الجمعة، 18 مايو 2018

FALALAR AZUMIN RAMADAN


Hudubar Masllacin Annabi 2-Ramadan -1439AH
Hudubar Farko:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin sarki,  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa ,  kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa  da aminci tabbatacce mai yawa,
Bayan haka ku ji tsoron Allah - ya ku bayin Allah - hakkin tsoronsa, ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.
Ya ku musulmai!
Ranaku da dararraki na tafiya cikin sauri, shekara na nade watanninsa daya bayan daya, a cikin haka Masu bauta  kuma suna komawa ne ga Allah, ba da jimawa ba zasu je su riski ayyukansu,
Na daga falalar Allah da karamcinsa ya  zaba musu zamuna da lokuta na da'a, ya zabi wasu ranaku da dararraki da wasu sa'o'I don kara kaimin kwadayin ibada da kimtsawa, masu munafasa kuma suna tsere gurin ayyukan alheri , a duk lokacin da jinjirin watan ramadan ya bullo sai ya buso mana wasu kyauta masu albarka, sai musulmai su fiskance shi zuciyarsu na cike da farinciki da annashawa,  zai iya yiwuwa wani sa'a na karbar aiki ya riski bawa  sai ya kai wasu darajoji na yarda da walwala.
Wata  mafi daraja da tsarkaka ta sauka gare mu,lokaci ne mai girma Allah ya kebance ta da karramawa da daukakawa,sai ya turo manzonsa a cikinta ya saukar da littafinsa, ya farlanta azumtanta,  sa'o'inta na da albarka, duk lokutanta ana raya su da alheri ne, alheru na bibiyan juna a cikinta, albarka na gamewa a cikinta, wata ne na ihsani da sadaka zamani ne na neman gafara da kankaran zunubai,  wuninta azumi ne darenta tsayuwa ake yi, ana raya ta da Alkur'ani, ana bude kofofin Aljanna a cikinta, ana rufe kofofin wuta,ana daure shaidanu da mari a cikinta, akwai dare a cikinta  da yafi wata dubu alheri, duk wanda aka hana alherin cikinta to lalle katangagge ne daga samun alheri.
Ramadana fage ne mai yalwa don tsere cikin aikin da'a, kyauta ne na gyaran zuciya daga dauda da matsaltsalu,wata ne mai karamci ana ribanya ayyuka a ciki, ana kankare kusakurai a ciki da laifuka, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(salloli biyar da juma;a zuwa wata juma'a  da ramadan zuwa wani ramadan na kankare abin da ke tsakaninsu muddin an nesaci manyan zunubai) Muslim ne ya rawaito
A cikin watan ne musulmai ke sauke nauyin daya daga cikin rukunan musulunci, kuma wani abu ne na bayyane da ke nuna girman wannan addini, da kuma hada kan musulmai, a nan ne fadin Allah Madaukaki sarki ya ke bayyana  (Lalle wannan al'umarku ce guda daya kuma nine Ubangijinku ku bauta min)
  Ribatan lokutan alheri  budi ne daga Allah ga wanda ya so daga cikin bayinsa,a cikin ramadan na ne tushen Ibadoji  mafi girma ke gamewa  ga salihan bayi.
Salla sadarwa ne tsakanin bawa da Ubangijinsa,ba ta rabuwa da musulmi a dukkanin rayuwarsa, sallar mutum cikin jam'i  farilla ne tana daidai da sallar mutum a gidan shi da kasuwan shi sau ashirin da bakwai, ya dace da musulmi  ya nemi taimako da salla bisa azumin shi , kuma ya zama yana da kaso mafi girma na salla a darensa, To (wanda ya yi tsayuwan dare na ramadana cikin imani da neman lada an gafarta masa abin da ya gabata na daga zunuban shi) Bukhari da Muslim ne suka rawaito
(Wanda ya yi tsayuwan dare tare da limami har ya tafi to an rubuta masa tsayuwan dare)Tirmizi ne ya rawaito.
Zakka da sadaka tsarkaka ne ga dukiya da habaka, wadata ne ga zuciya da tsarkakuwa tasirinta a bayyane yake ga zuciya da dukiya  da yara, mai tunkude bala'i  mai janyo  yalwa, wanda ya yi kyauta  ga bayin Allah, Allah zai yi mishi kyauta, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :  Allah Madaukakin sarki ya ce ya kai dan Adam ! ka ciyar zan ciyar da kai.)Bukhari da Muslim suka rawaito
Dukkan mutum yana inuwar mutuwarsa ne ranar Alkiyama, to ku yi sadaka da da dan kadan ne, ka  dadawa rai da ita, ka taimaki maragalihu,  (Duk wanda ya ciyar da mai azumi yana da kwatankwacin ladan shi)
Kuma yana daga cikin koyarwarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai  ciyarwa da kyauta, yana bayar da kyauta irin kyautan wanda bai tsoron talauci, in ya zo bada kyauta sai ya yalwata, in ya bada sai yawaita. Ba ya maida mai tambaya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ,ba a taba tambayarsa wani abu ba face ya bada,
Manzon Allah ya fi kyauda a cikin ramadana, ya kasance a cikinsa mai kyauta kamar iska mai kaiwa ga kowa.
Azumi shi ne ibada mafi girma a wannan wata  mai falala, Musulmai na guzurin takawa a cikinsa, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku wadanda suka yi imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka gabace ku ko zaku ji tsoron Allah)
Ladansa ba iyaka ko kididdiga, Allah ya ce a hadisul kudsi : (Dukkan aikin dan adam na shi ne sai azumi  don shi nawa ne ni zan saka game da shi)Bukhari da muslim ne suka rawaito.
(Wanda ya yi azumin ramadana cikin imani da neman lada daga Allah  an gafarta masa abin da ya gabata na daga zunubansa)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Azumi na shamaki tsakanin ma'abocinsa da sharri da zunubai, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Azumi garkuwa ne)Tirmizi ne ya rawaito
Ba abin da ya fi  wani  ya  nemi taimako da shi bisa takawa da kiyaye dokokin Allah da nesatan abubuwan da Allah ya haramta  kamar  azumi, Ibnul kayyim Allah ya mishi rahama  ya ce : ( Amfaninsa ya fi karfin iyakancewa  yana da tasiri na ban mamaki  wurin kiyaye lafiya.)
A lahira zai yi ceto ga ma'abotansa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Azumi da Alkur'ani suna ceto ga bawa a ranar Alkiyama sai azumi yace ya Ubangiji na hana shi abinci  da sha'awarsa a wuni to ka cece shi don ni, sai Alkur'ani ya ce : Na hana shi barci da dare to ka bani cetonsa,  yace sai a basu cetonsa.Ahmad ne ya rawaito.
Na daga cikin ayyuka na kwarai da ake ribata akwai umra , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Umra a ramadan na daidai da hajji)Bukhari da Muslim ne suka rawaito
Kur'ani maganar Allah ne kuma hujjarsa  ne a kan bayinsa, shi ne mabubbuga na hikima, mu'ujiza ce na sakon manzanci, babu hanya zuwa ga Allah sai ta gun shi, babu tsira gare mu ba tare da shi ba, haske ne  na basira da kuma gani  wanda ya kusance shi zai samu  daukaka  wanda yayi riko da shi zai samu buwaya   tilawar sa lada ne da shiriya, bitar sa kuma ilimi ne da tabbatuwa  aiki da shi   kariya ne da aminci  ilmantar da  shi  da kira zuwa gare shi kambina a kawunan masu biyayya  ,   a ramadana  ana karfafa yawaita karanta shi  da tadabburi da neman iliminsa  da kuma ilmantar da shi da aiki da shi  da kuma bin koyarwar sa  a cikin shi ne ya sauka , Allah madaukakin sarki ya ce: ( watan ramadana da a ka saukar da alkur'ani a cikin ta  shiriya ne ga mutane da  bayyanannu na daga shiriya da rarraabewa).Jibrilu amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana bitan alkur'ani tare da Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sau daya a kowace  shekara ,   a shekarar da ya rasu a cikinta  ya yi bita tare da shi  sau biyu   tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi .
    Addu'a ibada ce kuma kusanci ce , wata ganima ce da ba tare  da  wahala ba  kuma riba ce wanda babu asara a cikin ta , yana  janyo sauki kuma makiyi ne ga dukkan wani bala'I  ba wanda zai halaka muddin yana adu'a,  da shi ne bawa yake riskan burin shi ya samu bukatar sa  , sau da yawa yakan  kusanto da abin da yake nesa  kuma sau da yawa yakan saukake abu  mai wahala sau da yawa kuma yakan yaye bakin ciki  mafi karbuwan adu'a shi ne wanda aka yi shi  a cikin karshen dare , idan bawa ya marairaice a gaban Ubangijin shi  , sai Allah ya  amsa mishi bukatar sa ,  idan rayi ta ji yunwa sai zuciya ta tausasa ta kwanta  mai azumi ba a maida adu'ar sa har zuwa lokacin buda baki  Ibn Rajab Allah ya mishi rahama  ya ce : (   Mai azumi a daren sa da yinin sa yana cikin ibada ne  , ana  amsa adu'ar sa  a azumin sa haka kuma yayin buda bakin sa  , to shi a wunin sa yana azumi kuma yana mai hakuri  a daren sa kuma  mai ciyarwa ne kuma mai godiya )
Wanda ya yi gamon-katar shi ne wanda ya kwankwasa kofar sama, ya sanya wa kansa a wadannan ranaku da dararraki wani abin adana.
Ambaton Allah ibada ce mai girma mai sauki,duk wanda ya ambaci Allah to Allah zai ambace shi, bawa idan bai shagaltar da harshensa ba da anbaton Allah ba to kuwa zai shagaltar da shi da magana mara amfani da na sabo.
Addini muamala ne, mafi  cancanta ihsaninka cikinn halittu shi ne wanda Allah ya gwama hakkinsu  da na shi, Iyaye biyu Aljannaka ne kuma wutar ka ne, su suka fi cancanta ka kyautata musu cikin mutane, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi,ya ce : (Hancinsa ya dumbuli kasa ! Hancinsa ya dumbuli kasa! Hancinsa ya dumbuli kasa! Sai aka ce da shi wane ne? wanda ya riski iyayensa biyu sun girma ko daya daga cikinsu ko su biyun   bai shiga Aljanna ba),Muslim ne ya rawaito.
(zumunci na hade ne da Al'arshi ne tana cewa ya Allah duk wanda ya sada ni ka sada misi, wanda ya yanke min ka yanke mishi)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
(wanda zai burge shi da a yalwata mishi a arzikinsa,  a jinkirta masa a bayansa to ya sada zumuncinsa) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Na daga cikin cikan daa  a kiyaye su daga dukkan abin da zai tawaye su ko ya warware su
Mai azumi ya fi tsananin son ya kiyaye ibadarsa da azuminsa daga abin da zai keta alfarmansa ko ya bata shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( a ranar da dayanku yake azumi to kada  yayi batsa, kada ya yi hayaniya, idan wani ya zage shi ko ya nemi fada da shi,  to yace ni mutum ne, mai azumi ne  )  Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Na daga cikin koyarwar magabata Allah ya musu rahama idan sun yi azumi sai su zauna a masllaci sai su ce : Mu kiyaye azuminmu kar mu ci naman wani, Ahmad Allah ya mishi rahama ya ce : Ya dace ga mai azumi da ya bibiyi azuminsa ya bashi kulawa tun daga harshensa  kada ya yi musu, ya dace ga mai azumi idan ya yi azumi ya kiyaye jinsa da ganinsa   da harshen sa da dukkan  gabbansa , kada ya sanya ranar azumin sa kamar ranar shan ruwan sa , 
Bayan haka ya ku musulmai :
 To lallai biyayya bata kasancewa cikakkiya  kuma bata tsayawa akan kwabrinta  da kuma gun da ya dace sai tare da kauna wanda za ta kai ma'abocinta zuwa ga ikilasi  da gaskiya  wanda ke haifar da kekkewar bin sunna , aiki baya kasancewa na kusanci har sai tushen shi  da ma'ingizan shi ya kasance imani ne ba al'ada ba da son rai , ba kuma neman suna ko yi don riya ba   kuma har sai ya kasance manufar sa  shi ne neman lada gun Allah da kuma yardar sa  idan imani ya hadu da neman lada a aiki to nan ne karbuwa yake tabbatuwa da kuma gafara .
         INA NEMAN TSARIN ALLAH DAGA SHAIDAN ABIN JEFEWA
(Ku yi gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijin ku da aljanna  da  fadinta  sammai da kassai  antanajeta ga masu tsoron Allah ).
Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin al'kur'ani mai girma


HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah bisa ga kyautatawan sa  godiya ta tabbata a gare shi bisa ga datarwansa   da kuma baiwarsa  na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya  ina mai girmama sha'anin sa  , kuma na shaida Annabinmu Muhahammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne  tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi  da iyalan shi da sahabban shi da aminci tabbatacce mai kari .
  YA KU MUSULMAI :
Duniya za ta kare da jin dadin ta da kuma bakin cikin ta shekaru za su kare da   tsawon su da gajertan su  kowa ya je ya hadu da Ubangijin su to a wannan lokacin ne fa dukiya ba zai yi amfani ba ko 'ya'ya face wanda ya zo wa Allah da zuciya  lafiyayyiya  , to ku fiskanci watan ku da tuba na gaskiya  , kuma ku kulla azama bisa ga ribatanta da kuma raya lokutan ta da biyayya , rayuwan duniya ba wani abu ba ne face wasu numfashi  kididdigaggu da kuma ajali  iyakantacce  , ku ribaci lokuta masu daraja   ku sani  kuma ku yi fata kuma ku yi bushara  , hasararru su ne wadanda suka riski ramadana ba a gafarta musu ba , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :  (Hancin shi ya  dongwali kasa duk mutumin da ramadana ya shiga har ya fita kafin a gafarta masa ) Tirmizi ne ya rawaito
 (Duk wanda bai bar fadin karya ba da kuma aiki da shi to ba ruwan Allah da ya bar abin cin sha da ruwan shan sa ) Bukhari da Muslim suka rawaito .
Mafi girman abin da zai gyara zuciya shi ne ambaton Allah da kuma lizimtar alkur'ani mai girma, da tsayuwan dare,  da zama da mutanen kwari .
Sannan ku sani ; lallai Allah ya umarce ku da salati da aminci ga Annabin sa ………
  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق