الجمعة، 4 مايو 2018

SURATUL MA'UN (AKIDA DA HALAYYA)


Hudubar Juma'a  a Masallacin Annabi tare da shaikh Abdulbari dan Awad Assubaiti 18-8-1439 AH
Allah ya saukar da littafinsa mai girma don shiryar da Dan-Adam , surorinsa haske ne, ayoyinsa fayyacewa ne, kuma ruwan marmaro  ne da bai  fakewa, mashayan ruwa ne da bai bushewa, ko gurbacewa, wanda ke cikin damuwa da bakin ciki in ya fiskance shi zai samu warakarsa cikinsa, haka wanda ke cikin bacin rai in ya koma masa zai samu  abin da zai rarrashe shi a cikinsa ya bashi annashawa.
Na daga cikin gwalagwalai masu tsada da ban kaye da ke cikin Alkur'ani akwai suratul ma'uni,
( Bamu labarin wanda yake karyatawa da ranar sakamako.
Shi ne wanda yake ingije maraya.
Ba ya kwadaitarwa bisa ga ciyar da miskini.
To azaba ta tabbata ga masallatan nan.
Wadan da suke rabkana ga barin sallarsu.
Wadan da suke riya kuma suke hana agaji.) Alma'un 1-6
Sura ce mai girma tsarin gininta ta bayyana auratayya mai karfi da ke tsakani kuduri da halayya,
Wanda ke karyata ranar sakayya shi ne mai karyata ladan Allah da ukubarsa, kuma ya karyata hisabi, imani da ranar lahira bai zauna da gindin shi ba a cikin zuciyarsa, mummunar kuduri na kai ga lalacewan aiki, lalacewan aiki alama ne na lalacewan kuduri.
Me yasa aka sifanta shi da mai karyata sakayya, sabo da yana karyata addini ne, sabo da a rayuwansa bai yi wani abu da ke hukunta yana yin addini ba kamar ya tabbatar da haka da harshensa kuma zuciyarsa ta gaskata,sai dai bai aiwatar da jikinsa ba abin da addini ya kumsa  na halayya da dabi'un addini ba, da bada hakki na imani da ke kansa ba, da bin tafarkin alkur'ani, kuma kowa ya sani imani fadi ne da harshe da gaskata wa da zuciya da aiki da gabbai.
Wanda imaninsa da hisabi da sakayya  ya yi rauni  to shi ne mai karyata addini, wanda zuciyarsa ta kekashe ta dunkule ta bushe, na daga cikin sifarsa yana ingije maraya ya walakanta shi ya cutar da shi, shi bai iya da imaninsa mai rauni da ya kyautata  rayuwarsa da halinsa, ya tsoraci mummunar aiki,
To ina kimar addini idan tasirinsa bai bayyana ba a halaye da dabi'u ba?
To ina hakikanin imani idan bai sa mutum ya yi laakari da waninsa ba har ya yi mishi alheri ba da aikata ihsani da ciyar da miskini kai da kwadaitarwa bisa ciyar da miskini, ko da a ce abin da Allah ya nema a yi abu ne na abin duniya to yin shi alama ne imani.
Imani da tadawa da sakayya shi ne  zai ja ka zuwa ga gaskiya, wanda zai dasa fiskantar ayyukan kwarai har ya zama mishi jiki, idan ya taso a kai, ba zai mishi wahala ba zai tsarkaka  ba tare da wani nauyi ba.
Kekashewar zuciya na kaiwa zuwa ga gafala da karyata addini, maganin haka na cikin hadisin mafificin halitta,Manzon halitta  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, lokacin da wani mutum ya koka mishi bushewar zuciyarsa sai ya ce: Ka shafa kan maraya ka ciyar da miskini) Albani ya rawaito cikin sahih Attargib wattarhib.
A fadin Allah : (ba su kwadaitarwa bisa ga ciyar da miskini) akwai nuni ga cewa musulmi ana so ya kwadaitar da waninsa wurin yin ihsani, hakan kuma ba zai sauke nauyin da ke kansa ba aikata alheri ga masu rauni na daga marayu da miskinai gajiyayyu tare da kiyaye mutuncinsu da  yin nesa daga karya zukatansu, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Magana kyakkyawa da gafara ya fi alheri kan sadaka da gori ke binta)
Mafi suran ihsani shi ne taimaka  musu da kayan masrufi da zai taimaka musu don tafiyar da rayuwarsu, da samar musu da hanyoyi na  aiki ga zauna gari banza daga cikinsu da tattala su da shirya su da samar musu da kayan aiki.
(To azaba ta tabbata ga masallatan nan). Na daga cikin sifofinsu suna yin salla ne na jeka na yika,ba tare da aikata abin da sallar ta kumsa ba,ta wofinta daga hakikanin manufarta.rukunanta kuma a tawaye. Wani mutum ya shiga masallaci ya yi sallah a halin Annabi na zaune a gefe, sai ya zo yayi mar sallama sai Annabi ya ce: ( Je ka sake sallah don ba salla ka yi ba.) Bukhari ne ya rawaito.
Wanda ya yi lura da halin wadanda basu taimakawa marayu kuma basu ciyar da miskini, suna zamba kuma suna karya, kuma suna saba alkawari, kuma suna zalunci zai samu suna rabkana ga barin sallarsu.
Duk wanda ya tawaye sallarsa to sai ya fi tawaye  duk wani abu  komabayanta.
Idan ibada ta rasa ma'anarta  sai ta zama kawai motsa jiki ne da ba karfafan imani ko gyaran hali, sai tasirinta ya raunana a rayuwa, nassoshin kur'ani da hadisi sun bayyana hikimar shar'anta ibadoji  da kuma manufofinta da tasirinta a rayuwar mutane, kuma wasu makarantu ne na tarbiyya, Allah Madaukakin sarki ya ce : (ka tsaida sallah don sallah na hana alfahasha da munkari)
Allah ya ce game da azumi (ya ku wadanda suka yi imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka gaba ce ku ko zaku ji tsoron Allah)
Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Duk wanda bai bar fadin karya ba da aiki da ita to  Allah bai da bukatar ya bar abincinsa da abin shansa) Bukhari ne ya rawaito.
Allah ya ce : Karbi sadaka daga dukiyoyinsu ka tsarkake su da ita ka kwalle su daga tsatsar zunubai).
Yace game da Hajji : (Namanta ba ya tarar da Ubangiji ko jininta sai dai tsarkakar niyya ce take samunsa daga gare ku) Hajj  37
Sallah ita ce karshen abin da zaa  rasa na daga addini, idan  ta tawaya to addini gaba daya ya tawaya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(za a kwance igiyar riko na musulunci gaba gaba, a duk lokacin da wata igiya ta kwance sai mutane su riki wacce ke bi mata, wacce zata fara warwarewa ita ce hukunci na karshe ko ita ce sallah)     
  Ingantacce ne Albani ya rawaito shi cikin Attargib Wattarhib kuma yana da wani hadisi da zai karfafe shi a matsayin shahid.
Idan an datar da bawa  gurin yaki da musibar  rabkanuwa daga barin ibada to suratul Ma'un zata tunatar da shi game da gyaran zuciyarsa daga riya  da fadin Allah (Wadan da suke riya) wato masu yin riya a cikin sallah da waninta :ta hanyar aikata abu da yin shi ba don Allah ba,sai don neman yardar mutane, Riya na daga cikin manyan zunubai na zuciya, yana rusa aiki ya hana shi samun karbuwa a gurin Allah. Na daga cikin abin da ayar ke nuni gare shi muna fahimtar niyyar da ta cakuda da riya na sauya aiki nagari ya koma sabo, wanda ma'abocinta ya cancanci bone. Allah Madaukakin sarki ya ce :   
(To azaba ta tabbata ga masallatan nan.
Wadan da suke rabkana ga barin sallarsu.
Wadan da suke riya).
Haka nan ne zuciyar da ta rasa ikhlasi maganar ta ba ta da kimai, ibada ba zata yi wani tasiri ba a halayenta, kuma ba zaa karbi aikinta ba, ba tsarkaka ga ruhinta.
Na daga cikin mabudi mafi girma na nasara : a datar da bawa ga jan ragamar sha'awarsa ta riya ya ja mata linzami, kuma ya mika wuyarsa ga Allah, ya yi ikhlasi a aikinsa, niyyarsa kuma ya fiskance shi da ita, ya tace ta daga neman wata ganima, ko sha'awa ko matsayi ko dukiya, ko suna, ko samun matsayi cikin zukatar mutane, ko neman yabonsu, ko gudun zargi a gare su, Allah Madaukakin sarki na cewa a hadisin Alkudusi: (ni ne mafi wadatuwa daga abokan tarayya, duk wanda ya yi wani aiki ya hada ni da wani a ciki to na bar shi abokin tarayyar tasa) Muslim ne ya rawaito.
Huduba ta biyu
Karshen aya ta wannan sura na nuni ga muhimmanci halye na gari ga al'uma, ta hana zamewa kankamo, Allah Madaukakin sarki ya ce : ( kuma suke hana agaji.) wato suna hana bada aron abin da mutane suke arawa junansu, cikin abin da ba a saba hana wa ba a al'adance.
Wadannan  basu kyautata bautan Ubangijinsu ba, basu kuma kyautatawa halittunsa ba, ta hanyan bada aron abin da zaa amfana da shi  a taimaka da shi, tare da wanzuwar  abin a komo da shi ga mai shi,  to wadanna n mutanen  sun fi kusa da hana bada zakka da abubuwa na neman kusanci sama da wani abu,   
( Bamu labarin wanda yake karyatawa da ranar sakamako.
Shi ne wanda yake ingije maraya.
Ba ya kwadaitarwa bisa ga ciyar da miskini.
To azaba ta tabbata ga masallatan nan.
Wadan da suke rabkana ga barin sallarsu.
Wadan da suke riya kuma suke hana agaji.) Alma'un 1-6
   
  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق