السبت، 18 أغسطس 2018

laduban Hajji


Hudubar  Juma'a  a Masllacin Annabi  6-12-1439AH
Sheikh Salah bin Muhammad Al- Budair
Hudubar farko:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah , godiyar da ta dace da ni'imarsa da kyautarsa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, ba abi bauta bisa cancanci koma bayansa.Na shaida cewa Annabinmu  kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne , Annabinsa ne zababbensa  abin kaunarsa ,Majibincinsa yardajjensa, abin kulawarsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da Iyalan shi da sahabban shi salati madawwami  muddin gari na waye wa haske na bayya
Bayan haka ya ku musulmai!  Ku ji tsoron Allah ta hanyar aiki zuwa ga neman yardarsa da nesatan saba masa .
( ya ku wadan da suka yi  imani ku ji tsoron Allah cancancin tsoronsa kar ku mutu face kuna musulmai)
Ya ku musulmai!
Hakika iska kakkamsa ta kada tsarkakakka  daddada  wacce ke dauke da kamshin ayyukan Hajji da ruhinsa, da labaransa da manyan alamominsa da farillansa, da Haramin Allah mai aminci  da ya cika shi  da karama  da kawa da kaye da  tsarkaka da daukaka,
Ga tawagar Alhazai suna nufan  Dakin Ka'aba suna (talbiyya  ) amsa kira daga kowane sako mai zurfi suna cike da farin-ciki  da dadin rai da washewar zuciya.
     Wannan tawagar Allah din wanda ta fiskanto zuwa ga Ubangijinta cikin gaggawa ta shimfida tafukan kaskanci tana mai rusunawa ,  sai ga idanuwanta na cika da hawaye , adu'o'in ta na daguwa zuwa sama 
     Gare ka na zo ya Ubangiji ina mai amsa kira *** Ka albarkaci hajjina da adu'o'I  na ya Ubangiji
Na zo  babu guzuri fatana ne kyautar ka  *** Baya hasara duk wanda ya  nemi kyautan ka
   Alhazan dakin Allah  ku girmama harami  kuma ku ga  girmar alfarmar sa  ku kiyaye matsayin sa  ku bada kariya ga kwarjinin sa ,  ku kiyaye bin doka da oda , ku yi nesa da abin da zai kawo matsala a aikin haji  ko kuma zai sabawa manufofin shi  ko kuma zai ci karo  da hadafin shi   haji ba wuri ne na husuma da cece ku ce ba       da musu  ba kuma gune na  taron gangami ko zanga-zanga ba  ba kuma gu ne na daga tutoti na ta'assubanci  ba ko  na  kungiyanci ba   Hajji  girman shi ya fi a ce wuri ne  na bajekolin sabani da kungiyanci   da mazhabanci  ko guri ne na bangaranci na siyasa ba .
     Ya ku Alhazai   da masu Umra ku nemi fahimtar fikhun Hajji  da sharudan isan  sa da siffan aiwatar da shi   kafin ku sanya ihrami  ku nufi dakin ka'aba mai alfarma  sau dayawa Alhaji  kan  aikata wani babban al'amari  har sai ya kai gari mai tsarki sannan ya kama aikin shi na hajj  sannan gashi bai san hukunce-hukuncen shi ba  bai kyautata cika shi ba  sai ya koma zuwa garin shi yana mai halin ya bar wani  rukuni    ko ya yada wani sharadi  ko kuma ya yi sakaci da wani abu na wajibi ko ya aikata wani  abin da aka hana mai ihrami ya aikata ,    ko ya zo da wani abu da aka yi gargadi a kai    .
 YA TAWAGAN   ALHAZAI DA MAZU UMRA DA MAZIYAR TA :
Akidar musulunci   ta hada ku , farillan hajji ya sa ku  a tsari  dankon zumuncin addini ya hada  ku  to, ku tausayawa juna    ku yi  ludufi  , ku yi taimakekeniya    kada ku yi tunkudedeniya  kar ku yi cunkoso kar ku yi fada  ku tausayawa masu rauni   ku shiryar da wanda suka bace   ku taimaki gajiyayye mabukaci  .
    Wajibi ne a gare ku ku tausaya   ku yi dako  da saukin lamari da  yafiya da barin cunkoso   da kuma janyo natsuwa  da kuma jin tsoron Allah a cikin zuciya  da lazimtar     mutuntawa da tausasawa , .
    Na hore ku da ku yi nesa daga jidali da musu   da dadin baki  da kiyaye cece ku ce  da jayayya  da kuma wasa irin na magana  ku nisaci fadin batsa da alfasha  da yasassar magana  da kauracewa juna  da zage-zage da  suka  lakuba marasa kyau, ku kiyaye Hajjin ku  daga kazantar shirka , da najasar bidi'o'I da fararrun abubuwa .
           Ku nisanci ketare iyaka   ku jefi  jamra da kananan duwatsu wanda girman su bai fi na gujjiya ba  ko kuma  kwallan dabino ,   ko kuma  kan yasu    ku kiyaye ketare iyaka na shari'a  ku yi koyi da masoyi abin kauna zababbe   tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ,  a  ibadodin ku da ayukan ku na hajji  ku yawaita tuba da istigfari    ku bayyana kankan da kai da marairaicewa da nadama da nuna bukatuwa ,  da nuna talauci da nuna bukata ga Allah     domin ku dinnan ku na wurin da rahama ke zuba  kuma kuna bigire da wurin karba  da wurin da ake sa ran karban adu'a  da gafara da 'yantawa daga wuta  ku tuna girman wurin da darajan zamanin Allah na karban adu'o'in ku da amsawa da neman gafarar ku da yarda da karban Hajjin ku  da sanya  aikin ku ya zama abin  godiya zunuban ya zama abi gafartawa  Hajjin ku ya zama   wadda aka yi da'a ne a cikinta , wanda ya yi hajji baiyi batsa ba bai yi fasikanci ba  zai koma kamar yanda mahaifiyar  shi ta haifiyar shi ta haife shi, shi hajjin da aka yi da 'a a cikin shi bai da sakayya sai aljanna ina fadin abin da kuke ji kuma ina neman gafaran Allah  , ku nemi gafaran Allah  domin shi mai yawan gafara ne  ga masu komawa gare shi da tuba.
HUDUBA  TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga  Allah wanda bisa ludifin sa   ya tattara wanda ya tattaro    na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah wanda shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya  ya warkar da ni'imar sa da mutumin da ciwon sa ya sa ya yanke tsammani daga magani   na shaida cewa Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad bawan sa ne kuma Manzon sa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi , tsira mai wanzuwa da aminci mai bibiyan juna .
BAYAN HAKA:
YA KU MUSULMAI:- ku ji tsoron Allah ku yi murakabarsa , ku mishi biyayya kada ku saba masa,    (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah   ku kasance tare da masu gaskiya  )
YA KU MUSULMAI :
Ranar arfa rana  ne mai daraja  da daukaka  kuma idi ne mai girma  ga ma'abota maukif   rana ne da ake 'yanta  wuyaye a cikin shi  ana sauraron adu'o'i kuma a amsa  rana ne wanda alherin Ubangijin mu ya yawaita kuma ya dadada,  ba wani rana da Allah ya fi 'yanta bawa daga wuta  kamar ranar arfa  lallai yana kusanta sannan ya yi alfahari da su gaban mala'iku sannan ya ce mai wadannan suke so .
   Adu'an da ya fi ko wanne albarka  da yalwa  a wurin lada   da saurin amsawa shi ne Aduar Arfa, to ku yi kokari da kankan da kai da kyautata yabo , da Adu'a , kuma mustahabbi ne yin azumin ranar Arfa ga wanda bai hajji, azumtar ta na kankare  zunuban shekarar da ta gabata, da shekara da ta biyo ta.
Mustahabbi ne yin kabbarori a karshen sallolin farillah, tun daga asuban ranar Arafa har zuwa ranar karshe na ayyamu al-Tashrik, wanda aka tsere wa a  wani sashe na sallah to zai kawo su kabbarorin ne bayan ya rama sallarsa,  Alhazai za su fara kabbarorin ne daga azahar na ranar Babbar sallah.
Ya ku Musulmai!
Ku yi kabbarori a sassa da nahiyoyi,ku yi kabbarori a gine gine da sarari, ku yi kabbarori a gidaje da jeji, ku yi kabbarori a safiya da maraice, ku yi ta kabbarori har ya cika sama,
Allahu Akbar Allahu Akbar  la'ilaha illal lahu Allahu Akbar walillahil Hamd
Ku yi salati da aminci ga Ahmadu mai shiryarwa  mai ceto ga dukka halittu, wanda ya mishi salati guda Allah zai mishi guda goma.
Ya Allah ka yi dadin tsira ga bawan ka kuma manzonka  Muhammad, ya Allah ka yarda da iyalanshi da sahabbai da mu  ya mai karamci mai kyauta.
Ya Allah ka daukaka Musulunci da Musulmai ka kaskantar da shirka da mushrikai, ka rusa makiya Addini, ka sanya garuruwan musulmai cikin aminci da natsuwa da kwanciyan hankali da zaman lafiya ya Ubangijin talikai             

هناك تعليق واحد:

  1. Sannu Kowa,
    Sunana Mista, Rugare Sim. Ina zaune a Holland kuma ni mai farin ciki ne yau? kuma na gaya wa kaina cewa duk wani mai ba da bashi wanda zai tseratar da ni da iyalina daga mummunan halinmu, zan koma ga duk mutumin da ke neman bashi a kansa, ya ba ni farin ciki a gare ni da iyalina, na kasance ina buƙatar aro na € 300,000.00 don fara rayuwata gaba daya kamar ni uba daya ne da yara 2 Na hadu da wannan mai gaskiya kuma Allah yana tsoron mai bada rancen da zai taimake ni da rancen € 300,000.00, shi mutum ne mai tsoron Allah, idan kana bukatar aro Kuma za ku biya bashin don Allah ku kira shi ku gaya masa cewa (Mr, Rugare Sim) yana nuna muku shi. Tuntuɓi Mista, Mohamed Careen ta imel: (arabloanfirmserves@gmail.com)


    MAGANAR BAYANIN AIKIN LATSA
    Sunan rana......
    Suna na tsakiya .....
    2) Jinsi: .........
    3) Bukatar Lamuni: .........
    4) Tsawon Lamuni: .........
    5) Kasa: .........
    6) Adireshin Gida: .........
    7) Lambar Waya: .........
    8) Adireshin Imel ..........
    9) Gashi na wata-wata: …………… ..
    10) Aiki: ...........................
    11) Wanne rukunin yanar gizo kuka kasance game da shi …………… ..
    Godiya da kuma mafi kyawun gaisuwa.
    Email arabloanfirmserves@gmail.com

    ردحذف