafiya  daga masaukan wahayi na hukunta  gaggautawan mutanen Afganistan  zuwa ga  rungumar zaman lafiya ,  musamman malamai daga cikin su tare da aiki wurin tabbatar da aminci da kwanciyar hankali a garin su  bayan karon battan su da ya tafiyar da danye da busasshe( be bar komai ba ) Allah madaukakin sarki ya ce : (  Ubangiji ya alkawarta ga wadanda da suka bada gaskiya daga cikin ku suka yi aiki na gargaru lallai zai mayar da su kalifofi a cikin kasa   tamkar  yadda ya sanya wadan da suke gaban su  lallai zai tabbatar musu da addinin su wanda ya yarda da shi gare su  lallai zai musanya musu aminci bayan tsoron su da za su dinga bauta min ba za su shirkanta komai

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق