الجمعة، 25 مايو 2018

Ma'anar azumi da abubuwan lura da ya kumsa.


Hudubar Juma'a na  Masallacin Annabi na shaikh Muhammad Salah Al-Budair 9-9-1439AH
Ya ku masu azumi … farkon ramadana ya shude, har mun doshi na gomansa,
To a gaggauta a yi hanzari a yi kukan kura a dage, ku yi tsere cikin watanku kafin ya nade darensa  da tabarmarsa, ku gaggauci ramadana kafin ya tafi, ku ribace shi kafin ya shude,
Ya ku masu azumi !
Abin mamaki ga wanda zai riski ramadana azuminsa bai gyara shi ba, tsayuwansa bai girgiza shi ba, ranakunsa bai sanja  shi ba!
Abin mamaki ga mutumin da zai riski ramadana kuma yana kwadayin Aljanna da gafara da 'yantawa daga wuta amma ya sarayar da shi cikin  wasanni da da abubuwan da aka hana da haramtattu,
Ya kaiton wanda alherin ramadan ya tsere mishi!  ya hasaran wanda ya sarayar da watan ramadan!
An karbo daga Abu huraira Allah kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce  (Hancin shi ya  dongwali kasa; mutumin da aka ambace ni bai yi min salati ba, Hancin shi ya  dongwali kasa duk mutumin da ramadana ya shiga har ya fita ba a gafarta masa ba,hancinsa ya dangwali kasa wanda ya riski iyayensa biyu sun girma   basu shigar da shi  Aljanna ba) Tirmizi ne ya rawaito.
Ya wanda ke tambaya game da kurar hanya da tankaden gari da hadiyar nyawu ko suna bata azumi ko aa? Ya kai mai kiyaye kananan abubuwa  kuma ka yi sakaci a abubuwa masu girma! to ka kiyaye daga manyan zunubai  na alfahasha da laifuka, ka kiyaye daga cin dukiyan dan'uwanka musulmi, da cin mutuncin shi, da zambatan shi da zaluntarsa, da yaudararsa da mishi dabara.
Shin ko ya yi azumi mutumin  da ya kame daga ci ko sha a wunin ramadana alhali bai daina sakaci da yaransa ba ya barsu gurin matarsa da ya saka ba tare da kyautatawa ko tausayi ba ko tambaya game da su ko ciyarwa ba?
Shin ko ta yi azumi wacce ta haramta wa yaranta ganin mahaifinsu da ya sake ta ko ziyartarsa, ta karfafe su gun keta zarafin mahaifi da kuma fasikanci,?
Shin ya yi azumi mutumin da ya hana yaransa ganin mahaifiyarsu  da ya sake ta wacce ba dadi ga rayuwarsu sai da shinshinan  kamshinta, da ganin fiskanta da jin duminta irin na tausayi.
Shin ya yi azumi mutumin da ya kaurace wa matarsa ya kyale ta abar  zalunta an tauye hakkinta ratayayya ita ba mata ba kuma ba a sake ta ba.
Shin ya yi azumi wanda ya ci zarafin iyayen shi ya kaurace musu ya musu dagun kai, ya kuntata don yi musu hidima, in an tambaye shi yayi rowa, in an zarge shi sai ya yi wauta, in an sa rai game da shi sai ya basar, in an neme shi sai ya faku, bai amsawa sai da nuna isa, bai bayarwa sai don tsoro, bai san wani abu ba face " sai nan gaba".
Shin ya yi azumi kenan mutumin da ya yi bacci ya bar sallan farilla? Ko lokacin salla ya fita bai yi azahar da la'asar ba sai a bayan lokacinsu?  Kuma ya saba kan haka a cikin watan ramadan gaba daya.
Shin ya yi azumi mutumin da ya cinye  dukiyar gado na 'yan uwansa  maza da mata, ya yi fashin dukiyan marayu da miskinai, yayi sama da fadi da dukiyan wakafi, da hurumin masu hakki?
E, ya yi azumi da yake na sauke nauyin wajibi amma azumin da ke cakude da karya da alhaki da zalunci, wanda ke hade da manyan zunubai da laifuka masu girma.
Watakila ladan  azumin nasa ba zai kai  nauyin alhakin zaluncin sa ba da laifin sa .
 Ku ji tsoron Allah ya ku  wadan da suka rike baki daga abubuwan da suke  karya azumi da masu bata su  yayin azumi,  ku ka kuma  aikata abin da ya wajaba ga  musulmi   ya nisance shi    kuma ya haramta a gare shi ya aikata su  ko yaushe  .
 Yi salla irin sallan mai fata da tsoro*** Kafin ka yi azumi ka yi  azumi daga dukkan alfasha
 An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare shi y ce :( Idan ka yi azumi   to jinka da ganin ka da harshen ka su ma su yi azumi daga  karya da laifi  kada ka cutar da hadimin ka   ya zamana a gare ka akwai girmamawa da  natsuwa a wunin azumin kar ka sanya wunin da ka ke shan ruwa  daya da wunin da kake azumin)  .
An karbo daga hafsa  'yar Sirin ta ce : ( Azumi  garkuwa ce muddin mai ita bai ketata ba ; ketata shine yi da  wani).
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Wanda bai bar fadin karya ba da aiki da ita  to Allah bai bukatar sa  da ya bar abincinsa da abin shan sa ) Buhari ne ya rawaito .
 Ya wanda ya kame daga ci ko sha  a yinin  ramadana  to ka kame daga zalunci da haramun  ka kuma kame daga fin karfin mai rauni da karbe hakkin sa ba tare da yardan sa ba .
 Ya wanda ya yi azumi daga ci *** ina ma a ce ka yi azumi daga zalunci
Ko azumi zai yi amfani ga wanda ya yi zalunci *** cikin sa na cike da laifuka
Idan har bai kasance game da ji na a kwai kurumcewa ba  a idanuwana akwai rintsawa ***  a furuci na akwai  kamewa 
 To kaso na game da azumi na kawai shi ne yunwa da kishir ruwa*** ko da na ce ni na yi azumi to ba fa azumin na yi ba .
Allah ya sanya ni da ku cikin wadan da suka yi azumin ramadana  suka kiyaye shi  ba su gurbata ayukan su ba da kyautatawan su ba  da zunubai,  ina  fadin abin da kuke ji kuma ina neman gafarar Allah , to ku nemi gafarar sa  lallai shi ya kasance  ga masu komawa gare shi mai yawan gafara ne.
 Huduba ta biyu
 Ya ku musulmai :
  Wannan lokaci ne na komawa ga Allah  wannan ruwa ne na wanka mai sanyi da kuma sha .
 Ya wanda zunubai ya daure shi, ya wadan da ayukan ababan kunya suka  kulle shi , wannan wata ne da ake kwance daurarre mai sabo,
Ya wanda ya saba  da zunubai da laifuka  , ya wanda ya wayi gari ya sammaka cikin kurakuran shi yana mai nadama   ka tuba  gaba gare ka  ga bukatar ka da kuma riba , Allah yana so ya  yi kyauta da kuma  rahama  , kuma ya yi afuwa ga masu tuba   don falala daga gare shi da kuma karamci .
 Dadi ya tabbata ga wanda ya wanke zunuban shi  a cikin ramadana  da tuba  ya dawo daga kusa kuran shi kafin kwacewan lokaci.       


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق