Hudubar Juma'a
na Masallacin Annabi na shaikh Muhammad
Salah Al-Budair 9-9-1439AH
Ya ku masu azumi …
farkon ramadana ya shude, har mun doshi na gomansa,
To a gaggauta a yi
hanzari a yi kukan kura a dage, ku yi tsere cikin watanku kafin ya nade
darensa da tabarmarsa, ku gaggauci
ramadana kafin ya tafi, ku ribace shi kafin ya shude,
Ya ku masu azumi !
Abin mamaki ga wanda
zai riski ramadana azuminsa bai gyara shi ba, tsayuwansa bai girgiza shi ba,
ranakunsa bai sanja shi ba!
Abin mamaki ga mutumin
da zai riski ramadana kuma yana kwadayin Aljanna da gafara da 'yantawa daga
wuta amma ya sarayar da shi cikin
wasanni da da abubuwan da aka hana da haramtattu,
Ya kaiton wanda alherin
ramadan ya tsere mishi! ya hasaran wanda
ya sarayar da watan ramadan!
An karbo daga Abu
huraira Allah kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce (Hancin
shi ya dongwali kasa; mutumin da aka
ambace ni bai yi min salati ba, Hancin shi ya
dongwali kasa duk mutumin da ramadana ya shiga har ya fita ba a gafarta
masa ba,hancinsa ya dangwali kasa wanda ya riski iyayensa biyu sun girma basu
shigar da shi Aljanna ba) Tirmizi ne ya
rawaito.
Ya wanda ke tambaya game da kurar hanya da tankaden gari da hadiyar
nyawu ko suna bata azumi ko aa? Ya kai mai kiyaye kananan abubuwa kuma ka yi sakaci a abubuwa masu girma! to ka
kiyaye daga manyan zunubai na alfahasha
da laifuka, ka kiyaye daga cin dukiyan dan'uwanka musulmi, da cin mutuncin shi,
da zambatan shi da zaluntarsa, da yaudararsa da mishi dabara.
Shin ko ya yi azumi mutumin da ya
kame daga ci ko sha a wunin ramadana alhali bai daina sakaci da yaransa ba ya
barsu gurin matarsa da ya saka ba tare da kyautatawa ko tausayi ba ko tambaya
game da su ko ciyarwa ba?
Shin ko ta yi azumi wacce ta haramta wa yaranta ganin mahaifinsu da ya
sake ta ko ziyartarsa, ta karfafe su gun keta zarafin mahaifi da kuma
fasikanci,?
Shin ya yi azumi mutumin da ya hana yaransa ganin mahaifiyarsu da ya sake ta wacce ba dadi ga rayuwarsu sai
da shinshinan kamshinta, da ganin
fiskanta da jin duminta irin na tausayi.
Shin ya yi azumi mutumin da ya kaurace wa matarsa ya kyale ta abar zalunta an tauye hakkinta ratayayya ita ba
mata ba kuma ba a sake ta ba.
Shin ya yi azumi wanda ya ci zarafin iyayen shi ya kaurace musu ya musu
dagun kai, ya kuntata don yi musu hidima, in an tambaye shi yayi rowa, in an
zarge shi sai ya yi wauta, in an sa rai game da shi sai ya basar, in an neme
shi sai ya faku, bai amsawa sai da nuna isa, bai bayarwa sai don tsoro, bai san
wani abu ba face " sai nan gaba".
Shin ya yi azumi kenan mutumin da ya yi bacci ya bar sallan farilla? Ko lokacin
salla ya fita bai yi azahar da la'asar ba sai a bayan lokacinsu? Kuma ya saba kan haka a cikin watan ramadan
gaba daya.
Shin ya yi azumi mutumin da ya cinye dukiyar gado na 'yan uwansa maza da mata, ya yi fashin dukiyan marayu da
miskinai, yayi sama da fadi da dukiyan wakafi, da hurumin masu hakki?
E, ya yi azumi da yake na sauke nauyin wajibi amma azumin da ke cakude
da karya da alhaki da zalunci, wanda ke hade da manyan zunubai da laifuka masu
girma.
Watakila ladan azumin nasa ba zai
kai nauyin alhakin zaluncin sa ba da laifin
sa .
Ku ji tsoron Allah ya ku wadan da suka rike baki daga abubuwan da suke karya azumi da masu bata su yayin azumi, ku ka kuma aikata abin da ya wajaba ga musulmi
ya nisance shi kuma ya haramta a gare shi ya aikata su ko yaushe
.
Yi salla irin sallan mai fata
da tsoro*** Kafin ka yi azumi ka yi
azumi daga dukkan alfasha
An karbo daga Jabir Allah ya kara
yarda a gare shi y ce :( Idan ka yi azumi
to jinka da ganin ka da harshen ka su ma su yi azumi daga karya da laifi kada ka cutar da hadimin ka ya zamana a gare ka akwai girmamawa da natsuwa a wunin azumin kar ka sanya wunin da
ka ke shan ruwa daya da wunin da kake
azumin) .
An karbo daga hafsa 'yar Sirin ta
ce : ( Azumi garkuwa ce muddin mai
ita bai ketata ba ; ketata shine yi da
wani).
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda
a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Wanda bai bar fadin karya ba
da aiki da ita to Allah bai bukatar
sa da ya bar abincinsa da abin shan sa )
Buhari ne ya rawaito .
Ya wanda ya kame daga ci ko
sha a yinin ramadana
to ka kame daga zalunci da haramun
ka kuma kame daga fin karfin mai rauni da karbe hakkin sa ba tare da
yardan sa ba .
Ya wanda ya yi azumi daga
ci *** ina ma a ce ka yi azumi daga zalunci
Ko azumi zai yi amfani ga wanda ya yi zalunci *** cikin sa na cike
da laifuka
Idan har bai kasance game da ji na a kwai kurumcewa ba a idanuwana akwai rintsawa *** a furuci na akwai kamewa
To kaso na game da azumi na
kawai shi ne yunwa da kishir ruwa*** ko da na ce ni na yi azumi to ba fa azumin
na yi ba .
Allah ya sanya ni da ku cikin wadan da suka yi azumin ramadana suka kiyaye shi ba su gurbata ayukan su ba da kyautatawan su
ba da zunubai, ina
fadin abin da kuke ji kuma ina neman gafarar Allah , to ku nemi gafarar
sa lallai shi ya kasance ga masu komawa gare shi mai yawan gafara ne.
Huduba ta biyu
Ya ku musulmai :
Wannan lokaci ne na komawa ga
Allah wannan ruwa ne na wanka mai sanyi
da kuma sha .
Ya wanda zunubai ya daure shi, ya
wadan da ayukan ababan kunya suka kulle
shi , wannan wata ne da ake kwance daurarre mai sabo,
Ya wanda ya saba da zunubai da
laifuka , ya wanda ya wayi gari ya
sammaka cikin kurakuran shi yana mai nadama
ka tuba gaba gare ka ga bukatar ka da kuma riba , Allah yana so
ya yi kyauta da kuma rahama
, kuma ya yi afuwa ga masu tuba
don falala daga gare shi da kuma karamci .
Dadi ya tabbata ga wanda ya wanke
zunuban shi a cikin ramadana da tuba
ya dawo daga kusa kuran shi kafin kwacewan lokaci.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق